Sashe 48
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nace."Hauwwa nima na fara zargin haka wallahi dan gaskiya idan ya kasance Aunty Murja tana da karfin sha'awa kuma tana da rauni to zata iya jefa kanta cikin matsala amma ni bana fatan nayi wannan harkar Hauwwa zan duba shawarar ki dan gaskiya ina masifar 'kwaruwa a zamantakewa ta da mutumin nan."
Tace."To shikkenan Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi." na amsa da ameen ya Allah 'kawata nagode kwarai da gaske."
Haka rayuwar ta cigaba da tafiya yau da dad'i goge babu ta 'bangaran maigidan babu dad'i bangaran Aunty Murjar ma haka domin kwata kwata yanxu ni da ita bama shiri tun ranar da ta fahimci cewa na gane abinda takeyi ta sanja taku a gidan bata shiga sabgata sai da ni sa'i da lokaci inayi mata magana idan tayi ra'ayi ta amsa idan ba tayi ba ta share ni...........
Ranar Wata laraba tayi bakuwa da yake a falo suka zauna ina jin hayaniyarsu a dakina a nutse na bude kofa na fito. ganin matar dake zaune a kusa da ita yasa gabana ya yanke ya fadi da sauri nayi niyyar komawa daki sai kuma na fasa domin nasan sun riga sun gan ni! A dake na k'arasa falon na nemu kujera na zauna da fadin."Aunty Murja bakuwa kikayi ne."? Yau da mutuminci ta amsa min da "Eh wallahi dama yanzu take cewa zata tafi kuma baku gaisa ba.
Nace." Allah sarki ina kallonta nace."Ina wuni ya gida ya yara."? Ta amsa tana min wani irin kallo kaina na sunkuyar kasa gabana na faduwa ina addua a zuciyata akan Allah yasa bata gane ni ba.
Tace."Ni kam kamar na san wannan fuskar taki." na kalleta tare da kokarin kauda fargabata nace."Allah ko."? Tace."Kwarai kuwa kamar kece watanni takwas da suka wuce kikaje asibiti keda wata tsohuwa domun a duba miki virginal d'inki."
Nace."Anya kuwa bani bace." 'Yar dariya tayi tace."Kece mana ko ba sunanki Sa'ida ba."? Nace."Sunana Sa'ida mana." Tace."Sannan kuma kice min bake bace." shuru nayi mata domin idan nace zanyi magana zan iya fashewa da kuka shikkenan asirina ya tonu.
Aunty Murja tace." Maryam naji kina maganar wata takwas da suka wuce kuma yanzu auransu da Abban Yusura wata biyar kenan.
Tace."Nima dai abinda ya bani mamaki kenan lokacin taje akan a dubata ko ta qaru a d'inke ta lokacin dana duba sai na fahimci cewar kamar tayi gardama ne a lokacin da za'a kar'bi budurcinta sai na rubuta mata magunguna. har nake tambayarta ina mijinta a lokacin take cewa dani yayi tafiya shine yace tazo asibiti a dubata duk ina da sheda a rubuce."
Aunty Murja ta dinga yi min wani irin kallo ni kuma sai wani irin gumi nake zabgawa tamkar wacce tayi gudun famfalaki.!
Mi'kewa nayi jikina a bala'in mace na bude dakina na shiga na fada a saman gado kuka na dinga rafsawa ina kiran sunan Allah.
Aunty Murja wayarta ta dauka da fad'in "Dama neman hanyar da zan hukunta yarinyar nan nake domin nima data rufa min asiri zan rufa mata dan haka yanzu zan kira Abban Yusura a waya yazo kiyi masa bayani da bakin ki."
Dr Maryam tace."Aa Murja kada kiyi haka dan Allah wallahi ni ban fadi wannan maganar da wata manufa ba ki rufa mata asiri ta zauna dakinta."
