Sashe 43
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kawu Iro ya mike zaune ransa a bace yace."Wato Khalid din daga zuwan sa da abinda ya fara kenan me kikayi masa da zaiyi yun'kurin kasheki.
Hawaye na share nace."Sabida kawai anyi masa dubara akan idan ya dawo gida za'a daura mana aure shi ne daya samu labarin aurena da Alhaji Nura ya yanke min wannan hukuncin."
Kawu na kokarin yayi magana ya fito daga dakinsa, a kaina ya tsaya kamar zai mangare ni yace."Ni yaro ne da zakiyi mun dubara mai yasa baki fada min gaskiya ba kika yaudare ni shin kin san halin da nake ciki a yanzu."?
Kawu ya buga masa tsawa da fad'in "Yanzu daka tsaya a kanta dukan ta za kayi kome."?
Sunkuyar da kansa yayi ya nemi gefe ya tsuguna yana watsa min harara! al'amarin ya dinga bani mamaki da tsoro yanzu gabad'aya tsoronsa nake ji sabida dazu nayi masifar galabaita a hannunsa.
Kawu ya kalleshi rai a 'bace murya a kausashe yace." Khalid wallahi ka fita daga idona na rufe kabar ganin duk abinda kayi Gwaggo tana daure maka gindi wallahi ka guji fushi na wato har ka manta laifinka ko ka dawo zaka yi rashin mutunci da rashin arziki ko? Yanzu Sa'ida sa'arka ce da zaka dinga dukan ta."?
Yace."Kawu ka gafarce ni dan Allah ni wallahi 'karya take min ban doke taba."
Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa wai yau yaron dana sharewa majina shine yake 'karyata ni."
Kawu ya cigaba da cewa." Kayi yun'kurin kasheta ta hanyar matse mata ma'kogwaro kana nufin idan ka kasheta za'a saurara maka."? shuru yayi Kawun ya cigaba da cewa''Yarinya tace bata sonka bata sonka amma saboda naci ka nace sai ta aureka waye ya fada maka a nai wa so dole ne."?
Khalid ya dinga jin wani maqaqin bakin ciki a cikin ranshi! Kawu Iro ya cigaba da watsa masa 'bakar magana iya yanda ransa yake so tas yayi masa wankin babban bargo dama haushinsa yake ji! Khalid ya rasa inda zai sanya kasa sabida bakin ciki da takaici babu shakka da yasan wannan bakin cikin zai zo ya tarar to da yayi zamansa a inda yake.
Kawu Iro ya cigaba da cewa"To wannan ce maganata da kai ta 'karshe Khalid nayi maka tsakani da Sa'ida babu kai babu ita babu kuma maganar so Sa'ida ta girme maka a yanzu tunda tanada aure sabida haka kada na 'kara jin ka furta mata kalmar so gaisuwar mutunci ce a tsakaninku.
Kaji ko ba kaji ba.?
Cikin Jin mugun ciwon kai yace." Naji Kawu." Ya kalleni da fad'in "Ki tashi kije ki kwanta ki huta insha Allah itama Gwaggon gobe zan zauna da ita akan wannan matsalar.'' Cikin jin dadin abinda yayi wa Khalid din nayi masa sallama na tafi zuciyata fes nasan tunda mahaifinsa yaja masa kunne dole ya fita daga harkata.
.🥰🤝🏻💜_*
*51&52*
Ko dana koma d'akin Gwaggo 'kin sakar mata fuska nayi duk wani abu dana san zanyi a dakin nayi na fito nayi shimfida a tsakar gida nayi kwanciyata itama uffan ba tace dani ba, tsakanin ni da ita ban san waye yafi jin haushin wani ba.
Ummatu kuwa itama da bakin ciki ta kwana dan bayan fita ta daga gurin Kawu Iro kiranta yayi itama ya 'kare mata tanadi yace kuma ta jawa Khalid kunne ya shiga hankalinsa idan kuma yasan neman fitina ne ya dawo dashi to sawun sa a likkafa ya koma inda ya fito baya bukatarsa a cikin gidansa....Ummatu taci kukanta ta koshi ba tare da tace masa komai ba ta bar gurin tare da kudirin wani abu ranta.
