Sashe 49
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nace."Gwaggo to me yasa kin san gaskiya kike takewa me yasa bakya ganin Laifin Khalid kuma me yasa kike fifitashi akaina."
Cikin nutsuwa tace."Sa'ida kada ki fassarani da wata manufa mara kyau ni dake da Khalid dik daya kuke a gurina babu wanda yafi wani hakika kuma naji bakin ciki da takaicin abinda yayi saboda haka an jima idan ya kira ni a wayar daya siya min zan nuna masa 'bacin raina."
Shuru nayi ina sha'kar bakin ciki! ta girgiza kanta tana jimanta al'amarin tace."Wai saki uku a gaskiya wannan mutumin bashi da hankali ko kad'an wallahi naji ciwon abinda yayi."
Nace."Gwaggo kiyi min addua kawai Allah yasa haka shi yafi alkairi Allah ya za'ba min miji nagari."
A sanyaye ta amsa da ameeen ya rabbi. dakin ya sake daukar shuru na 'yan mintina kafin nace."Gwaggo kin tuna asibitin da kika rakani a washe garin ranar da Khalid yayi min fyad'e."?
Kallonta tayi a sanyaye tace."Sa'ida bana so naji kina wannan maganar wallahi babu dadin ji.'' Cike da takaici nace."Gwaggo har duniya ta nad'e ba zan daina maganar nan ba kuma ba zan fasa neman sakayya gurin Ubangiji ba."
Babu walwala a tare da ita tace."To naji ya isa haka magana dai tuntuni ta wuce tayar da ita bashi da amfani yanzu sai ki fuskanci abinda yake gabanki.
Nace."Magana ai tuntuni na barwa Allah yanzu ma dalili tayi shiyasa na fada miki abinda yake zuciyata.
Shuru tayi ba tai magana ba, nace."Wannan likitar data duba ni ashe kawar aunty Murja ce."
Kallona tayi da mamaki a tare da ita, na cigaba da cewa "Itace duk ta warware masa komai shi kuma ya fusata ya yanke min wannan hukuncin kafin na fito daga gidan ba kiji irin zagi da cin mutuncin da Yayi min ba."
Hawaye ta goge tace."Ki rabu dashi daga shi har ita likitan Allah zai saka miki kuma duk wanda ya tona asirin wani shima sai Allah ya tona nasa yanzu ni tsorana Allah da Annabi kada maganar ta fita jama'ar gari su dinga yi mana wani irin kallo." Tana kuka take maganar.
Gabadaya naji zuciyata ta karye zafafan hawaye suka fara zubo min nace."Gwaggo insha Allahu hakan ba zata kasance ba idan kuwa maganar ta fita to zan tattara kayana na gudu gurin mahaifiyata."
Kuka takeyi sosai tana kallona had'e da girgiza kanta, Kaina na sunkuyar kasa ina shakar hanci tare da jin tsananin tausayinta a cikin raina.
"Gwaggo ba'kuwa kikayi ne na fito domin d'ibar ruwa naji magana a dakin ki.'' Maganar Ummatu ce ta dawo damu nutsuwarmu tana tsaye a bakin kofar dakin hannunta ri'ke da labule.
Ido muka had'a tace."Au ashe Sa'ida ce." Nace."Eh Ummatu Ina wuni ya gida."?
Ta amsa a sake tana tambayata maigidana....Gwaggo tace."Rabi wane maigida kike tambaya bayan ya sake ta.
Da sauri tace."Gwaggo ban gane maganarki ba." Tace."Ina nufin Alhaji Nura ya saki Sa"ida saki uku."
Da sauru tace."Subahannallahi Sa'ida garin ya haka ta faru me kikayi masa."?
Gwaggo a d'an hasale tace."Rabi har kin manta ashe."? Kallonta tayi jikinta duk yayi sanyi Gwaggo ta cigaba da cewa"Ko wane namiji dai yana kulafucin wannan abu (budurci) to da Alhaji Nura ya tabbatar da cewa Sa'ida bata dashi shine ya yanke shawarar sakin ta."
