Sashe 18
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Gwaggo zan koma gida amma da akwai sharad'i." Da sauri ta kalleni, na sha kunu da fad'in "Kiyi min tsakani da Khalid babu ni babu shi yaron bai da kirki da tarbiya akwai abubuwan da suka faru a tsakaninmu wanda idan na fito na fad'a miki hankalinki zai tashi ko kuma ma kice nai masa sharri to wannan dalilin yasa nayi shuru da bakina inaso ki zauna dashi kija masa kunne sosai ya fita daga sabgata maganar yana sona ya ajiyeta a gefe guda dan na rantse ba zan aureshi ba koda kuwa zan rasa mijin aure keda kike goya masa baya akan lamarin ki cire kanki domin ke zakiji kunya. abu na biyu kuma kina d'ora min lalurar aljanu ni lafiyata kalau kamar yanda nasha fada miki aure lokaci ne sabida haka Uwale ta daina janki gurin masu magani kina asarar kud'in ki bayan haka kuma idan kin san akwai ragowar wannan turaran da kike turnuk'awa a daki to da mun koma ki zubar dashi dan wallahi duk ranar da kika sake kunnawa zan bar gidan kuma komai abinki ba zan dawo ba guduwa ma zanyi ku rasa inda na nake.
Gwaggo gabanta ya fad'i! ta tsira min ido nace." Wallahi Gwaggo wannan maganar da nake miki har cikin zuciyata nake miki ita Khalid ba tsaran aure na bane ki daina tatsuniya ba zan aureshi ba sannan ni lafiyata kalau aure kuma lokaci ne insha Allah cikin satin nan Alhaji Nura zai turo da magabatansa.
"Sa'ida meye aibun Khalid da zaki dinga gudunsa ko dan bashi da kudi ne."? A sanyaye take magana dan na lura jikinta yayi sanyi da maganata.
Girgixa kaina nayi ina kokarin magana Umma ta shigo falon hannunta da farar leda cike da goro manya masu kyau Gwaggo da sauri tasa hannu ta kar'ba da fad'in " Kai amma naji dadi sosai Habiba Allah yayi miki albarka."
Umma Habiba ta amsa da "ameeen ya Allah." Ta fita daga falon.
Ledar ta kwance ta dauko daya ta 'bantara ta fara taunawa. Nace."Gwaggo Khalid ko ya kai *Dangwate* kud'i a duniya baya cikin tsarina yaje can ya auri daidai dashi nima na auri daidai dani magana ta mutu a gidan nan kada ki Sake yi min maganar Khalid."
Tace."Ai shikkenan Sa'ida tunda kinqi Khalid har kina kokarin yi masa sharri zanyi masa magana ya rabu dake tunda bakye kad'ai ce autar mata ba insha Allahu Allah zai bashi wacce ta fiki kyau da 'kuruciya."
Nace "Nima zan taya shi da adduar samun macan data fini."
Shuru tayi min ta cigaba da tauna goronta kallonta kawai nayi na gane maganata ta kashe mata jikinta, nace."Ko na kawo miki abinci."?
Girgiza kanta tayi tace."Bana bukata saboda inda na baro da akwai abinci." Nasan magana ta fad'a min a fakaice oho! ni dai na fad'a mata abinda yake raina sabida haka ita da Khalid din duk su shiga hankalinsu.
Tace."Khalid d'in ma gobe zai koma makaranta." Nace."Allah ya bada sa'a." ta amsa da "ameeen ya Allah."
Umma ce ta shigo dakin da fad'in "Gwaggo Alhajin ya dawo tashi muje nayi miki jagora ku gaisa." Da sauri ta miqe tana gyara yafan mayafinta suka fita tare.