Khalid yana kwance a d'aki! yaji duk irin cin mutuncin da Kawun kewa mahaifiyarsa ransa ya sake 'baci ya sake 'kullatar Auntyn nasa yana tunanin irin hukuncin da zai yanke mata.
Da zazzafan zazza'bi da ciwon kai ya kwana dan haka yana dawowa daga sallah ya shiga dakinsa ya kulle k'ofa ya kwanta ba tare da yayi tunanin zuwa ya duba Gwaggo mutuniyar tasa ba.
Cikin baccin daya soma fizgarsa ya dinga jin bugu ana kiran sunansa.
Mikewa yayi yaje ya bude kofar dakin, Ummatu ce ya bata hanya ta shiga dakin ta mayar da kofar ta rufe.
Gefan katifarsa ya zauna yana gaisheta ta amsa tana kokarin ajiye fulas din shayin dake hannunta.
Tace."Khalid ina fata jiya duk kaji irin cin mutumcin da mahaifinka yayi min ko."?
A sanyaye yace."Eh Umma naji kiyi hakuri dan Allah kin san halin baba be iya 'bacin rai ba."
Girgixa kanta tayi cikin takaici tace." Ba haka bane Khalid dama haka halin mahaifinka yake wani lokacin idan yayi ra'ayi haka zai zauna yaci mutuncina iya yanda ransa yake so akan wannan yarinyar Sa'ida babu abinda ba zai iya aikatawa ba."
Yace."Ummatu kiyi hakuri ki saba da halinsa idan kuma nine nake janyo muku sa'bani insha Allahu zan koma inda na fito kamar yanda naji yana fada jiya.
Tace."Khalid idan kai ka cika dan halak ne to dan Allah ka rabu da Sa'ida bafa ita kadai ce 'ya mace a duniya ba shin wai me ka hango a tattare da ita kake kulafunci.
Kansa ya sunkuyar kasa ta cigaba da cewa" A matsayina na mahaifiyarka nake umartarka a karo na biyu ka fita daga sabgar Sa'ida idan kana so kayi albarka a rayuwarka."
Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta a raunane yace."Umma ki taya ni addua akan abinda ke damuna a zuciyata insha Allahu zanyi kokarin ganin na cire aunt Sa'ida daga rayuwata."
Tace."To shikkenan Khalid zan cigaba dayi maka addua sannan inaso ka auri Jamila 'yar 'kanina Garba."
Ya kalleta cikin wani irin yanayi yace."Ummatu ki ajiye maganar Jamila a gefe guda ni bana ra'ayinta.
Tace."Khalid tuntuni fa na fahimci cewa baka kaunar dangi na kafi kaunar dangin mahaifinka yanzu meye aibun Jamila kasan dai tafi Sa'ida kyau ko gata yarinya daidai da kai."
Yace."Umma kin san shi so babu ruwan sa da wani kyau ko muni duk kyawun Jamila bata burge ni ba kuma bana jin sonta ko kadan a cikin raina.
Tace."Ni dai umarni nake baka ba za'bi ba saboda haka idan kana so kayi albarka to kabi umarnina."
Ya jima kansa a kasa kafin yace."Shikkenan Umma zanyi miki biyayya akan abinda kike so." murmushin jin dadi tayi tace."Insha Allahu kuwa zakayi alfahari da auran Jamila.
Shuru yayi bai ce mata komai ba tace."Ga ruwan shayi nan a fulas bari na kawo maka awara da sauran kayan shayin."
Yace."Nagode Ummana." fita tayi daga dakin ranta fari sol babu shakka za tayi farin ciki idan al'amarin nan ya tabbata.
3qutar ne a jikinsa sai kawai ya sanya k'aramar
T-shirt a jikinsa ya fito daga dakin nasa a daidai lokacin da Kawu ya fito daga nasa d'akin da shirin tafiya kasuwa.
'Dan risinawa yayi yace.''Kawu barka da asubah." Ba tare da ya kalleshi ba ya amsa da "Barka dai." ya d'aga labulan d'akin Ummatu yana mata magana. ganin haka yasa da sauri ya fita daga gurun.