Ummatu shuru tayi jikinta duk yayi la'asar Tace."To amma me yasa tun farko beyi magana ba sai da tayi wattani a gidansa Gwaggo anya wannan ce matsalar."
Girgiza kanta tayi tace."Rabi wannan ce matsalar ko kinqi ki kin so sai matsala ta biyu ashe Khalid duk jan kunnansa da nayi akan kada yaje gidan mutumin nan sai da yaje saboda tsabar wuce gona da irin nasa har 'kuryar daki ya shiga.
Ummatu gabanta na fad'uwa tace."Gwaggo a yaushe Khalid din yaje gidan bayan yau satin sa uku da tafiya.
Tace."A ranar da zai tafi yaje da safe kuma Alhaji Nuran ya ritsa shi a dakin baccin sa Rabi wace irin masifa yaron nan yake so ya janyo mana
Ummatu taji 'kwalla ta cika idonta Itakam ta rasa wace irin masifa ce wannan wane irin kwadayi da kulafuci yaron keyi akan wacce bata dace dashi ba, aranar da Gwaggo take masa fada akan kada ya kuskura yace zaije gidan tana jinsu har ta shiga dakin tasa baki tayi masa gargadi sosai ashe jinsu kawai yake da kunne ya mayar dasu shashashai sai da yaje ya dauko musu magana.
Kai ta kad'a ta bar gurin ba tare da tace komai ba, Gwaggo tace."Duk kauce-kaucen da za kiyi dole sunan Khalid ya fito a cikin mutuwar auran Sa'ida."
Koda kawu ya dawo ya sameni a gidan bai kawo komai ba a cikin ransa muka gaisa a nutse ya shiga gurin sa domin cin abinci da hutawa.
Gwaggo bayan ta tabbatar da cewa yaci abinci ya huta sai ta fito tsakar gida tana 'kwala masa kira, da sauri ya bude kofar gurun nasu ya fito yana fadin"Gwaggo lafiya dai ko? Ina S'ida ina fatan ta tafi gidanta.
Tace."Sa'ida tana nan ai kuma ta dawo kenan sabida saki ukun da mijin nata ya rattaba mata."
Kawu wani irin gumi! ne ya jika masa riga baki na rawa yace."Gwaggo me yasa mutumin nan zaiyi mana haka? me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata irin wannan hukuncin
Kai tsaye tace "Munafurtar sa akayi Ibrahim me yasa tun farko baka sameshi ka fada masa abinda ya faru ba.
Yace." Gwaggo ya za'ayi na tonawa yarinyar nan asiri? wane namiji ne kike gani zai ji wannan al'amari ya yarda da auran."
Tace."To ai *"GA IRINTA NAN!* An yanka ta tashi domin dai likitar data duba ta a washe garin ranan da al'amarin ya faru To itace ta tabbatar masa da gaskiyar lamarin bayan haka kuma ashe Khalid a ranar da zai tafi sai da yaje gidan saboda kuma wace gona da iri irin nasa har uwar daki ya b ita a takaice ma dai sai da maigidan ya shiga ya same shi Ibrahim ka fad'a min shin Khalid me yake nufi da aikata hakan."?
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*60&61*
Kawu Iro shuru yayi a gurin tamkar ruwa ya cinyeshi gabadaya al'amarin ya daure masa kai ya rasa ma bakin magana shi kam ya rasa wane irin yaro Allah ya bashi. Gwaggo ta kalleshi da fadin"Ibrahim kayi shuru ka kasa magana." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace."Gwaggo al'amarin ne ya daure min kai shiyasa kikaji nayi shuru na kasa cewa komai wato Khalid yayi hakane domin ya kashe mata aure ta fito daga gidanta shi ya aureta hakane ko ba haka bane." ? Gwaggo tace."Ato nima abinda nake zargi kenan.....Ummatu ta karaso gurun da fad'in "Dan Allah Gwaggo kuyi wa al'amarin nan kyakykyawar fahimta kada ku zargeshi da mummunar manufa tunda kun san dai maganar auransa da Jamila tayi nisa to mai zai sanya ya kashe auran Sa'ida wannan magana tuntuni ta mutu domin ya hakura ya kar'bi Jamila a matsayin matar auransa.
