Sashe 52
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace."Sai kawai mu zauna zaman jiran ki ai tuntuni mukaje asibiti suka duba shi suka kuma bashi magani aman jini kuma an wanke domun ke baki isa ayi miki 'karya ba.
Nace."Gwaggo me ya kawo wannan maganar ai nima ba 'karyatawa nayi ba." Dauke kanta tayi ta cigaba dayi masa firfita da maficin hannunta, tsakin Ummatu naji akaina kafin na juyo ta bar gurin tana surutai.
Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min.....Tace."Sa'ida ai kuka yanzu kika fara tunda baki da tausayi sai Allah ya sakawa wanda kika zalinta.
Shuru nai mata na mayar da hankalina kansa har yanzu idonsa a rufe yake murya na rawa na kira sunansa.
Shuru yayi bai amsa min ba, na sake kiran sunansa tare da kama hannunsa......da mugun sauri ya fizge hannunsa ya bude idonsa yana kallona cikin Sha'kakkiyar murya yace."Bana bukatar ganin ki Aunty Sa'ida I hit you i hit it !! na tsane ki! bana sonki! sai kinga sakamakon abinda kikayi min kije ki auri duk wanda zaki aura ni kuma zan mutu da sonki a cikin raina." Yana maganar yana tari da riqe kirji! Gwaggo duk ta gigice tana rirrikeshi cikin dauriya na hau katifar sosai ina kokarin rikeshi kamar walkiya ya juyo a zafafe ya hankad'e ni na fad'i a kasan gurin! da hannu yake nuna ni yana so yayi magana amma kuttun bakin ciki ya hanashi kawai sai jini muka gani ya ambulo daga bakinsa.
Ihu! na kurma! a kid'eme na sake hawa katifar na kamo shi gefan hijabi na nasa ina goge masa ina kuka wurjajan na kalleshi da fadin."Khalid ashe da gaske ne? me yayi zafi Khalid kada ka kashe kanka don Allah kayi ta wakkali ka cigaba da neman za'bin Allah.''
Zafafan hawaye ne suke sauka a kumatunsa hannu na na rawa na dinga goge masa ina kuka da fadin."Kayi hakuri dan Allah ka barwa Allah lamarin nan Khalid ka daina aman jini kada kasa mu cikin masifa.
Gwaggo da tausayin su ya isheta sai ta mike jiki a sa'bule ta shiga dakinta tana share hawaye da adduar d'auki daga Allah.
Rarrashin sa na cigaba dayi ina shafa kanshi da bayansa gabad'aya ya lafke a jikina sai ajiyar zuciya yake saukewa nauyin sa be dame ni ba ni dai buri na yayi min magana yaja bakinsa yayi shuru idonsa a rufe sai sake sakin jikinsa yake a jikina.
A hankali na kira sunansa. Ya bude idon yana kallona nace."Kayi hakuri ko."? tsira min rikitattun idanun nasa yayi nayi tsai ina karanta abinda yake cikinsu.......Babu wata alama data nuna ya dauki nasiha ta.....Hannuna na turmutsa cikin tarin suman kanshi a sanyaye nace."Khalid komai na rayuwa yana tafiya ne da ikon Allah duk yanda mutum yake son abu idan Allah baya sonsa da abun dole ya hakura shiyasa kaji ina cewa kayi hakuri ka nemi za'bin Allah Ni bana 'kin ka Khalid idan Allah ya kaddara aurena dakai duk rashin sona dole na hakura don Allah ka kwantar da hankalinka.
'Kuguna ya zagaye da hannuwansa, kallonsa nayi gabana na faduwa.........."Zaki auri wani ya 'karasa kwashe min Ni'ima ko."? yafada cikin sar'kewar murya. gabana na wani irin bugawa nake kallonsa....lumshe idonsa yayi ya sake yin release a jikina.......Bana bukatar wani banza ya ra'bi jikin ki aunty Sa'ida ke kuma gashi kina ta basu goyon baya akan hakan yanzu me kika hango a tare da wannan mutumin da zaki aura ko kudinsa kike so."?