Gwaggo na kokarin fitowa daga d'akin ya shiga tace."Ai dama yanzu nake maganarka ina cewa ko da kaina zan shiga gurin naku na dubaka naga baka shigo mun gaisa ba."
D'akin ya shiga babu walwala a tare dashi yace." Na d'an yi bacci ne."
Tace."Koda naji nima nace ko bacci kakeyi to zauna ga guri mu gaisa a nutse." gefanta take karkad'e masa tana marmatsar da abubuwa sai kace barasake ne zai zauna a gurun.
Hankalinsa akanta tana bacci a gadon ba tare da tasan ya shigo dakin ba....Gwaggo ta lura da irin kallon 'kurrular da yake mata sai duk jikinta yayi sanyi itakam wannan jaraba ta isheta wai shin wane irin so yaron nan yake wa Sa'ida.
Labari take bashi wai dan duk ta dauke masa hankali jinta kawai yake amma gabadaya hankalinsa da tunaninsa baya kanta yana can tunani akan Sa'ida duk da yasan ya ga mai mata illah amma yana bala'in kishin Alhaji Nura akanta shi kad'ai yake so ya cigaba da dabdala a wannan ramin amma wani katon banza ya shigar masa gona.
Gwaggo haushi ya bata ganin ya'ki barin abinda yake tace.''Ni kam banta'ba ganin mara zuciya irinka ba."
Sumar kansa ya shafa babu sukuni yace."Me nayi miki kuma."? Tsaki taja tace."Tunda ka shigo kake kallon Sa'ida alhalin bacci take yi ko gaisawa ba muyi ba hankalinka gabadaya yana kanta to ka dai kiyaye kada ka jefa kanta a matsala domin naga idanuwanka sunyi ja."
Murmushi yayi yana kallonta yace."Waye yace miki ita nake kallo."? Tace."Ai makauniya ce ni." Dariya yasa yana sosa kansa tace."Ka karya kummalo."?
Girgiza kansa yayi tace."To bari na zuba maka abinci." Yace."Gwaggo ba zanci abinci da safe ba ki bani ruwan shayi." Tace."Aa Ni yau kunu nasha ruwan shayi ka tambayi mahaifiyarka."
Yace." Okey na manta ma da akwai a fulas a dakina idan nasha zanzo naci abincin." Tace."To shikkenan.
D'akin ne yayi shuru na minti biyu ya cigaba da satar kallon Sa'ida ta 'kasan ido Gwaggon ta kalleshi tana girgiza kanta Hankali tace."Kasan abinda yake faruwa ko.''?
Girgiza kansa yayi yana d'an ya mutsa fuskarsa yace."Sai kin fad'a."
Juyawa tayi ta d'an kalli inda take kwance ta dawo da hankalinta kansa 'kasa-'kasa tace."Ai *GA IRINTA NAN!* ta guje ka ta auri wanda take so gashinan tana fuskantar matsala a gurinsa da matarsa ya hanata komawa gurin aiki kuma baya biya mata bukatarta.''
Jim yayi yana kallonta kafin yace."Gwaggo ban gane baya biya mata bukata ba."?
Waiwaya wa tayi ta sake kallon inda take kwance tayi 'kasa da murya tace."Bukatarta ta gurin auratayya mana wai baya son haihuwa shine yake inzali a waje ma'ana yana zubar da 'kwayoyin haihuwarsa."
Cike da mamaki yake kallonta! tana so ta 'kara tabbatar masa da maganar na tashi zaune duk sai suka diririce mussaman Gwaggo da gabadaya yanayin ta ya nuna na marasa gaskiya.
Yi nayi tamkar ban fahimci abinda suke ba na mike na fita, brush nayi na dawo d'akin na tarar dasu suna wata hirar.
Ta kalleni da fad'in '"Ga kayan karin kummalo nan." Ba tare da nace mata komai ba na hau bud'e kwanukan...........dakin yayi shuru na minti biyu kafin naji sautin muryarsa da fadin" Kin tashi lafiya."?