Kawu yace." Rabi ke kika haifi Khalid amma har yanzu baki san halinsa ba yaron mugun Hatsabibi ne." Cikin bacin rai yayi maganar....Gwaggo tace."Kada kayi masa baki Ibrahim ka daina kiransa da wannan suna addua za'ayi masa.
Yace."Gwaggo idan wannan ce manufar Khalid akan Sa'ida to ni mutukar ni na haifeshi ba zan lamunce masa auranta ba Allah zai kawo mata miji daidai da ita ta aura."
Jin abinda ya fada Yasa Ummatu jin dadi a zuciyarta gurin ta bari tana godewa Allah. Gwaggo jiki a sanyaye tace." Allah ya kyauta ya za'ba mana abinda yafi alkairi." amsawa yayi da amin ya kama hanyar fita yana kokarin fito da wayarsa.
Kofar gida ya zauna yana goge gumi hankalinsa a tashe ya nemo number wayar Alhaji Shamsu ya kirashi domin ya sheda masa halin da ake ciki.
Alhaji Shamsu hankalinsa ya tashi jin irin bayanin da Kawu Iron ke masa yace."Ibrahim na jima ban ji 'bacin rai irin na yau ba kuma banta'ba tsammanin Alhaji Nura zaiyi mana wannan wulakancin ba shin me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata saki uku."?
Kawu ya goge gumi yana dawurwura hakika yana jin nauyi da kunyar fada masa dalilin da ya janyo sakin....Alhaji Shamsu yace."Ibrahim ka kwantar da hankalinka Alhaji Nura bamu ya tozarta ba kansa ya tozarta kuma abinda kayi wa d'an wani kaima sai anyi wa naka.
Kawu yace."Kwarai da gaske Alhaji maganarka haka take." Yace."Yanzu yanzu zan kirashi a waya dole ya fad'a min dalilin da yasa ya saki yarinyar nan domin hankalina gabadaya ya kasa Kwanciya inata tunani babu shakka ruwa baya tsami banza.
Jiki a mace Kawu yace."To shikkenan Alhaji duk yanda kukayi dashi sai ka kira wayata ka sanar dani."
Alhaji Shamsu yace."Insha Allahu zan kaji daga zarar mun tattauna magana dashi."
Sallama sukayi kowanne ya kashe wayarsa.
Washe gari da safe Alhaji Shamsu ya zaunar da matarsa kafin ya fada mata abinda yake faruwa sai da yayi mata nasiha mai ratsa jiki sannan ya sheda mata abunda ya faru da 'yarta.
UmmuHabiba fashewa tayi da kuka tana girgiza kanta take fadin."Innalillahi wa'ina ilaihi raji'una Alhaji wannan wane irin wulakanci ne? saki uku a lokaci guda akan wane dalili ashe dama mutumin nan auran sha'awa yayi."
Alhaji Shamsu ganin hankalinta ya tashi tana kuka ya shiga rarrashinta yana bata baki har sai da tayi shuru tana goge fuskarta yace." Dama yanzu nake tunanin kiransa a waya naji bayani daga bakinsa domin tabbas akwai dalili mai karfi da ya janyo hakan."
Tace."Eh ai gwara ka kirasa a wayar yayi mana bayani muji abinda ya janyo wannan cin mutuncin.
Wayarsa ya dauka ya nemo number Alhaji Nuran ya shiga gurin kira.
Yana kokarin fita kasuwa kiran wayar ya sameshi ya fito da ita daga aljihu yana dubawa, ganin number Alhaji Shamsu yasa yaja tsaki! aunty Murja ta kalleshi da fadin"Lafiya dai.''? Yace.''Mahaifin yarinyar nan ne Sa'ida." shuru tayi bata ce uffan ba har wayar ta katse wani kiran ya sake shigowa.
