Sashe 12
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_
*13*
A daran ranar Gwaggo kasa rintsawa tayi asubar fari ta tashi tai alwala tayi sallah da carbi a hannunta ta fito kai tsaye gurin baba iro ta nufa ta shiga bubbuga musu kofa. Lokacin shi yana massalaci bai shigo ba, bugun kofar da take ya tashi khalid a firgice ya mike zaune dama shima sai dab da asubah baccin ya daukeshi agogon da yake kafe a bangon dakin ya kalla shida da rabi da sauri ya dauki brush dinsa ya fito.....kallo ta bishi dashi da fadin."Kada dai kace sai yanzu ka tashi."? kansa ya daga mata ya ratseta ya wuce bayansa tabi da kallo kafin tace."Khalid me yasa kake wasa da sallah ne."? ba tare da ya tanka mata ba ya dauki buta ya shiga bandaki, sai itama ta bar gurin ta nufi dakinta ta zauna cikin alhini da damuwa.
Baba Iro ne ya shigo dakin da carbi a hannunsa suka gaisa yace."Gwaggo ya kike ganin za'ayi ne."? Tace."Ibrahim ni da kaina zani gidan Alhaji Shamsun dan bana tantama can ta nufa kome suke ji dashi na rantse ni nafi karfinsu Sa'ida ikona ce dan haka tilas ta dawo gabana ta cigaba da zama."
Yace."Gwaggo kada ki fusata komai cikin nutsuwa za'ayi Alhaji Shamsu babban mutum ne mai mutunci bai kamata kije har gidansa gaban iyalinsa kici masa mutunci ba."
"Ibrahim bafa zan zauna nayi lako-lako ba wato ka manta irin d'auki ba dad'in da mukayi dasu a wacan karon ko wane irin abune baiyi ba akan lallai Sai Sa'ida ta zauna a hannunsa to wannan karon ma ko yafi 'kuda naci ba zata zauna a gidansa ba domin bamu gaza dayi mata komai ba."
Baba Iro yayi shuru yana mamakin halin mahaifiyarsa yasan halinta da rashin tsinkaye da hangen nesa zata iya zuwa gidan mutum gaban iyalinsa ta tsinka shi wannan dalilin yasa yayi wani tunani....."Gwaggo ki nutsu ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Sa'ida zata dawo gida da kaina nake so naje gidan mu tattauna da Alhajin yana ganin mutuncina sosai itama Sa'idar haka da yardar Allah tare da ita zan dawo gida."
"Aa Iro gwara mu tafi tare ayi komai a gabana wallahi nake fada maka jiya kewarta hana ni rintsawa tayi.'' Yace." Ai bake kad'ai ba Gwaggo ni kaina banyi bacci ba amma insha Allah komai zai zo da sauki kiyi hakuri naje ni kad'ai din."
Shuru tayi alamar bata gamsu da maganarsa ba...Khalid ya shigo dakin suka gaisa da mahaifin nasa tace."Khalid kaje ka aro adaidaita sahun abokin ka kazo ka dauke ni ka kai ni gidan Alhaji Shamsu."
Babu walwala a fuskarsa yace."Me zakije kiyi."? da sauri tace."Zanje na dauko Sa'ida ne." Yace."Gwaggo babu inda zakije aunty Sa'ida zata dawo da kafafunta bayan haka kuma shi wanda zai bani aron adaidaita sahun nasa ya fita aiki da ita saboda haka ki zauna a gida zamuje nida Baba."
Da sauri tace."Zakuwa ku gan ni a gidan domin kuwa Allah ya hore min kudin mota.''
Baba Iro cikin rarrashi yace."Gwaggo abinda nutsuwa bata bayar ba to tashin hankali ma ba zai bayar dashi ba dan Allah ki nutsu kada kizo ki aikata abu daga baya kizo kina jin kunya Alhaji Shamsu bai cancanci tozarci a gurin mu ba yana kuma da ikon ri'ke Sa'ida a hannunsa tunda yana matsayin mijin mahaifiyarta.
Tace."Ai kaji abinda nake gudu dama nasan ko kaje ba wani mataki zaka dauka ba karshe ma ka dawo gida kai kadai ba tare da ita ba to sai naje na fada maka."
Khalid yace."To kije d'in kina shiga gate din zan sa masu gadi su saki karnuka kin san zan iya ko." shuru tayi tana kallonsa, Yace."An fada miki cewa komai a hankali da nutsuwa ake binsa amma kin kasa ganewa." tasa kuka da fad'in "Khalid bana son Sa'ida tayi nesa dani shiyasa kaga duk hankalina ya tashi bana so wannan karon Alhaji Shamsu ya samu galaba akan mu."
