← Book details Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 90

Sashe 32

Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nace."Eh hakan yace insha Allahu gobe zai zo kuyi maganar." Gwaggo tace."To kaga shikkenan sai ka jira zuwansa kada ka fita kuma kuyi sa'bani."

Yace."Insha Allahu zan zauna nayi jiran zuwan nasa. Mi'kewa yayi da fad'in zai fita ya sha iska a waje." Gwaggo tace."Haba ai zafin ya isa muma yau kwanciyar tsakar gida zamuyi ai." Kawu yana kokarin saka takalmansa yace."Hakan yayi gwaggo ke Sa'ida sai ki fito ki dan gyara muku inda zaku kwanta din." Nace."To shikkenan." mikewa nayi na fito tsakar gidan domin na gyara mana inda zamu kwanta.

To kamar yanda dai Alhaji Nura yayi alias a run zuwa gurin Kawu su tattauna maganar haka din ne ya kasance domin Kawu a daran ranar ya kira wayar Alhaji Shamsu mijin mahaifiyata ya sheda masa dukkanin abinda yake da akwai Alhaji Shamsu yace babu damuwa insha Allahu zai fito da wuri ayi zaman dashi.

Sun tattauna abinda ya dace a tsakaninsu tinda dukkaninsu ba yara bane sun san harkokin kasuwanci mussaman Alhaji Shamsu shi ya 'kara karfafawa Alhaji Nura gwiwa akan tafiyar tasa amma kuma sai yace mai zai hana kawai a daura auran idan yaso in ya dawo sai ayi maganar tarewa.

Lokacin da yayi wannan maganar Kawu Iro hankalinsa ne ya tashi yayi shuru yana sauraran yaji amsar da zai bashi Alhaji Nuran yace yafi so ayi komai a lokacin da yake nan." Alhaji Shamsun yace to shikkenan babu damuwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi."

Dukkaninsu suka amsa da ameen ya Allah ." suka rabu cikin mutumci da girmama junansu.

****
*Bayan sati biyu*
Khalid da Salmanu mota suka bi da kayansu da kuma guzirin su domin zuwa Lego's dan su nemi aikin yi su kuma cigaba da gudanar da harkokinsu na buga kwallo a cewarsu duk inda ta fad'i sha ne, Salmanu lafiya lau suka rabu da mahaifiyarsa da da sauran 'yan uwansa shi kuwa Khalid babu sa albarka uwa da uba ya d'auki irin wannan tafiya aikuwa cikin dare suna tsakiyar titi motarsu na sharara gudu *da'u fataken dare!* ('Yan fashi) suka tare musu mota yana ganin haka yayi saurin bude wayarsa ya cire sim card dinsa yasa a bakinsa ya danne a kasan harshen sa......'Yan fashin suka dinga sakin harbi! ta ko'ina suka sanya dik wa'inda suke motar mata da maza suka fito suka kwanta a tsakiyar titi duk motar da ta karaso gurin sai sun tsayar da ita sun fito da mutanan ciki.....Daya bayan d'aya suka dinga binsu suna kar'be musu wayoyinsu wa'inda sukayi gardama a cikinsu suyi musu dukan mutuwa ganin haka yasa mutane suka tsorata domin tsira da ransu da lafiyarsu suka dinga mika musu wayoyinsu da jakkunan kayansu da guzurinsu.

Sai da suka kwace musu komai suka loda cikin motocinsu sannan suka dawo gurin da suke kwance suna haskasu.........Babban cikinsu ya tsuguna kusa da wata mata ta rungume d'anta sai kuka take ta hada uban gumi jikinta sai karkawa yake.

Fuskarta ya haska sosai yake 'karewa jikinta kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin akwai mamora a jikinta yasa ya kira daya daga cikin 'yan uwansa ya nuna masa ita da fad'in "Zamuje da ita mu biya bukatarmu."

Matar ta fashe da kuka tana waiwayen bayanta mijinta take nema can ta hangoshi ya rarrafo gurin cikin fitar hayyaci yace."Oga dan Allah kada kuyi mata wani mummunan abu ni ne mijinta tunda dai kun samu abunda kuke bukata shikkenan."

