Sashe 71
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace." Tunda na gane abinda kike so to ba zanyi ba sai na galabaitar dake tukkuna zaki san wanda kike wa rashin kunya.''
Hanya ya kama zai fita nace."Tsaya ka saurare ni." Tsayawa yayi yana watsa min kallon banza Nasa hannu na goge hawayen fuskata nace."Yaya Aminu nagode da irin sakayyar da kayi min inaso na sanar maka da cewa shi Ubangiji baya bacci kuma shine alkalin kowa na rantse da girman zatin sa ba zan yafe maka k'azafin da kayi min ba."
Tsaki yaja ya bude kofa zai fita nace." Kuma zan cigaba da rokon sa akan ya raba ni da kai tunda kai ka kasance azzalimi mara tsoron Allah." Da sauri ya dawo inda nake yana huci! yace." Idan kika sake magana a gurin nan sai na baki mamaki wallahi." shuru nayi ina kallonsa hawaye na sauka a saman fuskata ko a mafarki ban ta'ba tsammanin mutumin zaiyi min haka ba.
Sosai ya tsaya a kaina yaci min mutumci iya son ransa ya kad'a kansa ya fita yana fad'in zai ga wanda ya isa yasa shi ya sake ni.
Hakika na tsorata da al'amarin mutuka saboda haka yana fita na tashi da sauri na harhad'a kaya na a kwati na dauka da sauri na kama hanyar hotoro ina addua akan Allah ya bani rinjaye a kansa.
Kici'bus nayi dashi a lokacin da nake kokarin shiga gidan shi kuma yana fitowa fuskarsa kawai na kalla gabana ya fadi da sauri na dauke kaina nayi gaggawar jan akwatin kaya na domin barin gurin.
Ido jawur ya tare min hanya "Sa'ida ni zakiyi wa haka ko."? Yanda ya fadi maganar a kufule shi ya nuna min cewar a cikin bacin rai yake.
Cikin jarumta nace." Me nayi maka."? Da kyar ya hadiyi wani yawu mai d'acin gaske yace."Me yasa kika kasa hakuri kika fad'awa mahaifina tsakaninmu."
Dauke kaina nayi nace."Saboda na gaji da zama da kai ina bukatar rabuwa da kai shiyasa na shedawa mahaifinka domin hausawa suna cewa ta inda aka hau ta nan ake sauka."
Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace."To bukatar ki ta biya Alhaji ya tursasa ni na sake ki ba dan raina yaso ba."
Wani irin sanyi naji a zuciyata nace."Alhamdulillahi Allah nagode maka nasan yanzu dai ka gazgata cewa Allah na kowa ne ba naka bane kai kad'ai."
Shuru yayi yana kallona idanunsa sunyi jawur.....Ratse shi nayi zan wuce ya rike hannuna yana marairaice fuska yace."Don Allah kiyi hakuri ki dawo mu zauna ina son ki sosai zan nemi magani a duk inda yake."
Murmushin takaici nayi nace." Yaya Aminu kenan ai da wannan matsalar ce kad'ai da kai to da da sauki amma bari na fada maka cewa kai duk macan da ka aura to ba zaka ta'ba zaman lafiya da ita ba saboda halayenka."
Cikin sanyin murya yace."Wane irin halaye ne dani Sa'ida duk fa wasu abubuwa da nake miki kece kika janyo amma bana miki mugunta.
Girgiza kaina kawai nayi na ja akwatin kayana na barshi a gurin.......Jiki a mugun mace ya bude motarsa ya shiga yana mamakin yanda al'amarin ya sauya a yanda yaga mahaifin nasa na son auran bai ta'ba tsammanin zai yanke musu irin wannan hukuncin ba, sai bayan ya rubuta sakin ne yaji wani masifar kaunarta a cikin zuciyarsa shi kansa yasan yayi babban rashi duk da bai cika cikakken namiji ba amma yasan yarinyar zata zame masa garkuwa ko babu komai jamaa zasu dinga yi masa kallon cikakken mutum tunda yana da iyali shin yanzu wace mace zai aura da lalurarsa ta zauna dashi a haka a gaskiya abun da kamar wuya.
*****
Sati na biyu a gidan Alhaji hankali ya kwanta sosai kullum ina tare da mahaifiyata tana kwantar min da hankali akan irin kaddarar rayuwa ta.............Gwaggo kuwa data samu labarin mutuwar auran sam bata nuna damuwa da alhini ba koda tazo gidan Alhajin ma cewa tayi Allah yasa haka shi yafi alkairi Kawu Iro ne kawai ya nuna damuwarsa tamkar ya zubar da hawaye saboda damuwa rayuwar yarinyar ce take bashi tausayi har yanzu Allah bai bata nagartaccen namiji ba......Kasa hakuri nayi da zata tafi nace."Gwaggo kwanaki da mukayi waya da Khalid yace zai zo gida ko."