Alhaji Shamsu yana zaune a kan kujera yana lissafi da wayar hannunsa sukayi sallama a dakin nasa....cikin kulawa ya amsa da fad'in"Gwaggo sannu da zuwa ga guri nan zauna."yafada yana nuna mata kujerar dake kallonsa
Gwaggo ta zauna kan kujerar tana amsawa tare da fad'in "Ai na jima a gidan ina jiranka da fatan ka dawo lafiya."? Yace." Lafiya lau gwaggo ai ban sani ba da tuntuni na dawo gidan sabida ke koda na shigo ma maigadi yake sanar dani zuwan Ibrahim bayan fita ta hakika banji dadin faruwar hakan ba."
Tace."Aikam dole kaji rashin dadi dan muma jiya haka muka kwana zuciyoyinmu Babu dadi wannan dalilin ne ma yasa shi Ibrahim dako sammako yazo gurinka domin ku tattauna magana sai kuma akayi rashin sa'a ka fita kasuwa shine nace to ni bari idan rana tayi sanyi sai nazo gidan na sameka mu tattauna maganar dan nazo tafiya da Sa'ida ne matarka Habiba tace lallai sai ka dawo ka bada umarni shine nace to komai dare kuwa zan zauna har ka dawo domin naji uzirinka akan yarinyar."
Alhaji Shamsu yayi gyaran murya yana kallonta ya riga yasan halinta 'yar taratsatsi ce yace."Hakane Gwaggo Sa'ida tazo gidan nan cikin halin damuwa tana kuka ta sheda mana abinda yake faruwa acan gidan al'amarin ya tayar min da hankalina sosai Gwaggo shi ai aure lokaci gareshi mai zai sanya ku tayar da hankalinku akan yarinyar nan har ku dinga d'ora mata lalura irin ta aljanu bayan haka kuma har a samu masu yi mata 'kazafi na zina wannan al'amari baiyi min dadi ba gaskiyar lamari raina ya 'baci dajin wannan magana shine dalilin da yasa ma na yanke hukunci kancewa ba zata koma gidan ba sai an kwana biyu kuma dole ne mu samu zama dashi Ibrahim din akan maganar yana da kyau ya jawa matarsa kunne ta guji jifan yarinyar nan da muna nan kalamai domin hakan bai dace ba."
Gwaggo tace."To ai Alhaji Ibrahim ya tauna tsakuwa dan aya taji tsoro inaso na sheda maka cewar duk yanda kake kaunar yarinyar ba kamar shi ba tunda Ubanta ne ya saki nono shi ya kuma ya kama kaga dole yayi kishinta ya kuma nunawa matarsa 'bacin rai dan yanzu maganar da nake maka Rabi tana gidansu tun jiya ya koreta daga gidansa yace mutukar ba Sa'ida ce ta dawo gidan ba to ya gama zama da ita."
Alhaji Shamsu yace."Subahanallahi Me yayi zafi Ibrahim zai yanke wannan hukunci." Ummah Habibatan tace."Nima haka na gani Alhaji Iro ya yanke hukuncin da bai kamata ba ai komai a sannu a hankali ake binsa."
Gwaggo tace."To ai shine nake so ku fahimta Ibrahim zai iya rabuwa da matarsa akan yarinyar nan to tun kafin hakan ta faru yasa nazo domin tafiya da ita."
Hankali a tashe ya dauki wayarsa da fad'in "Bari na kira wayarsa idan da hali sai yazo domin mu tattauna maganar a tsakanina dashi amma banji dadin wannan lamari ba."
Gwaggo tace."To shikkenan ai yanzu nasan ya dawo daga kasuwa idan ma bai dawo ba to babu shakka yana kan hanya.
Kawu Iro na adaidaita sahu kira ya shigo wayarsa ganin number Alhajin yasa da sauri ya daga suka gaisa a tsanake Alhaji Shamsu ya sheda masa uzirinsa....Kawu Iro yace."To babu damuwa Alhaji ganin zuwa insha Allahu." Wayar ya kashe ya umarci direban daya juya baya ya kaishi hotoro. Yace."Amma dai zaka 'kara min kudi ko."? Kawu Iro yace."Eh 'kwarai kuwa idan ma ka samu fasinja ka dauka." yace."to shikkenan.