Ajiyar zuciya na sauke ina kokarin cire shi daga jikina nace."Khalid me yasa kullum kai baka daukar nasiha ka daina barin shed'an yana tasiri a tare da kai aure nufin Allah ne.
Kansa ya d'ago yana kallona na kauda kaina da sauri! hannu yasa ya juyo da fuskata yana kallona yace."Idan na tafi amarica na tafi kenan ba zan dawo ba tunda kince na fita daga rayuwarki na fita har abadah zan barki kiyi zaman aure.
Hawaye suka kwace min nace."Kada ka yanke wannan hukuncin Khalid America ba gurin zama bane kada ka biyewa sharrin zuciya ka jefe mu a cikin masifa."
Murmushi mai ciwo yayi yace."Zama na a Najeria babban Jidali ne bana tsammanin zan iya barin ki ki zauna kalau a gidan auranki idan nayi nesa sai kinfi samun kwanciyar hankali." Sosai nake hawaye ina girgiza masa kai.....Hannu yasa yana goge min hawayen muka kurawa juna ido.....Haka kawai nake jin mugun tausayinsa na ratsa ni Khalid yana masifar sona babu shakka da maganar aurena da Aminu ba tayi nisa ba zan iya hakura na aureshi ko ya samu nutsuwa sai dai kash lokaci kadan ne ya rage a daura min aure bana tsammanin zan iya watsa mijin mahaifiyata 'kasa a ido.............."Salamu alaikum." Sallamar da muka ji itace ta sanya muka dawo nutsuwar mu. Baito ce da Jamila suka shigo gidan Baito sakin baki tayi tana kallon mu tare da tallafe ha'ba, ita kuwa Jamila ido jawur ta wuce gurin Ummatu fuuuuuuu! kamar tashin Iska.
_Nagode kwarai da adduarku masoya ciwon kai da sauqi sai dai dole ku cigaba dayi min uziri har zuwa lokacin da zan warware ina fata da yardar Allah na gama muku littafin nan kafin azimi a yanzu dai ina shan magani wannan pege din ma dauriya ce ganin kun damu da yawa yasa nayi typing din Ina rokon Ubangiji Allah ya 'kare mu da lafiya wannan zafin da muka shiga Allah kasa mu wuce lafiya NAGODE da Alfarma👏🏻_
*64&65*
Ina fita bakin titi adaidaita sahun Salim taci burki a gabana, dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata ya leko da kansa da fadin."Aunty Sa'ida ina zuwa haka."? Ba tare dana kalleshi ba nace."Hotoro na nufa." Murmushi yayi cike da kulawa yace."Aikuwa zaki jima baki samu babur ba domin a daidai wannan lokacin munfi dau'kar 'yan kasuwar kwari da bakin asibiti amma tunda Allah ya had'amu kawai ki shigo na kai ki.
Jin abinda yace yasa na shiga babur din ba tare da nayi masa musu ba, jan babur din yayi da sauri muka bar gurin......Sai da mukayi nisa sosai kira ya shigo wayarsa jin ya ambaci sunan Khalid a maganarsa yasa gabana faduwa, shuru ina sauraran maganar tasu yace."Okey to ni yanzu ina kan hanya amma idan na samu nutsuwa zan kira ka mu tattauna wata magana." Daga can bangaran Khalid yace."Okey to shikkenan nima ai na kusa shigowa garin domin nayi muku sallama zamu tafi amarica wasa." Salim cike da jin dadi da farin ciki yace kai amma nayi murna da farin ciki abokina Allah ya kara daukaka yasa ka zama zakaran gwajin dafi Allah yasa ka ciyo mana kofi.
Khalid yace."Ameeen abokina nagode sosai sai na jika." Salim yace."Babu damuwa zan kira ka idan na samu nutsuwa." Sallama sukayi da juna kowane ya kashe wayarsa.....Jikina ne yayi na d'an fahimci wasu maganganun nasu. ta mirror ya kalleni da murmushi a fuskarsa yace."Aunty Sa'ida kinji Khalid zai zo sallama ko? kullum yana sake samun nasara akan harkokinsa dan Allah ku taya shi da addua.