Tace."Eh ai yazo yau kwanansa goma sha biyu da zuwa sai da kullum baya zama jama'a sun takura masa sun mayar mana da kofar gida sansani su cika mana kunne da ihu! bayan 'yan maula wanda suke dako mana sammako da sassafe ya basu kudi dangin Rabi ma suyi ta damunsa da bani-bani."
Dariya ce ta kwace min ina yi nace."Haba Gwaggo sai kace tsohowar redio daga tambaya kin saki baki sai zuba kike kamar kanya."
Tsaki taja ta kalli Umma Habiba da fadin."Habiba ki duba magana ta da kyau akwai gaskiya a ciki wallahi tunda yaron nan ya dawo jama'a sun'ki barinsa ya huta wai daga jin labarin yaci kofin gold da miliyoyin kudi da motoci shine fa aketa cika mana kofar gida ni kaina idan na fito matasan layi kamar zasuyi min sujjada saboda tsabar kwadayi.
Umma Habiba na murmushi tace."Gwaggo ai arziki ne amma dai suma abinda suke bai dace ba haba ai sa barshi ya huta tukkuna.
Tace."Wallahi kuwa ai abin da takaici sai kinga yanda Dangin uwarsa suke tururuwar zuwa gidan kamar marasa hankali."
Nace."Gwaggo ki kyalesu don Allah babu ruwanki saboda nasan halinki da shiga sabgar da bata shafe ki ba."
Tace."Oh! o dama ni ina ruwa na abun ne dai yake ban haushi." Umma Habiba tace."To Allah dai ya kyauta shi kuma Allah ya kara masa daukaka ya kareshi daga sharri masu sharri." Gabadaya muka amsa da "ameeen ya Allah."
Tace."Sa'ida ki tashi ki shirya mu tafi gida." Umma Habiba sunkuyar da kanta tayi domin ba taso Gwaggon taga kamar dasa hannunta a gurin zaman Sa'idan a gidan.
Nace."Gwaggo kije kawai insha Allahu gobe ko jibi zan biyo bayan ki."
Tsaki taja tace."In banda rashin zuciya irin naki namiji ya sake ki amma ki zauna musu a gida kamar wacce ta rasa gurin zama to idan sha'awar gidan bulo da bulo kike ki kwantar da hankalin Khalid yana nan yana shirye-shiryen ruguje gidan ya sanja mana gini na zamani."
Umma Habiba tace."Haba Gwaggo ai Sa'ida bata da inda ya kai gidan ubanta komai lalacewarsa nan ne tushenta sabida haka don Allah ki daina wannan maganar."
Ta'be bakinta tayi tace."To ai nima abinda na gani kenan gashi ke da kika haife ta kin kasa tsawatar mata ta dawo inda take da gado."
Umma Habiba tace."Kiyi hakuri dan Allah Sa'ida ki tashi ki had'a kayan ki ku tafi." Ajiyar zuciya kawai na sauke na mike domin shirya kayana Gwaggo farin ciki yasa ta zauna kan kujera tana jan Umma Habiba da hira duk Rabi ta Khalid ce Umma Habiba murmushi kawai take dama ba tun yau ba tasan matar da jarabar son jikoki komai nata na Sa'ida da Khalid ne....
: *93*
A bakin kofar gidan adaidaita sahu ta ajiye mu ganin tarin mutane a kofar gidan yasa gabana ya yanke ya fadi kallonta nayi ina kokarin magana tace."Ai kada kiyi mamakin ganin jama'a a kofar gidan dama ai na fad'a miki haka suke damun mutane watakila ai Khalid din ya dawo tunda ga motarsa can a tsallaken hanya". ajiyar zuciya na sauke nace."Wallahi Gwaggo ba kiji yanda gabana ya fadi ba ganin mutane a kofar gidan ya tuna min da mutuwar mahaifina." Girgiza kanta kawai tayi ba tare da tace komai ba ta fita daga babur din tana gyara lullu'binta fitowa nayi ina kokarin daukar akwatin kaya na dake can baya da sauri wasu matasa suka karaso gurin suna fadin."Gwaggo sannu da zuwa unguwa kika je."? Tace."Eh naje hotoro ne." Sannu da zuwa sukayi mata kafin daya daga cikinsu ya dauko min akwatina sai sannu da hanya suke mana, idona ne ya sauka kan motar tasa dake can gefe a ajiye na dan tsaya ina kallon motar da mamakin k'ayatuwar ta duk irin tarin motocin Yaya Aminu banta'ba ganin shi da irinta ba da alama dai motar sabuwa ce kuma ba tayi yawa a gari ba, ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata nace."Lallai Khalid ya samu duniya lokaci guda ya tara dukiya da jama'a gashi ya zama super star kowa sai ji yake dashi......... Hayaniya ce ta cika gidan Gwaggo ta kalleni da fadin."Kin gani ko ai kullum gidan nan a cike yake dangin Rabi maza da mata harda masu aure suzo suci na rana dana dare saboda tsabar rashin tunani uwar tasu Baito tana kallonsu ba zata ha nasu ba.