Kaina a kasa na amsa da lafiya lau." Gwaggo tace."Kina bacci dazu da safe aka kira wayarki kin san ni ban iya dauka ba shiyasa na barta ta katse."
Hawaye na share nace."Sabida kawai anyi masa dubara akan idan ya dawo gida za'a daura mana aure shi ne daya samu labarin aurena da Alhaji Nura ya yanke min wannan hukuncin."
Kawu na kokarin yayi magana ya fito daga dakinsa, a kaina ya tsaya kamar zai mangare ni yace."Ni yaro ne da zakiyi mun dubara mai yasa baki fada min gaskiya ba kika yaudare ni shin kin san halin da nake ciki a yanzu."?
Kawu ya buga masa tsawa da fad'in "Yanzu daka tsaya a kanta dukan ta za kayi kome."?
Sunkuyar da kansa yayi ya nemi gefe ya tsuguna yana watsa min harara! al'amarin ya dinga bani mamaki da tsoro yanzu gabad'aya tsoronsa nake ji sabida dazu nayi masifar galabaita a hannunsa.
Kawu ya kalleshi rai a 'bace murya a kausashe yace." Khalid wallahi ka fita daga idona na rufe kabar ganin duk abinda kayi Gwaggo tana daure maka gindi wallahi ka guji fushi na wato har ka manta laifinka ko ka dawo zaka yi rashin mutunci da rashin arziki ko? Yanzu Sa'ida sa'arka ce da zaka dinga dukan ta."?
Yace."Kawu ka gafarce ni dan Allah ni wallahi 'karya take min ban doke taba."
Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa wai yau yaron dana sharewa majina shine yake 'karyata ni."
Kawu ya cigaba da cewa." Kayi yun'kurin kasheta ta hanyar matse mata ma'kogwaro kana nufin idan ka kasheta za'a saurara maka."? shuru yayi Kawun ya cigaba da cewa''Yarinya tace bata sonka bata sonka amma saboda naci ka nace sai ta aureka waye ya fada maka a nai wa so dole ne."?
Khalid ya dinga jin wani maqaqin bakin ciki a cikin ranshi! Kawu Iro ya cigaba da watsa masa 'bakar magana iya yanda ransa yake so tas yayi masa wankin babban bargo dama haushinsa yake ji! Khalid ya rasa inda zai sanya kasa sabida bakin ciki da takaici babu shakka da yasan wannan bakin cikin zai zo ya tarar to da yayi zamansa a inda yake.
Kawu Iro ya cigaba da cewa"To wannan ce maganata da kai ta 'karshe Khalid nayi maka tsakani da Sa'ida babu kai babu ita babu kuma maganar so Sa'ida ta girme maka a yanzu tunda tanada aure sabida haka kada na 'kara jin ka furta mata kalmar so gaisuwar mutunci ce a tsakaninku.
Kaji ko ba kaji ba.?
Cikin Jin mugun ciwon kai yace." Naji Kawu." Ya kalleni da fad'in "Ki tashi kije ki kwanta ki huta insha Allah itama Gwaggon gobe zan zauna da ita akan wannan matsalar.'' Cikin jin dadin abinda yayi wa Khalid din nayi masa sallama na tafi zuciyata fes nasan tunda mahaifinsa yaja masa kunne dole ya fita daga harkata.
.🥰🤝🏻💜_*
*51&52*
Ko dana koma d'akin Gwaggo 'kin sakar mata fuska nayi duk wani abu dana san zanyi a dakin nayi na fito nayi shimfida a tsakar gida nayi kwanciyata itama uffan ba tace dani ba, tsakanin ni da ita ban san waye yafi jin haushin wani ba.
Ummatu kuwa itama da bakin ciki ta kwana dan bayan fita ta daga gurin Kawu Iro kiranta yayi itama ya 'kare mata tanadi yace kuma ta jawa Khalid kunne ya shiga hankalinsa idan kuma yasan neman fitina ne ya dawo dashi to sawun sa a likkafa ya koma inda ya fito baya bukatarsa a cikin gidansa....Ummatu taci kukanta ta koshi ba tare da tace masa komai ba ta bar gurin tare da kudirin wani abu ranta.