Sai magariba Kawu Iro ya isa gidan kuma basu samu zama ba sai da suka gabatar da sallah tukkuna suka fito daga massalaci a tare wani 'kebantacan guri suka samu suka zauna suka sake gaisawa cikin mutumci kana suka shiga tattauna abinda ya had'asu.
Kawu Iro ya sauke ajiyar zuciya da fad'in "Alhaji ka kwantar da hankalinka insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba maganar mai d'akina kuma ni a ganina hukuncin dana dauka a kanta shine daidai kaga gaba zata kiyaye jifan yarinyar nan da wata mummunar kalma."
Alhaji Shamsu yace."Hakane Ibrahim to amma inaso dan Allah ka sake sanya ido akan yarinyar nan sannan idan da wani wanda kaga alamun da gaske yake sonta to kayi masa magana ya fito kawai domin hakan shine ya dace."
Kawu Iro yace."Insha Allahu hakan za'ayi akwai wani mutumin anan gaban inda muke yana son ta koga yanayin hidimar da yake mata to saboda haka idan na koma gida zan sameshi da maganar domin mu tattauna."
Alhaji Shamsu yace."To Alhamdulillahi Allah yasa sanya alkairi.'' Kawu Iro ya amsa da ameeen ya rabbi.''
To muna zaune a falo har gwaggon muna hira ya shigo. gwaggo tayi saurin fad'in "Ina fatan Ibrahim din yazo." Yace."Eh Gwaggo yazo ina fita da niyyar shiga massalaci na hangi zuwansa tare ma mukayi sallah masha Allah mun tattauna magana dashi ta fahinta saboda haka ke Sa'ida zaki koma gida magana ta wuce insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba sannan kuma Ibrahim ya sheda min cewa akwai wani mutumi da yake sonki a Cikin unguwar to nace masa yayi magana dashi idan da gaske yake sai yayi magana ayi abinda za'ayi."
Gwaggo har ta bud'e baki za tayi magana sai kuma ta fasa.
Yace."Gwaggo kamar akwai magana a bakinki." girgixa kanta tayi tace."Aa babu magana Alhaji." Ya kalleni da fad'in "Kinji hukuncin dana yanke ko."? Nace." Eh naji Alhaji dama nima inaso nayi masa magana kan cewa ya turo magabatansa ayi maganar aure idan da gaske yake."
Alhaji yace."To Alhamdulillahi hakan yayi kiyi masa magana shima Ibrahim din yayi masa sai ya dauki maganar da muhimmanci." Nace."To shikkenan Alhaji." hannu yasa a aljihu ya dauko kudi kimanin dubu biyar ya mikawa Gwaggo da fadin "Gashi kya sayi goro." Babu yabo babu fallasa ta kar'bi kudin dan Taji masifar haushin yanda yake nuna ikonsa akan Jikarta wai duk muna nan maganganun data ya'ba masa ba suyi masa zafi ba sai wani za'kal'kalewa yake.
Bayan fitarsa daga falon Ummah Habiba tace"Gwaggo bari na kawo miki abinci kici sai ku taf......tun kafin ta 'karasa tayi saurin katseta da fad'in "Bayan wanda naci d'azu kuma zaki sake d'ubga min wani Aa bana bukata tafiya za muyi." kana jin yanda tayi maganar kasan a fusace take......mi'kewa tayi tana gyara yafan mayafinta, nida Umma muka bita da kallon mamaki.
A cunkushe tace."To gimbiya ina jakar kayan naki take na d'aukar miki.'' Murmushi takaici nayi ba tare dana tanka mata ba na mi'ke Umma ma ta mi'ke tana 'yar dariya nasan ita da gwaggo ne....Hijabina na gyara na dauki jakar kayana na ri'ke ta ta'be bakinta tai tayi gaba tana surutai! Umma tace."Gwaggo ga mayafi da takalmi kayi amfani dasu."