"Humm! kawai na iya cewa na kautar da kaina ina kallon hanya, to shima Salim din ganin babu fuska sai yaja bakinsa ya rufe ya cigaba da abinda yake gabansa.
Lokacin dana shiga dakin su biyu na samesu a zaune ga dukkanin alamu muhimmiyar magana suke tattaunawa, a nutse naje na zauna kasan kafet tare da risinar da kaina kasa nace." Alhaji barka da safiya." cike da nuna kulawa ya amsa da barka dai Sa'ida kin 'karaso."? Nace."Eh wallahi." Kallonsa nayi kansa a sunkuye yana kallon kasan kafet nace."Yaya Aminu ina kwana."? babu yabo babu fallasa ya amsa min.
Dakin yayi shuru na 'yan mintina. Alhaji yayi gyaran murya tare da kallona, jikina yayi sanyi na sunkuyar da kaina kasa ina addua akan Allah yasa alkairi ne.
"Sa'ida naji uzirin ki a bakin Kawun ki Ibrahim inda yake fada min cewa kina so ki koma gurin aiki hakane ko."? a sanyaye nace." Eh hakane Alhaji dan tuntuni komai ya kammala gurin aikin nawa sun kar'bi uzirina sunce babu damuwa zan iya komawa bakin aiki."
Yace."To shikkenan Sa'ida amma ban tari hanzarin ki ba ina neman wata alfarma a gurin ki ina fata zan samu."
Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa a duniya akwai abinda mutumin nan zai nema a gurina na kasa yi masa.
Nace."Alhaji ko wace irin alfarama kake nema a gurina zanyi maka mutukar inada iko da ita.
Yace."To Alhamdulillahi Sa'ida nagode sosai da kika karrama ni sabida haka dan Allah inaso ki amince na had'aku aure da Yayanki Aminu domun hakika naji ciwo da takaicin abinda Alhaji Nura yayi miki da k'ananun shekarunki ya sake ki."
Na dinga jin wani irin shocking a jikina gumi duk ya tsatstsafo min banta'ba tsammanin haka daga gurinsa ba shuru nayi bakina ya mutu murus na rasa ma abinda zance."
Yace."Sa'ida kinyi shuru ko baki amince ba."? a sanyaye na dago kaina na kalleshi kafin na mayar dashi kasa nace."Alhaji na amince mutukar shi Yaya Aminun ya amince zai aure ni da zawarcina.
Murmushi yayi yace."Alhamdulillahi naji dadi sosai kuma kada ki damu da Aminu yanzu kafin ki shigo muka gama magana dashi ya tabbatar min da cewa ya kar'bi auranki kamar yanda na umarce shi."
Nace."To shikkenan Alhaji Allah yasa hakan shi yafi alkairi." ya amsa da ameeen ya Allah ya d'ora da fad'in "maganar aiki ki bar ta tunda anayi ne domin biyan wasu bukata na yau da gobe na tabbata idan Allah ya kaddara auraki da Aminu baki da matsala tunda Alhamdulillahi Allah ya rufa masa asiri."
Gumin saman goshina nagoge nace."To shikkenan Alhaji duk yanda kace hakan za'ayi Allah yasa haka shi yafi alkairi." ya amsa da ameeen ya Allah." Umarnin tafiya ya bani na mike a sanyaye na fita daga dakin.
Zaune na sameta a bedroom dinta tana ninke kayan sawarta, zama nayi gefan gado kuka ya kwace min.....a nutse ta juyo tana kallona kuka nake sosai! tace."Sa'ida ki rufa min asiri na fita kunyar mutumin nan dan Allah kada ki watsa min kasa a ido."
Cikin rawar murya nace."Umma anya al'amarin nan zai yiwu kuwa Yaya Aminu saurayi ne ya za'ayi ace za'a had'ashi dani bazawara sai nake ganin kamar tilas akayi masa baya sona.
