Sashe 64
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gwaggo tana kokarin magana Ummatu ta shigo gidan kafafunta fururu! gabadaya muka bita da kallo gani na a zaune yasa ta washe baki da fadin."Aa ashe amarya ce a gidan.''? babu yabo babu fallasa na gaisheta ina satar kallon jikinta. ta kalli su gwaggo da fadin."Sannunku da gida." Uwale ce kawai ta amsa Gwaggo a dakile tace."Yanzu Rabi ki fita tun farar safiya sai ana kiran magariba zaki dawo."? Shan kunu tayi da fadin."Gwaggo kafin na fita sai da na sheda miki cewa Hamara'u ce ta haihu 'yar dan uwana kuma mune iyaye dole muje da wurwuri muyi mata ayyuka." Gwaggo tace."Wane ayyuka Rabi ke dai kin biya yawon da kika saba dubi kafafunki."? Ummatu tabi kafafunta da kallo na minti biyu girgiza kanta tayi ta bar gurin.......aikuwa suka dasa gulmarta ita da Uwale sai magana suke kasa - kasa nace."Kuna dai rage mata zunubi duk inda taje ita da Allah ku dai babu ruwanku da wannan surutan da kuke gwara ku tashi kuyi alwala dan lokacin sallah yayi.
Uwale tana kokarin mikewa take fadin."Gaskiyarki Sa'ida Allah dai ya yafe mana amma a zahirin gaskiya abinda Rabi takeyi a gidan nan dole ne a taka mata burki."
Shuru nayi ban tanka ba suka mike tare da daukar butoci domin daura alwala.
Uwale sai da tayi sallar isha'i tukkuna ta tayi mana sallama ta tafi bayan ta sake jadadda min yanda za'ayi amfani da maganin data kar'bo.
Karfe takwas da rabi Yaya Aminu ya kira waya ta yace mani gashinan a waje na fito domin nayi masa jagora cikin gidan.
Na kalleta tana fama da redio a hannunta nace."Gwaggo Yaya Aminu yazo yana so ya shigo ku gaisa." Redion ta ajiye da fadin."To ai babu komai ya shigo mana." Mikewa nayi domin naje na shigo dashi.
Ina kokarin fita Kawu ya shigo zubewa nayi gwiwa a kasa ina gaisheshi cike da kulawa ya amsa yana ta farin ciki yace."Sa'ida ashe anan kika yini yanzu yanzu mijin naki yake sheda min."
Nace."Eh wallahi Kawu tun safe ina nan yace nazo na gaishe ku lokacin kuma da nazo kai ka fita dama inata addua Allah yasa kafin na tafi ka dawo mu gaisa."
Yace."Aikuwa ya kyauta sosai kuma naji dadin ganinku keda mijinki kicin koshin lafiya ina rokon Allah ya dawwamar miki da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan auranki."
A sanyaye na amsa da ameeen ya Allah Kawu." Yace."Kiyi maza kije ki shigo dashi yace yana so ya gaisa da Gwaggo." Nace."To Kawu." Hanya ya bani na wuce shi kuma ya karasa bakin kofar dakin mahaifiyarsa.
Gwaggo cikin girma da mutunci suka gaisa da Yaya Aminu kamar ba itace mai zagin sa da ganin aibun sa ba sai wasa take masa tana masa adduar fatan alkairi. Yaya Aminu da yake mutum ne mai saurin sabo ya saki jikinsa sosai suka dinga hira har ta zuba masa abinci ya zage ciki yana ci harda cire hula ita kuwa sai tsokanarsa take wai kada dai garin santi ya manta hularsa....Cikin wannan halin Khalid ya daga labulan dakin, ganin mu cikin raha da annushuwa yasa ya kirne fuskarsa kamar baya so ya miqa masa hannu da fadin"Barka da dare Alhaji." Yaya Aminu da sauri ya amsa da "Barka dai abokina ya kake ya al'amura."
Babu wani sakewa ya amsa da "Alhamdulillahi." Labulan dakin ya saki zai bar gurin Gwaggo da sauri tace."Jarumi ka shigo kaci abinci mana." Yana kokarin barin gurin yace."Sai an jima yanzu inada uziri." Gwaggo kasa'ke tayi tana tunani yanayin yanda yayi maganar a cunkushe ya nuna mata lallai akwai abinda yake damunsa.