Khalid yana kwance a d'aki! yaji duk irin cin mutuncin da Kawun kewa mahaifiyarsa ransa ya sake 'baci ya sake 'kullatar Auntyn nasa yana tunanin irin hukuncin da zai yanke mata.
Da zazzafan zazza'bi da ciwon kai ya kwana dan haka yana dawowa daga sallah ya shiga dakinsa ya kulle k'ofa ya kwanta ba tare da yayi tunanin zuwa ya duba Gwaggo mutuniyar tasa ba.
Cikin baccin daya soma fizgarsa ya dinga jin bugu ana kiran sunansa.
Mikewa yayi yaje ya bude kofar dakin, Ummatu ce ya bata hanya ta shiga dakin ta mayar da kofar ta rufe.
Gefan katifarsa ya zauna yana gaisheta ta amsa tana kokarin ajiye fulas din shayin dake hannunta.
Tace."Khalid ina fata jiya duk kaji irin cin mutumcin da mahaifinka yayi min ko."?
A sanyaye yace."Eh Umma naji kiyi hakuri dan Allah kin san halin baba be iya 'bacin rai ba."
Girgixa kanta tayi cikin takaici tace." Ba haka bane Khalid dama haka halin mahaifinka yake wani lokacin idan yayi ra'ayi haka zai zauna yaci mutuncina iya yanda ransa yake so akan wannan yarinyar Sa'ida babu abinda ba zai iya aikatawa ba."
Yace."Ummatu kiyi hakuri ki saba da halinsa idan kuma nine nake janyo muku sa'bani insha Allahu zan koma inda na fito kamar yanda naji yana fada jiya.
Tace."Khalid idan kai ka cika dan halak ne to dan Allah ka rabu da Sa'ida bafa ita kadai ce 'ya mace a duniya ba shin wai me ka hango a tattare da ita kake kulafunci.
Kansa ya sunkuyar kasa ta cigaba da cewa" A matsayina na mahaifiyarka nake umartarka a karo na biyu ka fita daga sabgar Sa'ida idan kana so kayi albarka a rayuwarka."
Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta a raunane yace."Umma ki taya ni addua akan abinda ke damuna a zuciyata insha Allahu zanyi kokarin ganin na cire aunt Sa'ida daga rayuwata."
Tace."To shikkenan Khalid zan cigaba dayi maka addua sannan inaso ka auri Jamila 'yar 'kanina Garba."
Ya kalleta cikin wani irin yanayi yace."Ummatu ki ajiye maganar Jamila a gefe guda ni bana ra'ayinta.
Tace."Khalid tuntuni fa na fahimci cewa baka kaunar dangi na kafi kaunar dangin mahaifinka yanzu meye aibun Jamila kasan dai tafi Sa'ida kyau ko gata yarinya daidai da kai."
Yace."Umma kin san shi so babu ruwan sa da wani kyau ko muni duk kyawun Jamila bata burge ni ba kuma bana jin sonta ko kadan a cikin raina.
Tace."Ni dai umarni nake baka ba za'bi ba saboda haka idan kana so kayi albarka to kabi umarnina."
Ya jima kansa a kasa kafin yace."Shikkenan Umma zanyi miki biyayya akan abinda kike so." murmushin jin dadi tayi tace."Insha Allahu kuwa zakayi alfahari da auran Jamila.
Shuru yayi bai ce mata komai ba tace."Ga ruwan shayi nan a fulas bari na kawo maka awara da sauran kayan shayin."
Yace."Nagode Ummana." fita tayi daga dakin ranta fari sol babu shakka za tayi farin ciki idan al'amarin nan ya tabbata.
3qutar ne a jikinsa sai kawai ya sanya k'aramar
T-shirt a jikinsa ya fito daga dakin nasa a daidai lokacin da Kawu ya fito daga nasa d'akin da shirin tafiya kasuwa.
'Dan risinawa yayi yace.''Kawu barka da asubah." Ba tare da ya kalleshi ba ya amsa da "Barka dai." ya d'aga labulan d'akin Ummatu yana mata magana. ganin haka yasa da sauri ya fita daga gurun.