Nace."Gwaggo me ya kawo wannan maganar ai nima ba 'karyatawa nayi ba." Dauke kanta tayi ta cigaba dayi masa firfita da maficin hannunta, tsakin Ummatu naji akaina kafin na juyo ta bar gurin tana surutai.
Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min.....Tace."Sa'ida ai kuka yanzu kika fara tunda baki da tausayi sai Allah ya sakawa wanda kika zalinta.
Shuru nai mata na mayar da hankalina kansa har yanzu idonsa a rufe yake murya na rawa na kira sunansa.
Shuru yayi bai amsa min ba, na sake kiran sunansa tare da kama hannunsa......da mugun sauri ya fizge hannunsa ya bude idonsa yana kallona cikin Sha'kakkiyar murya yace."Bana bukatar ganin ki Aunty Sa'ida I hit you i hit it !! na tsane ki! bana sonki! sai kinga sakamakon abinda kikayi min kije ki auri duk wanda zaki aura ni kuma zan mutu da sonki a cikin raina." Yana maganar yana tari da riqe kirji! Gwaggo duk ta gigice tana rirrikeshi cikin dauriya na hau katifar sosai ina kokarin rikeshi kamar walkiya ya juyo a zafafe ya hankad'e ni na fad'i a kasan gurin! da hannu yake nuna ni yana so yayi magana amma kuttun bakin ciki ya hanashi kawai sai jini muka gani ya ambulo daga bakinsa.
Ihu! na kurma! a kid'eme na sake hawa katifar na kamo shi gefan hijabi na nasa ina goge masa ina kuka wurjajan na kalleshi da fadin."Khalid ashe da gaske ne? me yayi zafi Khalid kada ka kashe kanka don Allah kayi ta wakkali ka cigaba da neman za'bin Allah.''
Zafafan hawaye ne suke sauka a kumatunsa hannu na na rawa na dinga goge masa ina kuka da fadin."Kayi hakuri dan Allah ka barwa Allah lamarin nan Khalid ka daina aman jini kada kasa mu cikin masifa.
Gwaggo da tausayin su ya isheta sai ta mike jiki a sa'bule ta shiga dakinta tana share hawaye da adduar d'auki daga Allah.
Rarrashin sa na cigaba dayi ina shafa kanshi da bayansa gabad'aya ya lafke a jikina sai ajiyar zuciya yake saukewa nauyin sa be dame ni ba ni dai buri na yayi min magana yaja bakinsa yayi shuru idonsa a rufe sai sake sakin jikinsa yake a jikina.
A hankali na kira sunansa. Ya bude idon yana kallona nace."Kayi hakuri ko."? tsira min rikitattun idanun nasa yayi nayi tsai ina karanta abinda yake cikinsu.......Babu wata alama data nuna ya dauki nasiha ta.....Hannuna na turmutsa cikin tarin suman kanshi a sanyaye nace."Khalid komai na rayuwa yana tafiya ne da ikon Allah duk yanda mutum yake son abu idan Allah baya sonsa da abun dole ya hakura shiyasa kaji ina cewa kayi hakuri ka nemi za'bin Allah Ni bana 'kin ka Khalid idan Allah ya kaddara aurena dakai duk rashin sona dole na hakura don Allah ka kwantar da hankalinka.
'Kuguna ya zagaye da hannuwansa, kallonsa nayi gabana na faduwa.........."Zaki auri wani ya 'karasa kwashe min Ni'ima ko."? yafada cikin sar'kewar murya. gabana na wani irin bugawa nake kallonsa....lumshe idonsa yayi ya sake yin release a jikina.......Bana bukatar wani banza ya ra'bi jikin ki aunty Sa'ida ke kuma gashi kina ta basu goyon baya akan hakan yanzu me kika hango a tare da wannan mutumin da zaki aura ko kudinsa kike so."?