Nace."Gwaggo dan Allah kiyi abinda yake gabanki kada ki shiga sabgarsu rai yazo yana b'aci."! Tace."Aikuwa sai na shiga na fito dashi watakila yana ciki sun tasa shi a gaba ko abinci basa bari yaci a nutse."
Kafin nayi magana ta tura kofar gurin ta shige sai surutai take, ni dai sakin bakina nayi kawai ina bin ta da kallo na rasa yaushe Gwaggo zata daina shiga abinda be shafe ta ba.
"Eh ai dama wannan dalilin ne yasa ta kashe auranta taji yaro yayi kudi ya zama attajiri duniya tasan dashi shine ta kashe auranta domun ta aureshi to mutukar ni na haifi Khalid ba zan bari ya aureta ba taje can ta auri daidai da ita." Maganar Ummatu ce ta daki kunnan gwaggo sai tayi lamfo ta cigaba da saurarar tattaunar da sukeyi Baito tace." Ai ba zama zakiyi ki saki baki ba domin dai kin san wannan kakar tashi idan ta gindaya masa abu baya tsallakewa kiyi musu farraqu gabadaya yaji ya tsaneta dakinta ma ya daina shiga idan ba haka kikayi ba to babu shakka zata iya sanya shi ya auri 'yar iskar yarinyar nan mai kashin tsiya."
Ummatu tace."Ai yanzu bana fargaba tunda ina da kudin da zan zubewa ko wane irin malami yayi min taimako insha Allahu gobe ko jibi da wurwuri zan fito muje gurin taimakon." Baito tace."Yawwa to hakan shine dubara mai kyau."
Hanya ya kama zai fita nace."Tsaya ka saurare ni." Tsayawa yayi yana watsa min kallon banza Nasa hannu na goge hawayen fuskata nace."Yaya Aminu nagode da irin sakayyar da kayi min inaso na sanar maka da cewa shi Ubangiji baya bacci kuma shine alkalin kowa na rantse da girman zatin sa ba zan yafe maka k'azafin da kayi min ba."
Tsaki yaja ya bude kofa zai fita nace." Kuma zan cigaba da rokon sa akan ya raba ni da kai tunda kai ka kasance azzalimi mara tsoron Allah." Da sauri ya dawo inda nake yana huci! yace." Idan kika sake magana a gurin nan sai na baki mamaki wallahi." shuru nayi ina kallonsa hawaye na sauka a saman fuskata ko a mafarki ban ta'ba tsammanin mutumin zaiyi min haka ba.
Sosai ya tsaya a kaina yaci min mutumci iya son ransa ya kad'a kansa ya fita yana fad'in zai ga wanda ya isa yasa shi ya sake ni.
Hakika na tsorata da al'amarin mutuka saboda haka yana fita na tashi da sauri na harhad'a kaya na a kwati na dauka da sauri na kama hanyar hotoro ina addua akan Allah ya bani rinjaye a kansa.
Kici'bus nayi dashi a lokacin da nake kokarin shiga gidan shi kuma yana fitowa fuskarsa kawai na kalla gabana ya fadi da sauri na dauke kaina nayi gaggawar jan akwatin kaya na domin barin gurin.
Ido jawur ya tare min hanya "Sa'ida ni zakiyi wa haka ko."? Yanda ya fadi maganar a kufule shi ya nuna min cewar a cikin bacin rai yake.
Cikin jarumta nace." Me nayi maka."? Da kyar ya hadiyi wani yawu mai d'acin gaske yace."Me yasa kika kasa hakuri kika fad'awa mahaifina tsakaninmu."
Dauke kaina nayi nace."Saboda na gaji da zama da kai ina bukatar rabuwa da kai shiyasa na shedawa mahaifinka domin hausawa suna cewa ta inda aka hau ta nan ake sauka."
Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace."To bukatar ki ta biya Alhaji ya tursasa ni na sake ki ba dan raina yaso ba."
Wani irin sanyi naji a zuciyata nace."Alhamdulillahi Allah nagode maka nasan yanzu dai ka gazgata cewa Allah na kowa ne ba naka bane kai kad'ai."
Shuru yayi yana kallona idanunsa sunyi jawur.....Ratse shi nayi zan wuce ya rike hannuna yana marairaice fuska yace."Don Allah kiyi hakuri ki dawo mu zauna ina son ki sosai zan nemi magani a duk inda yake."
Murmushin takaici nayi nace." Yaya Aminu kenan ai da wannan matsalar ce kad'ai da kai to da da sauki amma bari na fada maka cewa kai duk macan da ka aura to ba zaka ta'ba zaman lafiya da ita ba saboda halayenka."
Cikin sanyin murya yace."Wane irin halaye ne dani Sa'ida duk fa wasu abubuwa da nake miki kece kika janyo amma bana miki mugunta.
Girgiza kaina kawai nayi na ja akwatin kayana na barshi a gurin.......Jiki a mugun mace ya bude motarsa ya shiga yana mamakin yanda al'amarin ya sauya a yanda yaga mahaifin nasa na son auran bai ta'ba tsammanin zai yanke musu irin wannan hukuncin ba, sai bayan ya rubuta sakin ne yaji wani masifar kaunarta a cikin zuciyarsa shi kansa yasan yayi babban rashi duk da bai cika cikakken namiji ba amma yasan yarinyar zata zame masa garkuwa ko babu komai jamaa zasu dinga yi masa kallon cikakken mutum tunda yana da iyali shin yanzu wace mace zai aura da lalurarsa ta zauna dashi a haka a gaskiya abun da kamar wuya.
*****
Sati na biyu a gidan Alhaji hankali ya kwanta sosai kullum ina tare da mahaifiyata tana kwantar min da hankali akan irin kaddarar rayuwa ta.............Gwaggo kuwa data samu labarin mutuwar auran sam bata nuna damuwa da alhini ba koda tazo gidan Alhajin ma cewa tayi Allah yasa haka shi yafi alkairi Kawu Iro ne kawai ya nuna damuwarsa tamkar ya zubar da hawaye saboda damuwa rayuwar yarinyar ce take bashi tausayi har yanzu Allah bai bata nagartaccen namiji ba......Kasa hakuri nayi da zata tafi nace."Gwaggo kwanaki da mukayi waya da Khalid yace zai zo gida ko."
Tace."Eh ai yazo yau kwanansa goma sha biyu da zuwa sai da kullum baya zama jama'a sun takura masa sun mayar mana da kofar gida sansani su cika mana kunne da ihu! bayan 'yan maula wanda suke dako mana sammako da sassafe ya basu kudi dangin Rabi ma suyi ta damunsa da bani-bani."
Dariya ce ta kwace min ina yi nace."Haba Gwaggo sai kace tsohowar redio daga tambaya kin saki baki sai zuba kike kamar kanya."
Tsaki taja ta kalli Umma Habiba da fadin."Habiba ki duba magana ta da kyau akwai gaskiya a ciki wallahi tunda yaron nan ya dawo jama'a sun'ki barinsa ya huta wai daga jin labarin yaci kofin gold da miliyoyin kudi da motoci shine fa aketa cika mana kofar gida ni kaina idan na fito matasan layi kamar zasuyi min sujjada saboda tsabar kwadayi.
Umma Habiba na murmushi tace."Gwaggo ai arziki ne amma dai suma abinda suke bai dace ba haba ai sa barshi ya huta tukkuna.
Tace."Wallahi kuwa ai abin da takaici sai kinga yanda Dangin uwarsa suke tururuwar zuwa gidan kamar marasa hankali."
Nace."Gwaggo ki kyalesu don Allah babu ruwanki saboda nasan halinki da shiga sabgar da bata shafe ki ba."
Tace."Oh! o dama ni ina ruwa na abun ne dai yake ban haushi." Umma Habiba tace."To Allah dai ya kyauta shi kuma Allah ya kara masa daukaka ya kareshi daga sharri masu sharri." Gabadaya muka amsa da "ameeen ya Allah."
Tace."Sa'ida ki tashi ki shirya mu tafi gida." Umma Habiba sunkuyar da kanta tayi domin ba taso Gwaggon taga kamar dasa hannunta a gurin zaman Sa'idan a gidan.
Nace."Gwaggo kije kawai insha Allahu gobe ko jibi zan biyo bayan ki."