Juyowa tayi tana kallon ledar hannunta murmshi tayi wanda be kai ciki ba tace."Habiba kin manta ni tunda jajayen sawuna bana yafa wani gyale idan ba na atamfa ba."
Umma tace."Kwarai hakane na manta wallahi to ki kar'ba dai ko kyautarsa sai kiyi.....Nace."Umma ki ajiye mayafin ki zaiyi miki amfani idan ta kar'ba ma munafukar matar nan zata bawa Uwale."
Gwaggo gabanta ya fad'i! ta tsira min ido nace." Wallahi Gwaggo wannan maganar da nake miki har cikin zuciyata nake miki ita Khalid ba tsaran aure na bane ki daina tatsuniya ba zan aureshi ba sannan ni lafiyata kalau aure kuma lokaci ne insha Allah cikin satin nan Alhaji Nura zai turo da magabatansa.
"Sa'ida meye aibun Khalid da zaki dinga gudunsa ko dan bashi da kudi ne."? A sanyaye take magana dan na lura jikinta yayi sanyi da maganata.
Girgixa kaina nayi ina kokarin magana Umma ta shigo falon hannunta da farar leda cike da goro manya masu kyau Gwaggo da sauri tasa hannu ta kar'ba da fad'in " Kai amma naji dadi sosai Habiba Allah yayi miki albarka."
Umma Habiba ta amsa da "ameeen ya Allah." Ta fita daga falon.
Ledar ta kwance ta dauko daya ta 'bantara ta fara taunawa. Nace."Gwaggo Khalid ko ya kai *Dangwate* kud'i a duniya baya cikin tsarina yaje can ya auri daidai dashi nima na auri daidai dani magana ta mutu a gidan nan kada ki Sake yi min maganar Khalid."
Tace."Ai shikkenan Sa'ida tunda kinqi Khalid har kina kokarin yi masa sharri zanyi masa magana ya rabu dake tunda bakye kad'ai ce autar mata ba insha Allahu Allah zai bashi wacce ta fiki kyau da 'kuruciya."
Nace "Nima zan taya shi da adduar samun macan data fini."
Shuru tayi min ta cigaba da tauna goronta kallonta kawai nayi na gane maganata ta kashe mata jikinta, nace."Ko na kawo miki abinci."?
Girgiza kanta tayi tace."Bana bukata saboda inda na baro da akwai abinci." Nasan magana ta fad'a min a fakaice oho! ni dai na fad'a mata abinda yake raina sabida haka ita da Khalid din duk su shiga hankalinsu.
Tace."Khalid d'in ma gobe zai koma makaranta." Nace."Allah ya bada sa'a." ta amsa da "ameeen ya Allah."
Umma ce ta shigo dakin da fad'in "Gwaggo Alhajin ya dawo tashi muje nayi miki jagora ku gaisa." Da sauri ta miqe tana gyara yafan mayafinta suka fita tare.
Alhaji Shamsu yana zaune a kan kujera yana lissafi da wayar hannunsa sukayi sallama a dakin nasa....cikin kulawa ya amsa da fad'in"Gwaggo sannu da zuwa ga guri nan zauna."yafada yana nuna mata kujerar dake kallonsa
Gwaggo ta zauna kan kujerar tana amsawa tare da fad'in "Ai na jima a gidan ina jiranka da fatan ka dawo lafiya."? Yace." Lafiya lau gwaggo ai ban sani ba da tuntuni na dawo gidan sabida ke koda na shigo ma maigadi yake sanar dani zuwan Ibrahim bayan fita ta hakika banji dadin faruwar hakan ba."