Ajiyar zuciya na sauke ina kokarin cire shi daga jikina nace."Khalid me yasa kullum kai baka daukar nasiha ka daina barin shed'an yana tasiri a tare da kai aure nufin Allah ne.
Kansa ya d'ago yana kallona na kauda kaina da sauri! hannu yasa ya juyo da fuskata yana kallona yace."Idan na tafi amarica na tafi kenan ba zan dawo ba tunda kince na fita daga rayuwarki na fita har abadah zan barki kiyi zaman aure.
Hawaye suka kwace min nace."Kada ka yanke wannan hukuncin Khalid America ba gurin zama bane kada ka biyewa sharrin zuciya ka jefe mu a cikin masifa."
Murmushi mai ciwo yayi yace."Zama na a Najeria babban Jidali ne bana tsammanin zan iya barin ki ki zauna kalau a gidan auranki idan nayi nesa sai kinfi samun kwanciyar hankali." Sosai nake hawaye ina girgiza masa kai.....Hannu yasa yana goge min hawayen muka kurawa juna ido.....Haka kawai nake jin mugun tausayinsa na ratsa ni Khalid yana masifar sona babu shakka da maganar aurena da Aminu ba tayi nisa ba zan iya hakura na aureshi ko ya samu nutsuwa sai dai kash lokaci kadan ne ya rage a daura min aure bana tsammanin zan iya watsa mijin mahaifiyata 'kasa a ido.............."Salamu alaikum." Sallamar da muka ji itace ta sanya muka dawo nutsuwar mu. Baito ce da Jamila suka shigo gidan Baito sakin baki tayi tana kallon mu tare da tallafe ha'ba, ita kuwa Jamila ido jawur ta wuce gurin Ummatu fuuuuuuu! kamar tashin Iska.
_Nagode kwarai da adduarku masoya ciwon kai da sauqi sai dai dole ku cigaba dayi min uziri har zuwa lokacin da zan warware ina fata da yardar Allah na gama muku littafin nan kafin azimi a yanzu dai ina shan magani wannan pege din ma dauriya ce ganin kun damu da yawa yasa nayi typing din Ina rokon Ubangiji Allah ya 'kare mu da lafiya wannan zafin da muka shiga Allah kasa mu wuce lafiya NAGODE da Alfarma👏🏻_
*64&65*
Ina fita bakin titi adaidaita sahun Salim taci burki a gabana, dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata ya leko da kansa da fadin."Aunty Sa'ida ina zuwa haka."? Ba tare dana kalleshi ba nace."Hotoro na nufa." Murmushi yayi cike da kulawa yace."Aikuwa zaki jima baki samu babur ba domin a daidai wannan lokacin munfi dau'kar 'yan kasuwar kwari da bakin asibiti amma tunda Allah ya had'amu kawai ki shigo na kai ki.
Jin abinda yace yasa na shiga babur din ba tare da nayi masa musu ba, jan babur din yayi da sauri muka bar gurin......Sai da mukayi nisa sosai kira ya shigo wayarsa jin ya ambaci sunan Khalid a maganarsa yasa gabana faduwa, shuru ina sauraran maganar tasu yace."Okey to ni yanzu ina kan hanya amma idan na samu nutsuwa zan kira ka mu tattauna wata magana." Daga can bangaran Khalid yace."Okey to shikkenan nima ai na kusa shigowa garin domin nayi muku sallama zamu tafi amarica wasa." Salim cike da jin dadi da farin ciki yace kai amma nayi murna da farin ciki abokina Allah ya kara daukaka yasa ka zama zakaran gwajin dafi Allah yasa ka ciyo mana kofi.
Khalid yace."Ameeen abokina nagode sosai sai na jika." Salim yace."Babu damuwa zan kira ka idan na samu nutsuwa." Sallama sukayi da juna kowane ya kashe wayarsa.....Jikina ne yayi na d'an fahimci wasu maganganun nasu. ta mirror ya kalleni da murmushi a fuskarsa yace."Aunty Sa'ida kinji Khalid zai zo sallama ko? kullum yana sake samun nasara akan harkokinsa dan Allah ku taya shi da addua.