Yaya Aminu sai da ya cika cikinsa tsaf da abinci Gwaggo yasha ruwa babu wani kyankyami ya goge bakinsa da hankici ya kalleta a tsanake yace."Uwargida ran gida nagode sosai yau naci abincin tsofaffi wanda na jima banci irinsa ba.
Gwaggo na dariya tace."To masha Allah ai haka nake so naji kana kira na da uwargida domin dama so nake na kar'be gidan gabadaya.'"
Dariya yayi ya sunkuyar da kansa minti biyu a tsakani ya kalleta da fadin."Gwaggo insha Allahu sha biyar ga azimi zaki je umara k'asa mai tsarki inaso kiyi min addua akan wasu bukatuna."
Gwaggo ta kalleshi cikin farin ciki da kuma tausayi tace."Aminu Allah ya yaye maka damuwarka nagode sosai daka za'be ni a matsayin me maka addua nagode da wannan karamcin.
Na kalleshi a sanyaye nace."Yaya Aminu Gwaggo ta gode sosai Allah ya saka da alkairi." Ya amsa da ameeen ai babu komai Sa'ida insha Allahu tare dani dake zamuje mu dawo." Nace."To Allah ya yarda Allah kuma ya amsa adduarmu.
Yaya Aminu mikewa yayi bayan ya duba agogon hannunsa ya kalleta da fadin."Gwaggo mu zamu tafi sai kinji kira ko."? Ta mike da sauri tana fadin.''To shikkenan Allah ya kaimu lokacin nagode.
Mayafi na na gyara na fito na same su a tsakar gida suna magana har Ummatu ta fito daga gurinta ya dauko kudi masu yawa ya bawa kowacce Ummatu bakinta ya kasa rufuwa sai juya kudin take a hannunta tana zabga godiya, Khalid kuwa na bakin rijiya a zaune yana gyaran fuskarsa uffan bece ba sai da muka zo fita Yaya Aminu ya tsaya yana masa magana Da kyar yace."A sauka lafiya." Tsabar bacin ran abinda yake yasa na watsa masa harara tare da jan tsaki nabi bayan mijina da sauri Gwaggo har soro ta rako mu tana mana fatan alkairi da godiyar abin alkairi.
Koda ta koma cikin gidan Khalid rufe ta yayi da masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, Gwaggo dai tasan akan abinda yasa yake bala'i da ta gaji da bashi hakuri sai kawai ta shiga daki ta barshi a gurin.........Bayan ya gama gyaran fuskar zuwa yayi ya tsaya bakin kofar dakin da fadin."Sabida kawai ya biya miki umara sai wani rawar jiki kike masa harda bashi abinci da kawo shi daki har nawa umarar take to ni insha Allahu aikin hajji zan kai ki wata shekarar wannan shashashan mutumin kudinsa na banza ne tunda ba'a hanyar halak ya samesu ba.
Gwaggo tace."Aa Khalid bana san sharri da kazafi Yaron nan Aminu dukiyarsa ta halas ce." a zabure! yace."Waye ya fada miki haka? kina zaune a gida kike masa sheda duk 'yan kasuwar nan macuta ne mutsiyata kawai." Gwaggo baki ta rike tana kallonsa mamaki fal a zuciyarta.
Khalid ya cigaba da masifa da fadin."Shashashan namiji hotiho kawai kullum yana yawo cikin galla-gallan shadda da hula a saman a kansa amma gidansa hoto ne Allah ya tsinewa wannan auran."!
Gwaggo gumi ya dinga tsatstsafo mata ita kam wannan masifa ta isheta wallahi ta dauka yaron tuntuni ya hakura ashe bai hakura ba....Khalid bai saurara dayi wa Gwaggo rashin kunya ba sai da ubansa ya fito tukkuna ya bar gurin yana huci!! koda Kawu ya tambaye ta abinda yake faruwa kasa fada masa tayi ta dinga Kare Khalid din tana fadin."Aa ni ba wani laifin yayi min ba muna mayar da magana ne." Kawu yace."Amma nake jiyo shi yana daga murya kamar wanda yake magana da sa'arsa."
Murmushi tayi cikin kokarin bagarar da maganar tace."Ibrahim kasan Halin Khalid wani lokacin baya abu cikin kintsi amma ni babu wani abu da yayi min na bacin rai."
Kawu girgiza kansa kawai yayi domin yasan kawai ta fadi maganar ne domin ta kare yaron amma babu shakka akwai abinda yake faruwa. Yace."To Allah ya sawake shi kuma wannan yaro da ya biya miki umara Allah yayi masa albarka ya sake daukaka darajarsa." cikin farin ciki ta amsa da ameeen ya rabbi.