Yace."Ba zai samu ba insha Allahu." hawaye ta share tace."Khalid shiyasa nake so ka aureta na dinga ganinku a gabana inaso ku haifa min zuria mai yawa."
Tausayi ta bashi yace."To Allah ya amsa adduarki ina fata dai yanzu kin janye maganarki ta zuwa gidan." Tace."Tunda kunfi karfina na hakura ina zuba ido kuje ku dauko min ita."
Baba Iro yace."To Alhamdulillahi bari na kimtsa na fito, yana kokarin fita ta kira sunansa, juyowa yayi yana kallonta tace."Maganar Rabi baka ce min komai ba."
Yace."Tun jiya tana gidansu ai." girgiza kanta tayi tace."To wannan hukuncin daka yanke ni yayi min daidai na kuma ji dadi gobe ma sai ta sake aikatawa amma inaso yau idan Sa'ida ta dawo gida kaje kayo bikon matarka."
Yace."To Gwaggo yanda kika ce hakan za'ayi.'' ya juya da niyar fita sai ya tsaya da fad'in ."Me zaki karya dashi na aika a siyo miki." Tace."Ibrahim ba sai kayi asarar kudin ka ba ina da d'umame gashi can a jibge yanzu zan d'umama kafin ku tafi sai kuci."
Yace."To shikkenan Gwaggo." Bayan fitarsa daga dakin sai ta fara janyo kwanukan abincin tana dubawa doyar babu abinda tayi sannan itama farar shinkafar da Ummatu ta dafa a daran ranar ba tayi komai ba ta mike ta fita da kwanukan abincin a hannunta tana fad'in "Ruwan zafi kawai zan sa na turara shinkafar tunda da abincin ai ba sai anyi hidimar siyan wani abu ba."
Tsaf ta gyara abincin ya dawo tamkar sabo ta dauko ta kawo daki....cikin plate ta zuba masa ta zuba masa miyar nama da yawa.....yace." Gwaggo a'ina kuka samu nama haka."?
Tace."Kasan duk sati Alhaji Nura yakan kawo mana cefane to jiya da ya kawo sai Sa'ida tayi mana miya harda kayan shayi ma watakila ta tafi da abunta."
'Bata fuska yayi yace."Gwaggo nayi sha'awar abinci amma ba zanci ba." tace."Sabida me Khalid."? Hankalinsa nakan wayarsa yace."Saboda ina kishin mutumin na tsaneshi wallahi."
Tace."Khalid ka kwantar da hankalinka kai zaka auri Sa'ida Alhaji Nura kuwa shi yaga zai iya wahalar da kansa mu dai duk abinda ya kawo hannu biyu zamu sa mu 'karba.
Yace."Gwaggo idan kina bukatar farin ciki na to ki daina cin abinda mutumin zai kawo wa aunty Sa'ida wannan shine abinda nake bukata dake."
Shuru tayi tana girgiza kanta bata tsammanin zata daina cin kayan dad'in da Alhaji Nura zai kawo musu amma saboda ta kwantar masa da hankali tace."To shikkenan tunda baka so na daina."
Mikewa yayi zai fita tace."Yanzu Khalid kana kallon abinci da kyau amma kace ba zaka ci ba." Girgiza kansa yayi yana ta'be bakinsa yasa takalmansa ya fita..........Baba Iro ya shiga dakin cikin shiri yace."Ina Khalid din." tana tsotse 'kashin hannunta tace." Wata'kila ya tafi gurin mai shayi.'' da mamaki a tare dashi yace."Wannan abincin fa."?
Tace."Ibrahim kasan Khalid da zuciya da kishin kansa wai ba zai ci ba saboda yana kishi da wanda ya kawo cefanan."
Baba Iro ya zauna kusa da ita yana girgiza kansa mamaki yake sosai akan irin tarangahumar d'an nasa in banda abinsa inashi ina Sa'ida ko da yake Namiji komai 'kan'kantarsa mutukar ya balaga to mace duk girma da shekarunta bata gagararsa.....Gwaggo ta zuba masa abincin tasa masa miya da uban nama akai." Yace."Gwaggo ki rage naman." Tace."Ibrahim kaci ka 'koshi ka barshi.''
Bisimillah yayi ya fara cin abincin. dakin yayi shuru na tsayin minti biyar yace."Gwaggo ya kamata mu samu zama da mutumin nan idan da gaske yake akan yarinyar nan ya fito ayi abinda za'ayi."