Tace."Kayi hakuri ka dauka mana kaji abinda yake tafe dashi a yanzu dai ai babu wata magana tunda saki uku kayi mata."
Cikin nutsuwa tace."Sa'ida kada ki fassarani da wata manufa mara kyau ni dake da Khalid dik daya kuke a gurina babu wanda yafi wani hakika kuma naji bakin ciki da takaicin abinda yayi saboda haka an jima idan ya kira ni a wayar daya siya min zan nuna masa 'bacin raina."
Shuru nayi ina sha'kar bakin ciki! ta girgiza kanta tana jimanta al'amarin tace."Wai saki uku a gaskiya wannan mutumin bashi da hankali ko kad'an wallahi naji ciwon abinda yayi."
Nace."Gwaggo kiyi min addua kawai Allah yasa haka shi yafi alkairi Allah ya za'ba min miji nagari."
A sanyaye ta amsa da ameeen ya rabbi. dakin ya sake daukar shuru na 'yan mintina kafin nace."Gwaggo kin tuna asibitin da kika rakani a washe garin ranar da Khalid yayi min fyad'e."?
Kallonta tayi a sanyaye tace."Sa'ida bana so naji kina wannan maganar wallahi babu dadin ji.'' Cike da takaici nace."Gwaggo har duniya ta nad'e ba zan daina maganar nan ba kuma ba zan fasa neman sakayya gurin Ubangiji ba."
Babu walwala a tare da ita tace."To naji ya isa haka magana dai tuntuni ta wuce tayar da ita bashi da amfani yanzu sai ki fuskanci abinda yake gabanki.
Nace."Magana ai tuntuni na barwa Allah yanzu ma dalili tayi shiyasa na fada miki abinda yake zuciyata.
Shuru tayi ba tai magana ba, nace."Wannan likitar data duba ni ashe kawar aunty Murja ce."
Kallona tayi da mamaki a tare da ita, na cigaba da cewa "Itace duk ta warware masa komai shi kuma ya fusata ya yanke min wannan hukuncin kafin na fito daga gidan ba kiji irin zagi da cin mutuncin da Yayi min ba."
Hawaye ta goge tace."Ki rabu dashi daga shi har ita likitan Allah zai saka miki kuma duk wanda ya tona asirin wani shima sai Allah ya tona nasa yanzu ni tsorana Allah da Annabi kada maganar ta fita jama'ar gari su dinga yi mana wani irin kallo." Tana kuka take maganar.
Gabadaya naji zuciyata ta karye zafafan hawaye suka fara zubo min nace."Gwaggo insha Allahu hakan ba zata kasance ba idan kuwa maganar ta fita to zan tattara kayana na gudu gurin mahaifiyata."
Kuka takeyi sosai tana kallona had'e da girgiza kanta, Kaina na sunkuyar kasa ina shakar hanci tare da jin tsananin tausayinta a cikin raina.
"Gwaggo ba'kuwa kikayi ne na fito domin d'ibar ruwa naji magana a dakin ki.'' Maganar Ummatu ce ta dawo damu nutsuwarmu tana tsaye a bakin kofar dakin hannunta ri'ke da labule.
Ido muka had'a tace."Au ashe Sa'ida ce." Nace."Eh Ummatu Ina wuni ya gida."?
Ta amsa a sake tana tambayata maigidana....Gwaggo tace."Rabi wane maigida kike tambaya bayan ya sake ta.
Da sauri tace."Gwaggo ban gane maganarki ba." Tace."Ina nufin Alhaji Nura ya saki Sa"ida saki uku."
Da sauru tace."Subahannallahi Sa'ida garin ya haka ta faru me kikayi masa."?
Gwaggo a d'an hasale tace."Rabi har kin manta ashe."? Kallonta tayi jikinta duk yayi sanyi Gwaggo ta cigaba da cewa"Ko wane namiji dai yana kulafucin wannan abu (budurci) to da Alhaji Nura ya tabbatar da cewa Sa'ida bata dashi shine ya yanke shawarar sakin ta."