Khalid kuwa haka ya kwana da yunwa tsabar bakin ciki da takaici bai ta'ba tsammanin Gwaggo fuska biyu gare ta ba sai yau ashe duk goyon bayan da take nuna masa na gaibu ne tunda gashi yazo ya tarar tana hira da abokin adawarsa a daki har da bashi abinci.......da wannan takaicin ya kwanta ya kuma tashi dashi, a gurguje yayi shirinsa ya fito da jakar kayansa yana kokarin kulle dakinsa kira ya shigo wayarsa.....Oga Labaran ne ya daga wayar suka gaisa cikin mutumci kafin yace."Gani nan na fito Oga kada ka damu." Daga daya bangaran oga labaran yace."To Alhamdulillahi Allah ya kawoka lafiya " ya amsa da ameeen tare da kashe wayar.
Bakin kicin ya nufa inda mahaifiyarsa take ya tsuguna har kasa suka gaisa tace."Khalid har ka fito kenan." Yana duba agogon dake daure a hannunsa yace "Eh Wallahi Ummana inaso na sauka da wuri ne." Tace."To ka tsaya ka karya kummalo mana." Ya mike da fadin."Umma kiyi hakuri zan samu wani abu a mota nasa a cikina kiyi min fatan alkairi." Ummatu tace "To shikkenan Khalid Allah ya kiyaye hanya ya baku nasara akan abinda kasa a gaba.""
Ya amsa da ameeen Ummatu nagode sosai inaso ki cigaba dayi min irin wannan adduar har karshen numfashina." Tace."Insha Allahu Khalid zan cigaba dayi maka kyawawan addua mutukar ina numfashi a duniya." Khalid ya saki fuskarsa sosai yana mata godiya yaji dadi matuka da suka rabu lafiya ba tare da yayi mata wani abu na bacin rai ba. koda ya fito babban tsakar gidan Mahaifinsa ya samu a tsaye a bakin kofar dakin Gwaggo suna magana, hannu ya mika masa sukayi musabaha da juna Kawu yace."Har ka fito kenan."? Yace."Eh wallahi da wuri nake so na sauka. Yace."To Allah ya tsare sai ka kiyaye da abinda na fada maka Khalid kada kaje kasar waje ka hadu da arna ka watsar da addininka ka kula da sallah da salati da istigifari." Yace."Insha Allahu zan kula." Gwaggo ta fito daga dakin tana kallonsa duk tayi kalar tausayi
Kauda kansa yayi yana jin tausayinta kadan a ransa da kyar yace."Gwaggo ni na tafi.'' Murya na rawa tace."Khalid Allah ya tsare dan Allah ka buga kwallo a hankali kada su karya ka kasan kafuran nan basa kaunar musulunmi da gayya ma zasu jefar da kai ka karye."
Uwale tana kokarin mikewa take fadin."Gaskiyarki Sa'ida Allah dai ya yafe mana amma a zahirin gaskiya abinda Rabi takeyi a gidan nan dole ne a taka mata burki."
Shuru nayi ban tanka ba suka mike tare da daukar butoci domin daura alwala.
Uwale sai da tayi sallar isha'i tukkuna ta tayi mana sallama ta tafi bayan ta sake jadadda min yanda za'ayi amfani da maganin data kar'bo.
Karfe takwas da rabi Yaya Aminu ya kira waya ta yace mani gashinan a waje na fito domin nayi masa jagora cikin gidan.
Na kalleta tana fama da redio a hannunta nace."Gwaggo Yaya Aminu yazo yana so ya shigo ku gaisa." Redion ta ajiye da fadin."To ai babu komai ya shigo mana." Mikewa nayi domin naje na shigo dashi.
Ina kokarin fita Kawu ya shigo zubewa nayi gwiwa a kasa ina gaisheshi cike da kulawa ya amsa yana ta farin ciki yace."Sa'ida ashe anan kika yini yanzu yanzu mijin naki yake sheda min."
Nace."Eh wallahi Kawu tun safe ina nan yace nazo na gaishe ku lokacin kuma da nazo kai ka fita dama inata addua Allah yasa kafin na tafi ka dawo mu gaisa."
Yace."Aikuwa ya kyauta sosai kuma naji dadin ganinku keda mijinki kicin koshin lafiya ina rokon Allah ya dawwamar miki da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan auranki."