Tsaki taja tace."In banda rashin zuciya irin naki namiji ya sake ki amma ki zauna musu a gida kamar wacce ta rasa gurin zama to idan sha'awar gidan bulo da bulo kike ki kwantar da hankalin Khalid yana nan yana shirye-shiryen ruguje gidan ya sanja mana gini na zamani."
Umma Habiba tace."Haba Gwaggo ai Sa'ida bata da inda ya kai gidan ubanta komai lalacewarsa nan ne tushenta sabida haka don Allah ki daina wannan maganar."
Ta'be bakinta tayi tace."To ai nima abinda na gani kenan gashi ke da kika haife ta kin kasa tsawatar mata ta dawo inda take da gado."
Umma Habiba tace."Kiyi hakuri dan Allah Sa'ida ki tashi ki had'a kayan ki ku tafi." Ajiyar zuciya kawai na sauke na mike domin shirya kayana Gwaggo farin ciki yasa ta zauna kan kujera tana jan Umma Habiba da hira duk Rabi ta Khalid ce Umma Habiba murmushi kawai take dama ba tun yau ba tasan matar da jarabar son jikoki komai nata na Sa'ida da Khalid ne....
: *93*
A bakin kofar gidan adaidaita sahu ta ajiye mu ganin tarin mutane a kofar gidan yasa gabana ya yanke ya fadi kallonta nayi ina kokarin magana tace."Ai kada kiyi mamakin ganin jama'a a kofar gidan dama ai na fad'a miki haka suke damun mutane watakila ai Khalid din ya dawo tunda ga motarsa can a tsallaken hanya". ajiyar zuciya na sauke nace."Wallahi Gwaggo ba kiji yanda gabana ya fadi ba ganin mutane a kofar gidan ya tuna min da mutuwar mahaifina." Girgiza kanta kawai tayi ba tare da tace komai ba ta fita daga babur din tana gyara lullu'binta fitowa nayi ina kokarin daukar akwatin kaya na dake can baya da sauri wasu matasa suka karaso gurin suna fadin."Gwaggo sannu da zuwa unguwa kika je."? Tace."Eh naje hotoro ne." Sannu da zuwa sukayi mata kafin daya daga cikinsu ya dauko min akwatina sai sannu da hanya suke mana, idona ne ya sauka kan motar tasa dake can gefe a ajiye na dan tsaya ina kallon motar da mamakin k'ayatuwar ta duk irin tarin motocin Yaya Aminu banta'ba ganin shi da irinta ba da alama dai motar sabuwa ce kuma ba tayi yawa a gari ba, ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata nace."Lallai Khalid ya samu duniya lokaci guda ya tara dukiya da jama'a gashi ya zama super star kowa sai ji yake dashi......... Hayaniya ce ta cika gidan Gwaggo ta kalleni da fadin."Kin gani ko ai kullum gidan nan a cike yake dangin Rabi maza da mata harda masu aure suzo suci na rana dana dare saboda tsabar rashin tunani uwar tasu Baito tana kallonsu ba zata ha nasu ba.
Nace."Gwaggo dan Allah kiyi abinda yake gabanki kada ki shiga sabgarsu rai yazo yana b'aci."! Tace."Aikuwa sai na shiga na fito dashi watakila yana ciki sun tasa shi a gaba ko abinci basa bari yaci a nutse."
Kafin nayi magana ta tura kofar gurin ta shige sai surutai take, ni dai sakin bakina nayi kawai ina bin ta da kallo na rasa yaushe Gwaggo zata daina shiga abinda be shafe ta ba.
"Eh ai dama wannan dalilin ne yasa ta kashe auranta taji yaro yayi kudi ya zama attajiri duniya tasan dashi shine ta kashe auranta domun ta aureshi to mutukar ni na haifi Khalid ba zan bari ya aureta ba taje can ta auri daidai da ita." Maganar Ummatu ce ta daki kunnan gwaggo sai tayi lamfo ta cigaba da saurarar tattaunar da sukeyi Baito tace." Ai ba zama zakiyi ki saki baki ba domin dai kin san wannan kakar tashi idan ta gindaya masa abu baya tsallakewa kiyi musu farraqu gabadaya yaji ya tsaneta dakinta ma ya daina shiga idan ba haka kikayi ba to babu shakka zata iya sanya shi ya auri 'yar iskar yarinyar nan mai kashin tsiya."
Ummatu tace."Ai yanzu bana fargaba tunda ina da kudin da zan zubewa ko wane irin malami yayi min taimako insha Allahu gobe ko jibi da wurwuri zan fito muje gurin taimakon." Baito tace."Yawwa to hakan shine dubara mai kyau."