Da sauri tace."Ko da gaske yake ba zamu bashi Sa'ida ba tunda Khalid ya nuna yana so hausawa na cewa gida bai koshi ba ba za'a kai dawa ba."
Yace."Gwaggo duk da Sa'ida budurwa ce to bai cancanci ayi mata dole ba shin da bakinta kinji ta furta tana san auran Khalid."?
Girgiza kanta tayi tace."Aa bata furta ba asali ma kullum cikin fad'a da juna suke sam basa jituwa dalilin ma kenan da yasa naje na kar'bo taimaiko gurin mai magani Ibrahim yarinyar nan Sa'ida na tare da iskokai kaga kuwa idan ba na gida ne ya aureta ba to babu shakka akwai matsala shiyasa kaga sam! bana sha'awar wani na waje ya aure ta."
Baba Iro shuru kawai yayi ya cigaba da cin abincinsa, shi kam ba zai iya da rigimar mahaifiyarsa ba mutukar shine madaurin auran Sa'ida to ba zai daura mata aure da wanda bata so ba.
To Cikin nutsuwar zuciya na wayi gari a gidan mahaifiyata, sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina sannan ta shigo dakin fuska a sake tace."Sa'ida kinji shuru ko." Murmushi kawai nayi nace."Umma ai nasan inda kike ina fata kin tashi lafiya."?
Tace."Lafiya kalau alhamdulillahi Jiya duk na shedawa Alhaji abinda yake faruwa shima al'amarin bai masa dadi ba ko kad'an dan haka ya yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan sai kin kwana biyu anan kin samu nutsuwa tukkuna."
Ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata ina jin dadin hukuncin da ya yanke. tace."Ki tashi kije ku gaisa dan fita zaiyi bayan kin fito daga dakin nasa sai ki shiga dakin matan gidan ku gaisa.''
Nace."To shikkenan Umma." hanyar fita ta nufa da fad'in "Bari na shiga kicin na taimakawa Asabe da aiki kada ya yara su makara a makaranta." Nace."Umma ai yau Lahadi babu skull.'' tace."Ai yaran gidan nan suna zuwa islamiyya tahafiz in suka tafi sai yamma suke dawowa."
Bayanta nabi da fad'in "To bari nima nazo ayi aikin dani." Mirmushi tayi ba tare data ce komai ba ta nufi hanyar babban kicin din nasu dake tsakar gidan.
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_
*13*
A daran ranar Gwaggo kasa rintsawa tayi asubar fari ta tashi tai alwala tayi sallah da carbi a hannunta ta fito kai tsaye gurin baba iro ta nufa ta shiga bubbuga musu kofa. Lokacin shi yana massalaci bai shigo ba, bugun kofar da take ya tashi khalid a firgice ya mike zaune dama shima sai dab da asubah baccin ya daukeshi agogon da yake kafe a bangon dakin ya kalla shida da rabi da sauri ya dauki brush dinsa ya fito.....kallo ta bishi dashi da fadin."Kada dai kace sai yanzu ka tashi."? kansa ya daga mata ya ratseta ya wuce bayansa tabi da kallo kafin tace."Khalid me yasa kake wasa da sallah ne."? ba tare da ya tanka mata ba ya dauki buta ya shiga bandaki, sai itama ta bar gurin ta nufi dakinta ta zauna cikin alhini da damuwa.
Baba Iro ne ya shigo dakin da carbi a hannunsa suka gaisa yace."Gwaggo ya kike ganin za'ayi ne."? Tace."Ibrahim ni da kaina zani gidan Alhaji Shamsun dan bana tantama can ta nufa kome suke ji dashi na rantse ni nafi karfinsu Sa'ida ikona ce dan haka tilas ta dawo gabana ta cigaba da zama."
Yace."Gwaggo kada ki fusata komai cikin nutsuwa za'ayi Alhaji Shamsu babban mutum ne mai mutunci bai kamata kije har gidansa gaban iyalinsa kici masa mutunci ba."
"Ibrahim bafa zan zauna nayi lako-lako ba wato ka manta irin d'auki ba dad'in da mukayi dasu a wacan karon ko wane irin abune baiyi ba akan lallai Sai Sa'ida ta zauna a hannunsa to wannan karon ma ko yafi 'kuda naci ba zata zauna a gidansa ba domin bamu gaza dayi mata komai ba."
Baba Iro yayi shuru yana mamakin halin mahaifiyarsa yasan halinta da rashin tsinkaye da hangen nesa zata iya zuwa gidan mutum gaban iyalinsa ta tsinka shi wannan dalilin yasa yayi wani tunani....."Gwaggo ki nutsu ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Sa'ida zata dawo gida da kaina nake so naje gidan mu tattauna da Alhajin yana ganin mutuncina sosai itama Sa'idar haka da yardar Allah tare da ita zan dawo gida."