Ummatu shuru tayi jikinta duk yayi la'asar Tace."To amma me yasa tun farko beyi magana ba sai da tayi wattani a gidansa Gwaggo anya wannan ce matsalar."
Girgiza kanta tayi tace."Rabi wannan ce matsalar ko kinqi ki kin so sai matsala ta biyu ashe Khalid duk jan kunnansa da nayi akan kada yaje gidan mutumin nan sai da yaje saboda tsabar wuce gona da irin nasa har 'kuryar daki ya shiga.
Ummatu gabanta na fad'uwa tace."Gwaggo a yaushe Khalid din yaje gidan bayan yau satin sa uku da tafiya.
Tace."A ranar da zai tafi yaje da safe kuma Alhaji Nuran ya ritsa shi a dakin baccin sa Rabi wace irin masifa yaron nan yake so ya janyo mana
Ummatu taji 'kwalla ta cika idonta Itakam ta rasa wace irin masifa ce wannan wane irin kwadayi da kulafuci yaron keyi akan wacce bata dace dashi ba, aranar da Gwaggo take masa fada akan kada ya kuskura yace zaije gidan tana jinsu har ta shiga dakin tasa baki tayi masa gargadi sosai ashe jinsu kawai yake da kunne ya mayar dasu shashashai sai da yaje ya dauko musu magana.
Kai ta kad'a ta bar gurin ba tare da tace komai ba, Gwaggo tace."Duk kauce-kaucen da za kiyi dole sunan Khalid ya fito a cikin mutuwar auran Sa'ida."
Koda kawu ya dawo ya sameni a gidan bai kawo komai ba a cikin ransa muka gaisa a nutse ya shiga gurin sa domin cin abinci da hutawa.
Gwaggo bayan ta tabbatar da cewa yaci abinci ya huta sai ta fito tsakar gida tana 'kwala masa kira, da sauri ya bude kofar gurun nasu ya fito yana fadin"Gwaggo lafiya dai ko? Ina S'ida ina fatan ta tafi gidanta.
Tace."Sa'ida tana nan ai kuma ta dawo kenan sabida saki ukun da mijin nata ya rattaba mata."
Kawu wani irin gumi! ne ya jika masa riga baki na rawa yace."Gwaggo me yasa mutumin nan zaiyi mana haka? me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata irin wannan hukuncin
Kai tsaye tace "Munafurtar sa akayi Ibrahim me yasa tun farko baka sameshi ka fada masa abinda ya faru ba.
Yace." Gwaggo ya za'ayi na tonawa yarinyar nan asiri? wane namiji ne kike gani zai ji wannan al'amari ya yarda da auran."
Tace."To ai *"GA IRINTA NAN!* An yanka ta tashi domin dai likitar data duba ta a washe garin ranan da al'amarin ya faru To itace ta tabbatar masa da gaskiyar lamarin bayan haka kuma ashe Khalid a ranar da zai tafi sai da yaje gidan saboda kuma wace gona da iri irin nasa har uwar daki ya b ita a takaice ma dai sai da maigidan ya shiga ya same shi Ibrahim ka fad'a min shin Khalid me yake nufi da aikata hakan."?
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*60&61*
Kawu Iro shuru yayi a gurin tamkar ruwa ya cinyeshi gabadaya al'amarin ya daure masa kai ya rasa ma bakin magana shi kam ya rasa wane irin yaro Allah ya bashi. Gwaggo ta kalleshi da fadin"Ibrahim kayi shuru ka kasa magana." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace."Gwaggo al'amarin ne ya daure min kai shiyasa kikaji nayi shuru na kasa cewa komai wato Khalid yayi hakane domin ya kashe mata aure ta fito daga gidanta shi ya aureta hakane ko ba haka bane." ? Gwaggo tace."Ato nima abinda nake zargi kenan.....Ummatu ta karaso gurun da fad'in "Dan Allah Gwaggo kuyi wa al'amarin nan kyakykyawar fahimta kada ku zargeshi da mummunar manufa tunda kun san dai maganar auransa da Jamila tayi nisa to mai zai sanya ya kashe auran Sa'ida wannan magana tuntuni ta mutu domin ya hakura ya kar'bi Jamila a matsayin matar auransa.