Murmushin takaici tayi tace."Maryam wallahi ba zan kyale yarinyar nan ba domin itace tayi sanadiyar da Alhaji ya hana Aziza zuwa gidan nan sannan kuma tayi sanadin zuwana gidanmu nayi kwanaki tsayin shekarun aurena da mijina hakan bata ta'ba faruwa ba sai da ta shigo gidan sannan kuma kice na kyaleta ni dai kawai idan yazo kiyi masa cikakken bayanin da zai gamsu nayi miki alkawarin kyauta ta mussaman."
Dr Maryam tace."Ai shikkenan tunda ta kasa rufa miki asiri kema sai ki bankad'a nata." tace."Ashe kin fahimce ni.
Aunty Murja ta dauki waya ta kira mijinta tace dashi maza maza yazo gida akwai abinda yake faruwa. jin haka Alhaji Nura ya shigo motarsa ya kamo hanyar gida.
Wani irin tashin hankali ya shiga a lokacin da Dr Maryam ta gama warware masa 'boyayyan sirrin Sa'ida dake lullu'be! ya cire hularsa ya ajiye a hannun kujera yasa hannu ya sharce gumin goshinsa ido jajawur ya kallesu yace."A ranar dana kusanci yarinyar nan sai da na gane ba budurwa bace amma sabida ta iya tsari da 'karya ta kawo min wasu hojjojinta na banza to sabida haka tunda yanzu na gane gaskiya lamari zan dauki mataki a kanta domin ni ba zan lamunci zama da macen da zata ha'ince ni ba."
Yana gama maganarsa ya mike da saurin gaske ya kama hanyar dakinta, ido suka bishi dashi har ya bude dakin ya shiga.
Maganarsa naji a saman a kaina, a furgice na mike zaune ina kallonsa tunda na ganshi a burkice nasan ya samu labarin abinda yake da akwai.
Yana huci! yace." Sa'ida an yanka ta tashi yau Allah ya tona asirinki Dr Maryam ta bud'a min dukkanin sirrukan ki saboda haka tunda ke kin kasance ma ha'inciya macuciya kije na sake ki saki uku! sai kiji ki auri yaron da yake bibiyarki har gidan auranki wanda dama shi nake zargin ya lalataki kafin aure na dake."!
Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! kawai nake nanatawa a cikin raina yayin da nake jin wani irin mugun ciwon kai da mugun jiri d'akin sai juyawa yake dani a takaice dai ban san sanda ya gama cin mutuncinsa ya fita daga dakin ba.
*708 465 3262: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*58&59*
Na jima ina nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahiri raji'un a fili da zucci kafin naji wani k'arfin gwiwa gami da danga a tare dani......mikewa nayi jiki a mace na bude wardrobe na had'a kayana cikin akwati tsaf sai da na kwashe kayan sanyawata da duk abinda nasan ina bukata nasa a akwatin kana na rufe ta da kyar ina tunanin wanda zai dau'kar min.
Hijabi na nasa na d'aga akwatin tare da janyo hannunta da yake mai tayoyi ce sai kawai naja ta na bude dakin na fito kaina a kasa dan ko kadan bana kaunar na hada idona dasu....maganarsa naji a kunnena yana fad'in "Tsaya ki tafi da sakamonki cutar da kikayi min kuma na barki da Allah."
Tsayawa nayi ba tare dana juya ba zuciyata in banda tafarfasa babu abinda take
Daf dani ya tsaya hannunsa rike da takardar sakin nawa...."Kar'bi ki fice min daga gida bana bukatar sake ganinki shiyasa nayi miki saki uku domin hukuncin daya cancanta dake kenan "
Hawayen dake kokarin kwace min na danne hannuna na rawa na kar'bi takardar da fad'in "Nagode ina rokon Allah yasa haka shi yafi alkairi.''
"Shine ma alkairi kije ki auri daidai dake amma ni ban kasance mazinaciya ba nasan Allah ba zai jarrabe ni da auran mazin.....Hannu na daga masa da fadin" Kaga ka daina kira na da wannan sunan tunda dai ka datse igiyoyin auranka shikkenan.