Wani wawan mari ya kwad'a masa a take hancinsa ya fashe da Jini yasa kan bindigar dake hannunsa ya dinga dukan kansa da mugun karfi har sai da yaga galabaitar dashi tukkuna ya kyaleshi ya fad'i a gurin jina jina dashi! matarsa da 'yarsa sai kuka suke a kansa.........Fizgo hannunta yayi ya hau janta a k'asa ta dinga ihu tana fad'in "Ku taimaka min kada ku bari ayi zina dani." 'Kwakkwaran motsi babu wanda yayi a gurin mijin nata ya rarrafa ya mike domin ceton matarsa dan fashin ya kai masa wawan duka ya fadi a gurin a sume.

Khalid yayi shahada ya mike da saurin gaske yace."Kai bawan Allah kaji tsoron Allah kuji tsoron ranar had'uwa dashi shin wai baka san matar aure ce ba kada kuyi zina da ita da nauyin aure a kanta Allah ba zai barku ba.

A sukwane! sukayo kansa dukkaninsu! Salmanu ya shiga tsananin tashin hankali ya dinga jan hannun Khalid din wai ya tsuguna ya basu hakuri Khalid ko gezau beyi ba yana tsaye suka karaso gurin babban cikinsu ya daga hannunsa zai kwada masa mari Khalid da sauri ya rike hannun.......Cike da mamaki jama'ar gurin suke kallonsa. Kafin kiftawar ido yaji saukar wani mugun duka a tsakiyar kansa...ihu! ya kurma yayin da lokaci guda yaji wani dummmm! a kunnesa tangad'i ya farayi Salmanu ya mike a zabure! yayi nufin rikeshi Danfashin da yake bayansa ya bangajeshi ya fad'i! 'katon dutsen dake hannunsa ya sake bugawa Khalid a kansa a take ya fad'i a gurin ya suma gefen kansa ya fashe sai zubar da jini yake........Fitilolinsu suka kashe gurin yayi duhu! dumd'um! suka ja matar nan tana kurma ihu! suka sanyata a motarsu suka tafi da ita.....

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*35&36*
Cikin tsananin tashin hankali Salmanu ya nufi inda Khalid ke kwance ya tarairayoshi jikinsa yana kiran sunansa, Jama'ar dake gurin suka rufo kansu gurin ya hargitse da kace nace kowa yana fadar albarkacin bakinsa akan abinda ya faru Salmanu shi dai babban damuwarsa abokinsa ya farfado! direban motar ne ya karaso gurin hannunsa rike da jarkar ruwa ya bude da saurin gaske ya shiga tuttulawa khalid ruwan a jikinsa, yana gamawa dashi da sauri ya karasa inda mijin matar nan yake a kwance shima ya daga jakar ruwan ya kwara masa a jikinsa cikin ikon Allah gabad'ayansu suka farfad'o cikin jigata Khalid ya dinga kiran sunan Allah yana jin yanda kansa ke wani irin sarawa! hannu yasa saman goshinsa ya shafo jini Salmanu yace."Sannu Khalid ai ka auna arziki." kallonsa kawai yayi ya juya yana kallon jama'a dake gurin suna surutai da hayaniyar kowa sai gyara jakar kayansa yake Yace."Salmanu ina matar nan take bana so su cutar da ita."

Salmanu yace ."Sai dai hakuri ai sun tafi da ita."

Kansa ya dafe yana kiran sunan Allah! Ihu! mai karfi sukaji da sauri ya dago kansa mijin matar nan ne yake kurma ihu mutane na rirrikeshi wai sai ya tafi neman matarsa jamaa sun hana shi ga 'yarsa sai sandara ihu take itama.

Khalid cikin karfin hali ya mike Salmanu yace."Ina zakaje Khalid kai ma fa kana bukatar taimako.

Yace."Salmanu mutumin can ya bani tausayi zanje na rarrashe ne."

Kafin Salmanun yayi magana ya bar gurin Salmanu yabi bayansa zuwa inda mutumin ke zaune jamaa sun kewaye shi suna bashi hakuri.