Kawu yace." Rabi ke kika haifi Khalid amma har yanzu baki san halinsa ba yaron mugun Hatsabibi ne." Cikin bacin rai yayi maganar....Gwaggo tace."Kada kayi masa baki Ibrahim ka daina kiransa da wannan suna addua za'ayi masa.
Yace."Gwaggo idan wannan ce manufar Khalid akan Sa'ida to ni mutukar ni na haifeshi ba zan lamunce masa auranta ba Allah zai kawo mata miji daidai da ita ta aura."
Jin abinda ya fada Yasa Ummatu jin dadi a zuciyarta gurin ta bari tana godewa Allah. Gwaggo jiki a sanyaye tace." Allah ya kyauta ya za'ba mana abinda yafi alkairi." amsawa yayi da amin ya kama hanyar fita yana kokarin fito da wayarsa.
Kofar gida ya zauna yana goge gumi hankalinsa a tashe ya nemo number wayar Alhaji Shamsu ya kirashi domin ya sheda masa halin da ake ciki.
Alhaji Shamsu hankalinsa ya tashi jin irin bayanin da Kawu Iron ke masa yace."Ibrahim na jima ban ji 'bacin rai irin na yau ba kuma banta'ba tsammanin Alhaji Nura zaiyi mana wannan wulakancin ba shin me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata saki uku."?
Kawu ya goge gumi yana dawurwura hakika yana jin nauyi da kunyar fada masa dalilin da ya janyo sakin....Alhaji Shamsu yace."Ibrahim ka kwantar da hankalinka Alhaji Nura bamu ya tozarta ba kansa ya tozarta kuma abinda kayi wa d'an wani kaima sai anyi wa naka.
Kawu yace."Kwarai da gaske Alhaji maganarka haka take." Yace."Yanzu yanzu zan kirashi a waya dole ya fad'a min dalilin da yasa ya saki yarinyar nan domin hankalina gabadaya ya kasa Kwanciya inata tunani babu shakka ruwa baya tsami banza.
Jiki a mace Kawu yace."To shikkenan Alhaji duk yanda kukayi dashi sai ka kira wayata ka sanar dani."
Alhaji Shamsu yace."Insha Allahu zan kaji daga zarar mun tattauna magana dashi."
Sallama sukayi kowanne ya kashe wayarsa.
Washe gari da safe Alhaji Shamsu ya zaunar da matarsa kafin ya fada mata abinda yake faruwa sai da yayi mata nasiha mai ratsa jiki sannan ya sheda mata abunda ya faru da 'yarta.
UmmuHabiba fashewa tayi da kuka tana girgiza kanta take fadin."Innalillahi wa'ina ilaihi raji'una Alhaji wannan wane irin wulakanci ne? saki uku a lokaci guda akan wane dalili ashe dama mutumin nan auran sha'awa yayi."
Alhaji Shamsu ganin hankalinta ya tashi tana kuka ya shiga rarrashinta yana bata baki har sai da tayi shuru tana goge fuskarta yace." Dama yanzu nake tunanin kiransa a waya naji bayani daga bakinsa domin tabbas akwai dalili mai karfi da ya janyo hakan."
Tace."Eh ai gwara ka kirasa a wayar yayi mana bayani muji abinda ya janyo wannan cin mutuncin.
Wayarsa ya dauka ya nemo number Alhaji Nuran ya shiga gurin kira.
Yana kokarin fita kasuwa kiran wayar ya sameshi ya fito da ita daga aljihu yana dubawa, ganin number Alhaji Shamsu yasa yaja tsaki! aunty Murja ta kalleshi da fadin"Lafiya dai.''? Yace.''Mahaifin yarinyar nan ne Sa'ida." shuru tayi bata ce uffan ba har wayar ta katse wani kiran ya sake shigowa.
Tace."Kayi hakuri ka dauka mana kaji abinda yake tafe dashi a yanzu dai ai babu wata magana tunda saki uku kayi mata."