← Book details Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 90

Sashe 65

Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Duk d'aurewar da yake sai da yayi dariya ya kalleta tana goge hawaye yace."Idan sun karya ni ai ai sai na dawo gida kiyi jinyyata."
Girgiza kanta tayi tace "Bana fatan haka Khalid na fiso kaje ka dawo lafiya." Yana kokarin magana kira ya shigo wayarsa Salmanu ne sai yayi sauri ya daga wayar tare da sawa a kunnensa hanyar fita ya nufa yana amsa wayar hade da jan jakar kayansa....Gwaggo da Kawu suka bishi da kallo tare da bin shi da kyawawan addua gami da fatan alkairi.
[
******
Tun bayan kwanaki uku da suka wuce Yaya Aminu ya daina amfani da maganin gurin Uwale da farko dai kamar gaske duk sanda zan kawo masa maganin zai kar'ba yasha yana ya mutsa fuskarsa sannan idan dare yayi yakan kar'bi na shafawar wanda aka had'a da manshanu ya shafa a gabanshi wani lokacin ma ni yake sawa ina shafa masa maganin a gurin....amma kuma yanzu ban san abinda yasa ba duk sanda zanyi masa maganar maganin sai rai na da nasa ya 'baci! gabad'aya hankalina ya tashi da abinda yake yi na rashin arziki.

Samun sa nayi a kwance a dakinsa na zauna kusa dashi, ya kalleni da fadin."Sa'ida kina da damuwa ne."? Girgiza kaina nayi raina a k'untace nace."Yaya Aminu shifa magani ko wane iri ne hakuri yake bukata babu yanda za'ayi ace daga fara shan maganin ka kwana uku kaga aikinsa a jikin ka dan Allah kayi hakuri ka daure ka cigaba da shan maganin nan."

Shuru yayi be tanka ba na kalleshi da fadin .''Yaya Aminu magana fa nake dan Allah dan Annabi kada ka bani kunya ka bani hadin kai gurin amfani da maganin nan."

Ido a rufe yace."Sa'ida bafa zan sake shan maganin nan ba domun kashe min jiki yake wai shin baki ga yanda na koma bane kullum ina kwance a gida ina bacci sai kace malalaci wannan wane irin banzan magani ne."?

Murya na rawa nace."Ai ko wane magani da irinsa watakila aiki yake a jikinka shiyasa yake kashe maka jiki kuma shi na shafawar kamar yana aiki ko."?

Shuru yayi min. na mike a nutse na dauko 'yar k'aramar robar maganin na zauna kusa dashi hannu na dora a jikinsa da fadin."Dan Allah ka bari na shafa maka kaga jiya da daddare ba'a shafa ba kuma mai maganin yace kada a tsallake ko wace rana kwana bakwai za'ayi ana shafa maganin.

A fusace! ya mike zaune da fadin."Shin wai me maganin nan Ubanki ne ko kuma Kawun ki."!? Sakin baki nayi ina kallonsa gabana na wani irin faduwa." fuska a tur'bune ya cigaba da cewa"Haba kin dame ni akan abinda yake cutar dani dole ne? idan kin damu kiji ki samo wani maganin amma bazan 'kara amfani da wannan ba domin baya amfana min komai sai wahala."

Murya na rawa nace."Yaya Aminu abun har ya kai da zagi kuma." Komawa yayi ya kwanta yana jan tsaki! hawaye suka zubo min kawai na zuba masa ido ina kallonsa takaici da bakin ciki kamar su kashe ni.
Bacci ne ya dauke shi na mike jiki a sanyaye na fita daga dakin ina tunanin ta inda zan 'bullowa al'amarin.

Sai bayan hudu na yamma ya fito tsaf dashi sai kamshi yake fuskarsa babu walwala ya tsaya a kaina yana magana. ''Yanzu idan banda lalaci da tasirin wannan maganin da kika kawo mai zai sanya ni kwanciya a gida nayi ta bacci har la'asar ban fita ba bayan akwai jama'ar dake jira na a waje."

Hannu na daga masa babu walwala a tare dani nace."Yaya Aminu ni dai yanzu ba wata magana nake nema ba kaje kawai Allah ya bada sa'a magani kuma zan zubar dashi tunda baka bukata."

Yace."Hakan shi yafi alkairi domin ba zanyi amfani da abinda zai cutar dani ba." shuru nayi masa. ya kalli agogon hannunsa da fadin."Ni na fita." kasa-kasa nace."Allah ya bada sa'a." Ya amsa da ameeen tare dayin gaba.

Bayan kwana goma da faruwar al'amarin sai ga Uwale tazo tunda na ganta ita kadai nasan akwai abinda ke tafe da ita bayan mun gaisa na kawo mata abinci taci ta koshi sai ta kalle ni a tsanake tace."Sa'ida shuru ina ta tsammanin zuwanki domin naji abinda yake faruwa shuru baki zo ba shine nace to idan zan koma gurin me maganin na shigo na tambayeki halin da ake ciki.

Jim nayi na minti biyu kafin nace."Uwale magani yayi kyau sosai." Yanda na fadi maganar cikin inda-inda yasa ta kalle ni da fadin."Anya kuwa Sa'ida."? zuciyata ce ta karye dama neman wanda zai rarrashe ni nake ina kuka nace."Uwale mutumin nan yaki bani had'in kai tunda yayi amfani da maganin nan na kwana uku ya daina amfani dashi karshe ma sai ya kasance a duk sanda zanyi masa magana akan maganin sai munyi fada wannan dalilin yasa gabadaya na tattara maganin na zubar dasu."

Uwale ta dinga girgiza kanta tana mamakin al'amarin tace"Anya Sa'ida wannan mijin naki zai amince ku rufawa kanku asiri kuwa? wace irin rayuwa ce wannan ace namiji babu lafiya amma ba zai sha magani ba wane irin hali yake so ki shiga."?