"Humm! kawai na iya cewa na kautar da kaina ina kallon hanya, to shima Salim din ganin babu fuska sai yaja bakinsa ya rufe ya cigaba da abinda yake gabansa.
Lokacin dana shiga dakin su biyu na samesu a zaune ga dukkanin alamu muhimmiyar magana suke tattaunawa, a nutse naje na zauna kasan kafet tare da risinar da kaina kasa nace." Alhaji barka da safiya." cike da nuna kulawa ya amsa da barka dai Sa'ida kin 'karaso."? Nace."Eh wallahi." Kallonsa nayi kansa a sunkuye yana kallon kasan kafet nace."Yaya Aminu ina kwana."? babu yabo babu fallasa ya amsa min.
Dakin yayi shuru na 'yan mintina. Alhaji yayi gyaran murya tare da kallona, jikina yayi sanyi na sunkuyar da kaina kasa ina addua akan Allah yasa alkairi ne.
"Sa'ida naji uzirin ki a bakin Kawun ki Ibrahim inda yake fada min cewa kina so ki koma gurin aiki hakane ko."? a sanyaye nace." Eh hakane Alhaji dan tuntuni komai ya kammala gurin aikin nawa sun kar'bi uzirina sunce babu damuwa zan iya komawa bakin aiki."
Yace."To shikkenan Sa'ida amma ban tari hanzarin ki ba ina neman wata alfarma a gurin ki ina fata zan samu."
Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa a duniya akwai abinda mutumin nan zai nema a gurina na kasa yi masa.
Nace."Alhaji ko wace irin alfarama kake nema a gurina zanyi maka mutukar inada iko da ita.
Yace."To Alhamdulillahi Sa'ida nagode sosai da kika karrama ni sabida haka dan Allah inaso ki amince na had'aku aure da Yayanki Aminu domun hakika naji ciwo da takaicin abinda Alhaji Nura yayi miki da k'ananun shekarunki ya sake ki."
Na dinga jin wani irin shocking a jikina gumi duk ya tsatstsafo min banta'ba tsammanin haka daga gurinsa ba shuru nayi bakina ya mutu murus na rasa ma abinda zance."
Yace."Sa'ida kinyi shuru ko baki amince ba."? a sanyaye na dago kaina na kalleshi kafin na mayar dashi kasa nace."Alhaji na amince mutukar shi Yaya Aminun ya amince zai aure ni da zawarcina.
Murmushi yayi yace."Alhamdulillahi naji dadi sosai kuma kada ki damu da Aminu yanzu kafin ki shigo muka gama magana dashi ya tabbatar min da cewa ya kar'bi auranki kamar yanda na umarce shi."
Nace."To shikkenan Alhaji Allah yasa hakan shi yafi alkairi." ya amsa da ameeen ya Allah ya d'ora da fad'in "maganar aiki ki bar ta tunda anayi ne domin biyan wasu bukata na yau da gobe na tabbata idan Allah ya kaddara auraki da Aminu baki da matsala tunda Alhamdulillahi Allah ya rufa masa asiri."
Gumin saman goshina nagoge nace."To shikkenan Alhaji duk yanda kace hakan za'ayi Allah yasa haka shi yafi alkairi." ya amsa da ameeen ya Allah." Umarnin tafiya ya bani na mike a sanyaye na fita daga dakin.
Zaune na sameta a bedroom dinta tana ninke kayan sawarta, zama nayi gefan gado kuka ya kwace min.....a nutse ta juyo tana kallona kuka nake sosai! tace."Sa'ida ki rufa min asiri na fita kunyar mutumin nan dan Allah kada ki watsa min kasa a ido."
Cikin rawar murya nace."Umma anya al'amarin nan zai yiwu kuwa Yaya Aminu saurayi ne ya za'ayi ace za'a had'ashi dani bazawara sai nake ganin kamar tilas akayi masa baya sona.