"Aa Iro gwara mu tafi tare ayi komai a gabana wallahi nake fada maka jiya kewarta hana ni rintsawa tayi.'' Yace." Ai bake kad'ai ba Gwaggo ni kaina banyi bacci ba amma insha Allah komai zai zo da sauki kiyi hakuri naje ni kad'ai din."
Shuru tayi alamar bata gamsu da maganarsa ba...Khalid ya shigo dakin suka gaisa da mahaifin nasa tace."Khalid kaje ka aro adaidaita sahun abokin ka kazo ka dauke ni ka kai ni gidan Alhaji Shamsu."
Babu walwala a fuskarsa yace."Me zakije kiyi."? da sauri tace."Zanje na dauko Sa'ida ne." Yace."Gwaggo babu inda zakije aunty Sa'ida zata dawo da kafafunta bayan haka kuma shi wanda zai bani aron adaidaita sahun nasa ya fita aiki da ita saboda haka ki zauna a gida zamuje nida Baba."
Da sauri tace."Zakuwa ku gan ni a gidan domin kuwa Allah ya hore min kudin mota.''
Baba Iro cikin rarrashi yace."Gwaggo abinda nutsuwa bata bayar ba to tashin hankali ma ba zai bayar dashi ba dan Allah ki nutsu kada kizo ki aikata abu daga baya kizo kina jin kunya Alhaji Shamsu bai cancanci tozarci a gurin mu ba yana kuma da ikon ri'ke Sa'ida a hannunsa tunda yana matsayin mijin mahaifiyarta.
Tace."Ai kaji abinda nake gudu dama nasan ko kaje ba wani mataki zaka dauka ba karshe ma ka dawo gida kai kadai ba tare da ita ba to sai naje na fada maka."
Khalid yace."To kije d'in kina shiga gate din zan sa masu gadi su saki karnuka kin san zan iya ko." shuru tayi tana kallonsa, Yace."An fada miki cewa komai a hankali da nutsuwa ake binsa amma kin kasa ganewa." tasa kuka da fad'in "Khalid bana son Sa'ida tayi nesa dani shiyasa kaga duk hankalina ya tashi bana so wannan karon Alhaji Shamsu ya samu galaba akan mu."
Yace."Ba zai samu ba insha Allahu." hawaye ta share tace."Khalid shiyasa nake so ka aureta na dinga ganinku a gabana inaso ku haifa min zuria mai yawa."
Tausayi ta bashi yace."To Allah ya amsa adduarki ina fata dai yanzu kin janye maganarki ta zuwa gidan." Tace."Tunda kunfi karfina na hakura ina zuba ido kuje ku dauko min ita."
Baba Iro yace."To Alhamdulillahi bari na kimtsa na fito, yana kokarin fita ta kira sunansa, juyowa yayi yana kallonta tace."Maganar Rabi baka ce min komai ba."
Yace."Tun jiya tana gidansu ai." girgiza kanta tayi tace."To wannan hukuncin daka yanke ni yayi min daidai na kuma ji dadi gobe ma sai ta sake aikatawa amma inaso yau idan Sa'ida ta dawo gida kaje kayo bikon matarka."
Yace."To Gwaggo yanda kika ce hakan za'ayi.'' ya juya da niyar fita sai ya tsaya da fad'in ."Me zaki karya dashi na aika a siyo miki." Tace."Ibrahim ba sai kayi asarar kudin ka ba ina da d'umame gashi can a jibge yanzu zan d'umama kafin ku tafi sai kuci."
Yace."To shikkenan Gwaggo." Bayan fitarsa daga dakin sai ta fara janyo kwanukan abincin tana dubawa doyar babu abinda tayi sannan itama farar shinkafar da Ummatu ta dafa a daran ranar ba tayi komai ba ta mike ta fita da kwanukan abincin a hannunta tana fad'in "Ruwan zafi kawai zan sa na turara shinkafar tunda da abincin ai ba sai anyi hidimar siyan wani abu ba."
Tsaf ta gyara abincin ya dawo tamkar sabo ta dauko ta kawo daki....cikin plate ta zuba masa ta zuba masa miyar nama da yawa.....yace." Gwaggo a'ina kuka samu nama haka."?
Tace."Kasan duk sati Alhaji Nura yakan kawo mana cefane to jiya da ya kawo sai Sa'ida tayi mana miya harda kayan shayi ma watakila ta tafi da abunta."