Gwaggo na kokarin fitowa daga d'akin ya shiga tace."Ai dama yanzu nake maganarka ina cewa ko da kaina zan shiga gurin naku na dubaka naga baka shigo mun gaisa ba."
D'akin ya shiga babu walwala a tare dashi yace." Na d'an yi bacci ne."
Tace."Koda naji nima nace ko bacci kakeyi to zauna ga guri mu gaisa a nutse." gefanta take karkad'e masa tana marmatsar da abubuwa sai kace barasake ne zai zauna a gurun.
Hankalinsa akanta tana bacci a gadon ba tare da tasan ya shigo dakin ba....Gwaggo ta lura da irin kallon 'kurrular da yake mata sai duk jikinta yayi sanyi itakam wannan jaraba ta isheta wai shin wane irin so yaron nan yake wa Sa'ida.
Labari take bashi wai dan duk ta dauke masa hankali jinta kawai yake amma gabadaya hankalinsa da tunaninsa baya kanta yana can tunani akan Sa'ida duk da yasan ya ga mai mata illah amma yana bala'in kishin Alhaji Nura akanta shi kad'ai yake so ya cigaba da dabdala a wannan ramin amma wani katon banza ya shigar masa gona.
Gwaggo haushi ya bata ganin ya'ki barin abinda yake tace.''Ni kam banta'ba ganin mara zuciya irinka ba."
Sumar kansa ya shafa babu sukuni yace."Me nayi miki kuma."? Tsaki taja tace."Tunda ka shigo kake kallon Sa'ida alhalin bacci take yi ko gaisawa ba muyi ba hankalinka gabadaya yana kanta to ka dai kiyaye kada ka jefa kanta a matsala domin naga idanuwanka sunyi ja."
Murmushi yayi yana kallonta yace."Waye yace miki ita nake kallo."? Tace."Ai makauniya ce ni." Dariya yasa yana sosa kansa tace."Ka karya kummalo."?
Girgiza kansa yayi tace."To bari na zuba maka abinci." Yace."Gwaggo ba zanci abinci da safe ba ki bani ruwan shayi." Tace."Aa Ni yau kunu nasha ruwan shayi ka tambayi mahaifiyarka."
Yace." Okey na manta ma da akwai a fulas a dakina idan nasha zanzo naci abincin." Tace."To shikkenan.
D'akin ne yayi shuru na minti biyu ya cigaba da satar kallon Sa'ida ta 'kasan ido Gwaggon ta kalleshi tana girgiza kanta Hankali tace."Kasan abinda yake faruwa ko.''?
Girgiza kansa yayi yana d'an ya mutsa fuskarsa yace."Sai kin fad'a."
Juyawa tayi ta d'an kalli inda take kwance ta dawo da hankalinta kansa 'kasa-'kasa tace."Ai *GA IRINTA NAN!* ta guje ka ta auri wanda take so gashinan tana fuskantar matsala a gurinsa da matarsa ya hanata komawa gurin aiki kuma baya biya mata bukatarta.''
Jim yayi yana kallonta kafin yace."Gwaggo ban gane baya biya mata bukata ba."?
Waiwaya wa tayi ta sake kallon inda take kwance tayi 'kasa da murya tace."Bukatarta ta gurin auratayya mana wai baya son haihuwa shine yake inzali a waje ma'ana yana zubar da 'kwayoyin haihuwarsa."
Cike da mamaki yake kallonta! tana so ta 'kara tabbatar masa da maganar na tashi zaune duk sai suka diririce mussaman Gwaggo da gabadaya yanayin ta ya nuna na marasa gaskiya.
Yi nayi tamkar ban fahimci abinda suke ba na mike na fita, brush nayi na dawo d'akin na tarar dasu suna wata hirar.
Ta kalleni da fad'in '"Ga kayan karin kummalo nan." Ba tare da nace mata komai ba na hau bud'e kwanukan...........dakin yayi shuru na minti biyu kafin naji sautin muryarsa da fadin" Kin tashi lafiya."?
Kaina a kasa na amsa da lafiya lau." Gwaggo tace."Kina bacci dazu da safe aka kira wayarki kin san ni ban iya dauka ba shiyasa na barta ta katse."