Aunty Murja dake zaune akan kujera tace."Ai gaskiya Abban Yusura kayi kuskure banji dadin sakin wulakancin da kayi mata ba haba ina laifi kayi daya ko biyu.A harzuke yace."Murja saki uku ne ya dace da wannan macuciyar saboda haka ki daina nadama dan na sake ta.
Juyowa yayi kaina yana magana ban tsaya sauraransa ba da sauri na bude kofar falon na fita ina jan akwatin kaya na.
Duk da babu wata tazara mai tsayi sai da na nemi adaidaita sahu ya sauke ni har kofar gida, dari biyu na bashi naja akwatin kayana na shiga gidan gabana har yanzu bai daina faduwa ba.
Yau Gwaggo towon alkama take sha'awa dan haka sau ta tuka abin ta da miyar bushashshiyar ku'bewa ta idar da sallar isha'i ta janyo kwanukan abincin domun taci nayi sallama a gidan.
Labule ta d'aga da fadin."Kamar muryar Sa'ida nake ji da daddaran nan." Nace."Itace Gwaggo.
Tana kallona tace."To maraba lale shigo daga ciki nima danshi (ra'ba) ne ya hana ni zaman tsakar gidan kin san kwana biyu an tafka ruwan sama.
Ina kokarin shiga dakin nace."Eh Kwarai hakane kwana biyu ana ruwa sosai."
"Amma dai lafiya dai domin na gan ki da akwati Allah dai yasa ba yaji kikayi ba.
A sanyaye na zauna gefan tabarmarta nace." Ya sake ni Gwaggo."
Wani irin shocking taji a jikinta da sauri tace."Sa'ida me kike fad'a"?
hawaye na zuba nace."Gwaggo ina nufin Alhaji Nura ya sake ni kinga ma shedar nan." Takardar hannuna na mika mata.
A sanyaye tace."Yo ni ina nayi karantawa Sa'ida me ya faru mutumin nan yayi miki wulakanci kuma saki nawa yayi miki."
"Saki uku ne."? Na fada muryata na rawa, Gwaggo innalillahi wa'ina ilaihi raji'un kawai take nanata wa cikin furgici tace."Sa'ida anya mutumin nan kuwa yana da hankali saki uku a lokaci guda ke kuwa wane irin laifi kikayi masa."?
Cikin kokarin danne damuwata nace." Asiri ne ya tono Alhaji Nura ya gane 'boyayyan sirrin dake lullu'be shine ya yanke min wannan hukuncin."
"Sa'ida ta ina zai gane ke ba budurwa bace bayan da farko kinyi masa bayani kuma ya amince.
hawaye na share nace." Nifa Gwaggo bana zargin kowa da mutuwar aurena sai Khalid." Da sauri tace."Tofa! bakya zargin kowa sai Khalid to me yayi miki yaron da tuntuni ya tafi gurin sana'arsa.
Hannu nasa na share fuskata nace."Gwaggo Khalid yaje gidana kuma har cikin 'kuryar dakina sai da ya shiga kuma Alhaji ya shigo ya sameshi.
Gwaggo rike baki tayi da fad'in "Ashe dai duk jan kunnan da nayi wa yaron nan be ji ba sai da yaje to me yaje yayi miki."?
Nace."Gwaggo ya kike tambayata me yaje yayi min gashinan abu a zahiri Khalid yaje gidana dan ya lalata min aure to bukatarsa ta biya sai ya zuba ruwa a kasa yasha.
Gwaggo ta dinga girgiza kai tana fadin."Kai amma wannan al'amari beyi dadi ba Khalid kuma bai kyauta duk da khalid ya kasance dan uwanki amma ai bai cancanta yana baligi irin wannan ba ya shiga gidan matan aure ba tare da neman izina ba dik abinda Alhaji Nura yayi masa na hukunci daidai ne tunda shi ya taka sharia.