Tace."Aikam dole kaji rashin dadi dan muma jiya haka muka kwana zuciyoyinmu Babu dadi wannan dalilin ne ma yasa shi Ibrahim dako sammako yazo gurinka domin ku tattauna magana sai kuma akayi rashin sa'a ka fita kasuwa shine nace to ni bari idan rana tayi sanyi sai nazo gidan na sameka mu tattauna maganar dan nazo tafiya da Sa'ida ne matarka Habiba tace lallai sai ka dawo ka bada umarni shine nace to komai dare kuwa zan zauna har ka dawo domin naji uzirinka akan yarinyar."
Alhaji Shamsu yayi gyaran murya yana kallonta ya riga yasan halinta 'yar taratsatsi ce yace."Hakane Gwaggo Sa'ida tazo gidan nan cikin halin damuwa tana kuka ta sheda mana abinda yake faruwa acan gidan al'amarin ya tayar min da hankalina sosai Gwaggo shi ai aure lokaci gareshi mai zai sanya ku tayar da hankalinku akan yarinyar nan har ku dinga d'ora mata lalura irin ta aljanu bayan haka kuma har a samu masu yi mata 'kazafi na zina wannan al'amari baiyi min dadi ba gaskiyar lamari raina ya 'baci dajin wannan magana shine dalilin da yasa ma na yanke hukunci kancewa ba zata koma gidan ba sai an kwana biyu kuma dole ne mu samu zama dashi Ibrahim din akan maganar yana da kyau ya jawa matarsa kunne ta guji jifan yarinyar nan da muna nan kalamai domin hakan bai dace ba."
Gwaggo tace."To ai Alhaji Ibrahim ya tauna tsakuwa dan aya taji tsoro inaso na sheda maka cewar duk yanda kake kaunar yarinyar ba kamar shi ba tunda Ubanta ne ya saki nono shi ya kuma ya kama kaga dole yayi kishinta ya kuma nunawa matarsa 'bacin rai dan yanzu maganar da nake maka Rabi tana gidansu tun jiya ya koreta daga gidansa yace mutukar ba Sa'ida ce ta dawo gidan ba to ya gama zama da ita."
Alhaji Shamsu yace."Subahanallahi Me yayi zafi Ibrahim zai yanke wannan hukunci." Ummah Habibatan tace."Nima haka na gani Alhaji Iro ya yanke hukuncin da bai kamata ba ai komai a sannu a hankali ake binsa."
Gwaggo tace."To ai shine nake so ku fahimta Ibrahim zai iya rabuwa da matarsa akan yarinyar nan to tun kafin hakan ta faru yasa nazo domin tafiya da ita."
Hankali a tashe ya dauki wayarsa da fad'in "Bari na kira wayarsa idan da hali sai yazo domin mu tattauna maganar a tsakanina dashi amma banji dadin wannan lamari ba."
Gwaggo tace."To shikkenan ai yanzu nasan ya dawo daga kasuwa idan ma bai dawo ba to babu shakka yana kan hanya.
Kawu Iro na adaidaita sahu kira ya shigo wayarsa ganin number Alhajin yasa da sauri ya daga suka gaisa a tsanake Alhaji Shamsu ya sheda masa uzirinsa....Kawu Iro yace."To babu damuwa Alhaji ganin zuwa insha Allahu." Wayar ya kashe ya umarci direban daya juya baya ya kaishi hotoro. Yace."Amma dai zaka 'kara min kudi ko."? Kawu Iro yace."Eh 'kwarai kuwa idan ma ka samu fasinja ka dauka." yace."to shikkenan.
Sai magariba Kawu Iro ya isa gidan kuma basu samu zama ba sai da suka gabatar da sallah tukkuna suka fito daga massalaci a tare wani 'kebantacan guri suka samu suka zauna suka sake gaisawa cikin mutumci kana suka shiga tattauna abinda ya had'asu.
Kawu Iro ya sauke ajiyar zuciya da fad'in "Alhaji ka kwantar da hankalinka insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba maganar mai d'akina kuma ni a ganina hukuncin dana dauka a kanta shine daidai kaga gaba zata kiyaye jifan yarinyar nan da wata mummunar kalma."