Khalid ya dafa kafad'arsa ya dinga rarrashin sa kancewa yayi hakuri ya barwa Allah insha Allahu Allah ba zai basu nasara akan matarsa ba.....Yana kuka yace."Matata ciki ne da ita d'an wata uku gashi bata da cikakkiyar lafiya mahaifiyarta na Lego's ta matsa min da cewa tana so taje ta gaisheta hakika dana san wannan tsautsayin zamu hadu dashi to da ban amince da tafiyar nan ba.

Khalid yace."Kayi hakuri abokina dukkanin abinda kaga ya faru da kai da matarka rubutacce:ne daga Allah kayi mata addua kawai akan Allah ya ku'btar da ita.

Kansa ya sunkuyar kasa hawaye masu zafin gaske suna zubo masa hakika yana son matarsa so mai tsanani yana jin tsoron 'yan fashin nan su haike mata su kasheta da wahala.

A firgice ta tashi zaune tana rarraba idanuwanta a dakin kafin ta fara lalube kan shimfid'arta salati takeyi a zuciyarta tana kiran sunan Allah.

Fitilar ta ta kunna dakin yayi haske jiki a sanyaye ta mike ta dauki buta ta fita bandaki ta shiga ta kama ruwa ta fito garin yayi tsit Allah yana saukar da ikonsa.

Alwala ta d'aura ta shiga dakin ta gyara dadduma ta tayar da sallah.

Nafila tayi raka'a biyu tayi sallama sai ta daga hannunta sama hawaye ya 'kwace mata tana kuka take fad'in "Ya Ubangiji Allah ka karkato da hankalin yaron nan gida Allah ka yafe masa kada ka d'ora masa mummunar kaddara Allah Khalidu mai laifi ne a gurinka Allah ka sassauta masa Allah kada ka jarrabe mu da abinda ba zamu iya ba." Kuka ne yaci k'arfinta hannuwanta a sama ta kasa saukewa.

A tsorace na mike zaune ina kallonta gabana na faduwa nace"Gwaggo lafiya meye kike kuka me ya faru."?

Adduar ta shafa a fuskarta murya a dushe tace."Sa'ida dan Allah da Annabi ki yafe wa Khalid abinda yayi miki kaddara ce ki yafewa dan uwanki ko ya samu sassauci.

A sanyaye nace."Gwaggo me ya faru dashi.?

Tana rawar murya tace."Mummunan mafarki nayi dashi Sa'ida amma kafin na farka daga baccin na manta ni dai nasan na ganshi cikin mawuyacin hali jina jina da jini.

Gabana ya fad'i! nace."Gwaggo mafarki ba gaskiya bane ki daina gazgazata shi." Girgiza kanta tayi tace."Sa'ida ni bazan kira kaina waliyyiya ba ba kuma zan kira kaina 'yar baiwa ba amma Allah yakan nuna min abu a mafarkina mai dadi ko mara dadi kuma mafarkin yakan zama gaskiya ko mutuwa za'ayi Allah yakan nuna min a mafarkina shiyasa hankalina ya tashi da yin wannan mummunan mafarkin.

Shuru nayi har yanzu kuma ban daina jin faduwar gaba. ta cigaba da cewa "Dan Allah kice kin yafe masa ko ya samu sassauci." A sanyaye nace"Gwaggo tuntuni na yafe masa ki kwantar da hankalin ki."

Tace."To nagode sosai Allah yayi miki albarka na amsa da ameeen ya rabbi.

Kasa komawa bacci mukayi har asubah tayi mukayi sallah muna idarwa tace lallai wai sai na kira mata shi a waya, to nima nawa 'bangaran jikina yayi sanyi da al'amarin ban yi mata musu ba na kunna wayata na fara laluben number sa.

Na kira sau kusan biyar bata shiga, nace"Gwaggo kin dai ji da kunnanki wayar taki shiga ko."

A sanyaye tace."Watak'ila sun kashe shi." naji gabana ya yanke ya fad'i!

Kallonta nayi hawaye na kwarara a fuskarta tace."Sa'ida na d'an tuno mafarkin ganin sa nayi wasu mutane masu baka'ken kaya sun zagaye shi da bundigogi a hannunsu suna ta dukansa."
Chapter 32 · 0% Book details