Tace."To shikkenan Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi." na amsa da ameen ya Allah 'kawata nagode kwarai da gaske."
Haka rayuwar ta cigaba da tafiya yau da dad'i goge babu ta 'bangaran maigidan babu dad'i bangaran Aunty Murjar ma haka domin kwata kwata yanxu ni da ita bama shiri tun ranar da ta fahimci cewa na gane abinda takeyi ta sanja taku a gidan bata shiga sabgata sai da ni sa'i da lokaci inayi mata magana idan tayi ra'ayi ta amsa idan ba tayi ba ta share ni...........
Ranar Wata laraba tayi bakuwa da yake a falo suka zauna ina jin hayaniyarsu a dakina a nutse na bude kofa na fito. ganin matar dake zaune a kusa da ita yasa gabana ya yanke ya fadi da sauri nayi niyyar komawa daki sai kuma na fasa domin nasan sun riga sun gan ni! A dake na k'arasa falon na nemu kujera na zauna da fadin."Aunty Murja bakuwa kikayi ne."? Yau da mutuminci ta amsa min da "Eh wallahi dama yanzu take cewa zata tafi kuma baku gaisa ba.
Nace." Allah sarki ina kallonta nace."Ina wuni ya gida ya yara."? Ta amsa tana min wani irin kallo kaina na sunkuyar kasa gabana na faduwa ina addua a zuciyata akan Allah yasa bata gane ni ba.
Tace."Ni kam kamar na san wannan fuskar taki." na kalleta tare da kokarin kauda fargabata nace."Allah ko."? Tace."Kwarai kuwa kamar kece watanni takwas da suka wuce kikaje asibiti keda wata tsohuwa domun a duba miki virginal d'inki."
Nace."Anya kuwa bani bace." 'Yar dariya tayi tace."Kece mana ko ba sunanki Sa'ida ba."? Nace."Sunana Sa'ida mana." Tace."Sannan kuma kice min bake bace." shuru nayi mata domin idan nace zanyi magana zan iya fashewa da kuka shikkenan asirina ya tonu.
Aunty Murja tace." Maryam naji kina maganar wata takwas da suka wuce kuma yanzu auransu da Abban Yusura wata biyar kenan.
Tace."Nima dai abinda ya bani mamaki kenan lokacin taje akan a dubata ko ta qaru a d'inke ta lokacin dana duba sai na fahimci cewar kamar tayi gardama ne a lokacin da za'a kar'bi budurcinta sai na rubuta mata magunguna. har nake tambayarta ina mijinta a lokacin take cewa dani yayi tafiya shine yace tazo asibiti a dubata duk ina da sheda a rubuce."
Aunty Murja ta dinga yi min wani irin kallo ni kuma sai wani irin gumi nake zabgawa tamkar wacce tayi gudun famfalaki.!
Mi'kewa nayi jikina a bala'in mace na bude dakina na shiga na fada a saman gado kuka na dinga rafsawa ina kiran sunan Allah.
Aunty Murja wayarta ta dauka da fad'in "Dama neman hanyar da zan hukunta yarinyar nan nake domin nima data rufa min asiri zan rufa mata dan haka yanzu zan kira Abban Yusura a waya yazo kiyi masa bayani da bakin ki."
Dr Maryam tace."Aa Murja kada kiyi haka dan Allah wallahi ni ban fadi wannan maganar da wata manufa ba ki rufa mata asiri ta zauna dakinta."
Murmushin takaici tayi tace."Maryam wallahi ba zan kyale yarinyar nan ba domin itace tayi sanadiyar da Alhaji ya hana Aziza zuwa gidan nan sannan kuma tayi sanadin zuwana gidanmu nayi kwanaki tsayin shekarun aurena da mijina hakan bata ta'ba faruwa ba sai da ta shigo gidan sannan kuma kice na kyaleta ni dai kawai idan yazo kiyi masa cikakken bayanin da zai gamsu nayi miki alkawarin kyauta ta mussaman."