'Bata fuska yayi yace."Gwaggo nayi sha'awar abinci amma ba zanci ba." tace."Sabida me Khalid."? Hankalinsa nakan wayarsa yace."Saboda ina kishin mutumin na tsaneshi wallahi."
Tace."Khalid ka kwantar da hankalinka kai zaka auri Sa'ida Alhaji Nura kuwa shi yaga zai iya wahalar da kansa mu dai duk abinda ya kawo hannu biyu zamu sa mu 'karba.
Yace."Gwaggo idan kina bukatar farin ciki na to ki daina cin abinda mutumin zai kawo wa aunty Sa'ida wannan shine abinda nake bukata dake."
Shuru tayi tana girgiza kanta bata tsammanin zata daina cin kayan dad'in da Alhaji Nura zai kawo musu amma saboda ta kwantar masa da hankali tace."To shikkenan tunda baka so na daina."
Mikewa yayi zai fita tace."Yanzu Khalid kana kallon abinci da kyau amma kace ba zaka ci ba." Girgiza kansa yayi yana ta'be bakinsa yasa takalmansa ya fita..........Baba Iro ya shiga dakin cikin shiri yace."Ina Khalid din." tana tsotse 'kashin hannunta tace." Wata'kila ya tafi gurin mai shayi.'' da mamaki a tare dashi yace."Wannan abincin fa."?
Tace."Ibrahim kasan Khalid da zuciya da kishin kansa wai ba zai ci ba saboda yana kishi da wanda ya kawo cefanan."
Baba Iro ya zauna kusa da ita yana girgiza kansa mamaki yake sosai akan irin tarangahumar d'an nasa in banda abinsa inashi ina Sa'ida ko da yake Namiji komai 'kan'kantarsa mutukar ya balaga to mace duk girma da shekarunta bata gagararsa.....Gwaggo ta zuba masa abincin tasa masa miya da uban nama akai." Yace."Gwaggo ki rage naman." Tace."Ibrahim kaci ka 'koshi ka barshi.''
Bisimillah yayi ya fara cin abincin. dakin yayi shuru na tsayin minti biyar yace."Gwaggo ya kamata mu samu zama da mutumin nan idan da gaske yake akan yarinyar nan ya fito ayi abinda za'ayi."
Da sauri tace."Ko da gaske yake ba zamu bashi Sa'ida ba tunda Khalid ya nuna yana so hausawa na cewa gida bai koshi ba ba za'a kai dawa ba."
Yace."Gwaggo duk da Sa'ida budurwa ce to bai cancanci ayi mata dole ba shin da bakinta kinji ta furta tana san auran Khalid."?
Girgiza kanta tayi tace."Aa bata furta ba asali ma kullum cikin fad'a da juna suke sam basa jituwa dalilin ma kenan da yasa naje na kar'bo taimaiko gurin mai magani Ibrahim yarinyar nan Sa'ida na tare da iskokai kaga kuwa idan ba na gida ne ya aureta ba to babu shakka akwai matsala shiyasa kaga sam! bana sha'awar wani na waje ya aure ta."
Baba Iro shuru kawai yayi ya cigaba da cin abincinsa, shi kam ba zai iya da rigimar mahaifiyarsa ba mutukar shine madaurin auran Sa'ida to ba zai daura mata aure da wanda bata so ba.
To Cikin nutsuwar zuciya na wayi gari a gidan mahaifiyata, sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina sannan ta shigo dakin fuska a sake tace."Sa'ida kinji shuru ko." Murmushi kawai nayi nace."Umma ai nasan inda kike ina fata kin tashi lafiya."?
Tace."Lafiya kalau alhamdulillahi Jiya duk na shedawa Alhaji abinda yake faruwa shima al'amarin bai masa dadi ba ko kad'an dan haka ya yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan sai kin kwana biyu anan kin samu nutsuwa tukkuna."
Ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata ina jin dadin hukuncin da ya yanke. tace."Ki tashi kije ku gaisa dan fita zaiyi bayan kin fito daga dakin nasa sai ki shiga dakin matan gidan ku gaisa.''
Nace."To shikkenan Umma." hanyar fita ta nufa da fad'in "Bari na shiga kicin na taimakawa Asabe da aiki kada ya yara su makara a makaranta." Nace."Umma ai yau Lahadi babu skull.'' tace."Ai yaran gidan nan suna zuwa islamiyya tahafiz in suka tafi sai yamma suke dawowa."
Bayanta nabi da fad'in "To bari nima nazo ayi aikin dani." Mirmushi tayi ba tare data ce komai ba ta nufi hanyar babban kicin din nasu dake tsakar gidan.