A sanyaye na amsa da ameeen ya Allah Kawu." Yace."Kiyi maza kije ki shigo dashi yace yana so ya gaisa da Gwaggo." Nace."To Kawu." Hanya ya bani na wuce shi kuma ya karasa bakin kofar dakin mahaifiyarsa.
Gwaggo cikin girma da mutunci suka gaisa da Yaya Aminu kamar ba itace mai zagin sa da ganin aibun sa ba sai wasa take masa tana masa adduar fatan alkairi. Yaya Aminu da yake mutum ne mai saurin sabo ya saki jikinsa sosai suka dinga hira har ta zuba masa abinci ya zage ciki yana ci harda cire hula ita kuwa sai tsokanarsa take wai kada dai garin santi ya manta hularsa....Cikin wannan halin Khalid ya daga labulan dakin, ganin mu cikin raha da annushuwa yasa ya kirne fuskarsa kamar baya so ya miqa masa hannu da fadin"Barka da dare Alhaji." Yaya Aminu da sauri ya amsa da "Barka dai abokina ya kake ya al'amura."
Babu wani sakewa ya amsa da "Alhamdulillahi." Labulan dakin ya saki zai bar gurin Gwaggo da sauri tace."Jarumi ka shigo kaci abinci mana." Yana kokarin barin gurin yace."Sai an jima yanzu inada uziri." Gwaggo kasa'ke tayi tana tunani yanayin yanda yayi maganar a cunkushe ya nuna mata lallai akwai abinda yake damunsa.
Yaya Aminu sai da ya cika cikinsa tsaf da abinci Gwaggo yasha ruwa babu wani kyankyami ya goge bakinsa da hankici ya kalleta a tsanake yace."Uwargida ran gida nagode sosai yau naci abincin tsofaffi wanda na jima banci irinsa ba.
Gwaggo na dariya tace."To masha Allah ai haka nake so naji kana kira na da uwargida domin dama so nake na kar'be gidan gabadaya.'"
Dariya yayi ya sunkuyar da kansa minti biyu a tsakani ya kalleta da fadin."Gwaggo insha Allahu sha biyar ga azimi zaki je umara k'asa mai tsarki inaso kiyi min addua akan wasu bukatuna."
Gwaggo ta kalleshi cikin farin ciki da kuma tausayi tace."Aminu Allah ya yaye maka damuwarka nagode sosai daka za'be ni a matsayin me maka addua nagode da wannan karamcin.
Na kalleshi a sanyaye nace."Yaya Aminu Gwaggo ta gode sosai Allah ya saka da alkairi." Ya amsa da ameeen ai babu komai Sa'ida insha Allahu tare dani dake zamuje mu dawo." Nace."To Allah ya yarda Allah kuma ya amsa adduarmu.
Yaya Aminu mikewa yayi bayan ya duba agogon hannunsa ya kalleta da fadin."Gwaggo mu zamu tafi sai kinji kira ko."? Ta mike da sauri tana fadin.''To shikkenan Allah ya kaimu lokacin nagode.
Mayafi na na gyara na fito na same su a tsakar gida suna magana har Ummatu ta fito daga gurinta ya dauko kudi masu yawa ya bawa kowacce Ummatu bakinta ya kasa rufuwa sai juya kudin take a hannunta tana zabga godiya, Khalid kuwa na bakin rijiya a zaune yana gyaran fuskarsa uffan bece ba sai da muka zo fita Yaya Aminu ya tsaya yana masa magana Da kyar yace."A sauka lafiya." Tsabar bacin ran abinda yake yasa na watsa masa harara tare da jan tsaki nabi bayan mijina da sauri Gwaggo har soro ta rako mu tana mana fatan alkairi da godiyar abin alkairi.
Koda ta koma cikin gidan Khalid rufe ta yayi da masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, Gwaggo dai tasan akan abinda yasa yake bala'i da ta gaji da bashi hakuri sai kawai ta shiga daki ta barshi a gurin.........Bayan ya gama gyaran fuskar zuwa yayi ya tsaya bakin kofar dakin da fadin."Sabida kawai ya biya miki umara sai wani rawar jiki kike masa harda bashi abinci da kawo shi daki har nawa umarar take to ni insha Allahu aikin hajji zan kai ki wata shekarar wannan shashashan mutumin kudinsa na banza ne tunda ba'a hanyar halak ya samesu ba.