Hawaye na share nace."Uwale wai cewa yayi maganin yana kashe masa jiki yayi ta sashi bacci." Uwale tace"To idan banda abinsa ai haka ake so alamun maganin yana tasiri a jikinsa."
Nace"To wallahi babu yanda banyi dashi ba ya'ki sha sai fad'a yake wai maganin cutar dashi yake."

Tsaki taja tace."To ai shikkenan kansa yayi wa ke yanzu wace shawara kika yankewa kanki."? Hawaye na zuba nace "Uwale wace shawara zan cigaba da hakuri kawai." Girgiza kanta tayi tace."Aa ba za'ayi haka ba Sa'ida ai yana da magabata saboda haka kije ki samu iyayensa da maganar idan kika ce zaki cigaba da hakuri to zaki cutar da kanki saboda haka kije ki shedawa mahaifiyarsa halin da ake ciki." Ajiyar zuciya na sauke nace."Shikkenan Uwale zanyi kokarin zuwa insha Allahu amma don Allah kada naji maganar nan a bakin kowa Uwale ni bana so sirri na ya fita ko'ina."

Tace."Haba kada ki damu Sa'ida babu wanda zaiji maganar nan." Mikewa nayi na shiga daki na dauko mata kudi, ta kar'ba tana ta godiya direba nasa ya dauketa a mota domin ya kaita inda ta nufa.
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*82&83*
Bayan tafiyar Uwale na jima a zaune ina nazari akan shawararta tabbas dole manya su shiga cikin al'amarin tunda duk iya bakin k'okari nayi akan kada maganar ta fita waje wani yaji ya'ki bani had'in kai ni naso ace daga ni sai shi muka kashe matsalarmu amma rashin fahimtarsa yasa ya mayar da al'amarin wani iri mutukar kuwa nace zan cigaba da zama dashi a haka to rayuwata tana cikin garari tunda ni Allah ya hallice ni cikin masu tsabanin bukata wannan dalilin ya sanya kawai na yanke shawarar tunkarar iyayensa da maganar sai dai kuma ban san ya za'ayi na iya fad'a musu maganar ba........''Kawai idan kinje gidan ki samu mahaifiyarki ki sheda mata halin da kike ciki a gidan auranki." zuciyata ce ke tunasar dani abinda ya dace, ajiyar zuciya na sauke na amince da shawarar Uwale da kuma shawarar da zuciyata ta bani akan al'amarin.

Bai dawo gidan ba sai bayan tara na dare koda ya dawo din bayan yayi wanka falo ya fito ya zauna yana abinda ya saba lissafi da amsa kiran waya duk yabi ya wani murtuke fuskarsa dan kada nayi masa maganar magani. sai kawai na tashi na bar masa falon na shiga dakina nayi wanka na kimtsa na kwanta kan gado ina tunanin yanayi na rayuwa bacci ne ya dauke ni na dinga wani mummunan mafarkin da ya sani tashi a firgice ina takure jiki na bedlamp na kunna ina wulkita idona a dakin gani nake kamar yaron yana dakin ya 'buya a wani gurin a sanyaye na sauko daga gadon na shiga duba bayan labule gani nake kamar ya 'boya a wani gurin.

Jiki a mace na shiga toilet na wanke jikina na fito na zauna gefan gado tare da zabga tagumi! yanayin yanda mukayi mu'amula da yaron a cikin mafarkin tamkar a zahiri shine al'amarin yayi masifar gigita ni gabadaya nipples dina sun mi'ke sun dame bu da kyaikyayi ga wani irin ruwa dake fita daga jikina. zazzafar ajiyar zuciya na sauke na koma na kwanta tare da rungume filo rintse idona nayi ina sake tunano yanda yaron yake sarrafa ni a mafarkin babu abinda yafi gigita ni sai girman joystick d'inshi sosai ta cika min mara ta cif-cif! yanda kuma yake buguna yana sucking d'in breast d'ina shi ya dinga sanya ni sakin ihu ina rungumeshi da kiran sunansa, ina daf da samun gamsuwa mafarkin ya katse...."Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un ! Astagafirullah ya Allah." abinda nake ta nanatawa kenan ina birgima a gadon masifaffen feelings na taso min.

Ganin ina neman mutuwa ne yasa na mike a jigace na nufi dakin Yaya Aminu duk da nasan ba wani abun zan samu ba ina ganin dai ko rungume ni yayi ya tatta'ba ni zan samu saukin wani abun.

A bude kofar take na shiga tare da mayar da kofar na rufe, yana kwance a gadonsa yana bacci hankalinsa a kwance.

Ajiyar zuciya na sauke na karasa a hankali na kwanta a kusa dashi tare da dora kaina a kirjinsa......Ajiyar zuciya dai na sake saukewa a hankali na shiga kiran sunansa, shuru be amsa ba sai kawai na shiga shashshafa sassan jikinsa gabana na fad'uwa na fara ko'karin sa hannuna a cikin wandonsa.

A firgice ya tashi zaune ya wani ture ni na matsa gefe guda.

Bedlamp ya kunna yana kallona hade da matsawa baya....na kalleshi da idanuwa na da suka k'ankance saboda fitinar dake damuna.

"Yaya Aminu ina cikin wani yanayi ka taimak.........Hannu ya daga min tun kafin na karasa yace." Sa'ida wane irin taimako zanyi miki kamar baki san komai ba me yake damun ki ne."?

Murya na rawa nace."Sha'awa ce ta taso min cikin dare Yaya Aminu mara ta ciwo take na rasa yanda zanyi dan Allah kayi wani abu."
Chapter 65 · 0% Book details