Alhaji Shamsu yace."Hakane Ibrahim to amma inaso dan Allah ka sake sanya ido akan yarinyar nan sannan idan da wani wanda kaga alamun da gaske yake sonta to kayi masa magana ya fito kawai domin hakan shine ya dace."
Kawu Iro yace."Insha Allahu hakan za'ayi akwai wani mutumin anan gaban inda muke yana son ta koga yanayin hidimar da yake mata to saboda haka idan na koma gida zan sameshi da maganar domin mu tattauna."
Alhaji Shamsu yace."To Alhamdulillahi Allah yasa sanya alkairi.'' Kawu Iro ya amsa da ameeen ya rabbi.''
To muna zaune a falo har gwaggon muna hira ya shigo. gwaggo tayi saurin fad'in "Ina fatan Ibrahim din yazo." Yace."Eh Gwaggo yazo ina fita da niyyar shiga massalaci na hangi zuwansa tare ma mukayi sallah masha Allah mun tattauna magana dashi ta fahinta saboda haka ke Sa'ida zaki koma gida magana ta wuce insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba sannan kuma Ibrahim ya sheda min cewa akwai wani mutumi da yake sonki a Cikin unguwar to nace masa yayi magana dashi idan da gaske yake sai yayi magana ayi abinda za'ayi."
Gwaggo har ta bud'e baki za tayi magana sai kuma ta fasa.
Yace."Gwaggo kamar akwai magana a bakinki." girgixa kanta tayi tace."Aa babu magana Alhaji." Ya kalleni da fad'in "Kinji hukuncin dana yanke ko."? Nace." Eh naji Alhaji dama nima inaso nayi masa magana kan cewa ya turo magabatansa ayi maganar aure idan da gaske yake."
Alhaji yace."To Alhamdulillahi hakan yayi kiyi masa magana shima Ibrahim din yayi masa sai ya dauki maganar da muhimmanci." Nace."To shikkenan Alhaji." hannu yasa a aljihu ya dauko kudi kimanin dubu biyar ya mikawa Gwaggo da fadin "Gashi kya sayi goro." Babu yabo babu fallasa ta kar'bi kudin dan Taji masifar haushin yanda yake nuna ikonsa akan Jikarta wai duk muna nan maganganun data ya'ba masa ba suyi masa zafi ba sai wani za'kal'kalewa yake.
Bayan fitarsa daga falon Ummah Habiba tace"Gwaggo bari na kawo miki abinci kici sai ku taf......tun kafin ta 'karasa tayi saurin katseta da fad'in "Bayan wanda naci d'azu kuma zaki sake d'ubga min wani Aa bana bukata tafiya za muyi." kana jin yanda tayi maganar kasan a fusace take......mi'kewa tayi tana gyara yafan mayafinta, nida Umma muka bita da kallon mamaki.
A cunkushe tace."To gimbiya ina jakar kayan naki take na d'aukar miki.'' Murmushi takaici nayi ba tare dana tanka mata ba na mi'ke Umma ma ta mi'ke tana 'yar dariya nasan ita da gwaggo ne....Hijabina na gyara na dauki jakar kayana na ri'ke ta ta'be bakinta tai tayi gaba tana surutai! Umma tace."Gwaggo ga mayafi da takalmi kayi amfani dasu."
Juyowa tayi tana kallon ledar hannunta murmshi tayi wanda be kai ciki ba tace."Habiba kin manta ni tunda jajayen sawuna bana yafa wani gyale idan ba na atamfa ba."
Umma tace."Kwarai hakane na manta wallahi to ki kar'ba dai ko kyautarsa sai kiyi.....Nace."Umma ki ajiye mayafin ki zaiyi miki amfani idan ta kar'ba ma munafukar matar nan zata bawa Uwale."