Gwaggo tace."Aa Khalid bana san sharri da kazafi Yaron nan Aminu dukiyarsa ta halas ce." a zabure! yace."Waye ya fada miki haka? kina zaune a gida kike masa sheda duk 'yan kasuwar nan macuta ne mutsiyata kawai." Gwaggo baki ta rike tana kallonsa mamaki fal a zuciyarta.
Khalid ya cigaba da masifa da fadin."Shashashan namiji hotiho kawai kullum yana yawo cikin galla-gallan shadda da hula a saman a kansa amma gidansa hoto ne Allah ya tsinewa wannan auran."!
Gwaggo gumi ya dinga tsatstsafo mata ita kam wannan masifa ta isheta wallahi ta dauka yaron tuntuni ya hakura ashe bai hakura ba....Khalid bai saurara dayi wa Gwaggo rashin kunya ba sai da ubansa ya fito tukkuna ya bar gurin yana huci!! koda Kawu ya tambaye ta abinda yake faruwa kasa fada masa tayi ta dinga Kare Khalid din tana fadin."Aa ni ba wani laifin yayi min ba muna mayar da magana ne." Kawu yace."Amma nake jiyo shi yana daga murya kamar wanda yake magana da sa'arsa."
Murmushi tayi cikin kokarin bagarar da maganar tace."Ibrahim kasan Halin Khalid wani lokacin baya abu cikin kintsi amma ni babu wani abu da yayi min na bacin rai."
Kawu girgiza kansa kawai yayi domin yasan kawai ta fadi maganar ne domin ta kare yaron amma babu shakka akwai abinda yake faruwa. Yace."To Allah ya sawake shi kuma wannan yaro da ya biya miki umara Allah yayi masa albarka ya sake daukaka darajarsa." cikin farin ciki ta amsa da ameeen ya rabbi.
Khalid kuwa haka ya kwana da yunwa tsabar bakin ciki da takaici bai ta'ba tsammanin Gwaggo fuska biyu gare ta ba sai yau ashe duk goyon bayan da take nuna masa na gaibu ne tunda gashi yazo ya tarar tana hira da abokin adawarsa a daki har da bashi abinci.......da wannan takaicin ya kwanta ya kuma tashi dashi, a gurguje yayi shirinsa ya fito da jakar kayansa yana kokarin kulle dakinsa kira ya shigo wayarsa.....Oga Labaran ne ya daga wayar suka gaisa cikin mutumci kafin yace."Gani nan na fito Oga kada ka damu." Daga daya bangaran oga labaran yace."To Alhamdulillahi Allah ya kawoka lafiya " ya amsa da ameeen tare da kashe wayar.
Bakin kicin ya nufa inda mahaifiyarsa take ya tsuguna har kasa suka gaisa tace."Khalid har ka fito kenan." Yana duba agogon dake daure a hannunsa yace "Eh Wallahi Ummana inaso na sauka da wuri ne." Tace."To ka tsaya ka karya kummalo mana." Ya mike da fadin."Umma kiyi hakuri zan samu wani abu a mota nasa a cikina kiyi min fatan alkairi." Ummatu tace "To shikkenan Khalid Allah ya kiyaye hanya ya baku nasara akan abinda kasa a gaba.""
Ya amsa da ameeen Ummatu nagode sosai inaso ki cigaba dayi min irin wannan adduar har karshen numfashina." Tace."Insha Allahu Khalid zan cigaba dayi maka kyawawan addua mutukar ina numfashi a duniya." Khalid ya saki fuskarsa sosai yana mata godiya yaji dadi matuka da suka rabu lafiya ba tare da yayi mata wani abu na bacin rai ba. koda ya fito babban tsakar gidan Mahaifinsa ya samu a tsaye a bakin kofar dakin Gwaggo suna magana, hannu ya mika masa sukayi musabaha da juna Kawu yace."Har ka fito kenan."? Yace."Eh wallahi da wuri nake so na sauka. Yace."To Allah ya tsare sai ka kiyaye da abinda na fada maka Khalid kada kaje kasar waje ka hadu da arna ka watsar da addininka ka kula da sallah da salati da istigifari." Yace."Insha Allahu zan kula." Gwaggo ta fito daga dakin tana kallonsa duk tayi kalar tausayi
Kauda kansa yayi yana jin tausayinta kadan a ransa da kyar yace."Gwaggo ni na tafi.'' Murya na rawa tace."Khalid Allah ya tsare dan Allah ka buga kwallo a hankali kada su karya ka kasan kafuran nan basa kaunar musulunmi da gayya ma zasu jefar da kai ka karye."