Dr Maryam tace."Ai shikkenan tunda ta kasa rufa miki asiri kema sai ki bankad'a nata." tace."Ashe kin fahimce ni.
Aunty Murja ta dauki waya ta kira mijinta tace dashi maza maza yazo gida akwai abinda yake faruwa. jin haka Alhaji Nura ya shigo motarsa ya kamo hanyar gida.
Wani irin tashin hankali ya shiga a lokacin da Dr Maryam ta gama warware masa 'boyayyan sirrin Sa'ida dake lullu'be! ya cire hularsa ya ajiye a hannun kujera yasa hannu ya sharce gumin goshinsa ido jajawur ya kallesu yace."A ranar dana kusanci yarinyar nan sai da na gane ba budurwa bace amma sabida ta iya tsari da 'karya ta kawo min wasu hojjojinta na banza to sabida haka tunda yanzu na gane gaskiya lamari zan dauki mataki a kanta domin ni ba zan lamunci zama da macen da zata ha'ince ni ba."
Yana gama maganarsa ya mike da saurin gaske ya kama hanyar dakinta, ido suka bishi dashi har ya bude dakin ya shiga.
Maganarsa naji a saman a kaina, a furgice na mike zaune ina kallonsa tunda na ganshi a burkice nasan ya samu labarin abinda yake da akwai.
Yana huci! yace." Sa'ida an yanka ta tashi yau Allah ya tona asirinki Dr Maryam ta bud'a min dukkanin sirrukan ki saboda haka tunda ke kin kasance ma ha'inciya macuciya kije na sake ki saki uku! sai kiji ki auri yaron da yake bibiyarki har gidan auranki wanda dama shi nake zargin ya lalataki kafin aure na dake."!
Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! kawai nake nanatawa a cikin raina yayin da nake jin wani irin mugun ciwon kai da mugun jiri d'akin sai juyawa yake dani a takaice dai ban san sanda ya gama cin mutuncinsa ya fita daga dakin ba.
*708 465 3262: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*58&59*
Na jima ina nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahiri raji'un a fili da zucci kafin naji wani k'arfin gwiwa gami da danga a tare dani......mikewa nayi jiki a mace na bude wardrobe na had'a kayana cikin akwati tsaf sai da na kwashe kayan sanyawata da duk abinda nasan ina bukata nasa a akwatin kana na rufe ta da kyar ina tunanin wanda zai dau'kar min.
Hijabi na nasa na d'aga akwatin tare da janyo hannunta da yake mai tayoyi ce sai kawai naja ta na bude dakin na fito kaina a kasa dan ko kadan bana kaunar na hada idona dasu....maganarsa naji a kunnena yana fad'in "Tsaya ki tafi da sakamonki cutar da kikayi min kuma na barki da Allah."
Tsayawa nayi ba tare dana juya ba zuciyata in banda tafarfasa babu abinda take
Daf dani ya tsaya hannunsa rike da takardar sakin nawa...."Kar'bi ki fice min daga gida bana bukatar sake ganinki shiyasa nayi miki saki uku domin hukuncin daya cancanta dake kenan "
Hawayen dake kokarin kwace min na danne hannuna na rawa na kar'bi takardar da fad'in "Nagode ina rokon Allah yasa haka shi yafi alkairi.''
"Shine ma alkairi kije ki auri daidai dake amma ni ban kasance mazinaciya ba nasan Allah ba zai jarrabe ni da auran mazin.....Hannu na daga masa da fadin" Kaga ka daina kira na da wannan sunan tunda dai ka datse igiyoyin auranka shikkenan.
Aunty Murja dake zaune akan kujera tace."Ai gaskiya Abban Yusura kayi kuskure banji dadin sakin wulakancin da kayi mata ba haba ina laifi kayi daya ko biyu.A harzuke yace."Murja saki uku ne ya dace da wannan macuciyar saboda haka ki daina nadama dan na sake ta.
Juyowa yayi kaina yana magana ban tsaya sauraransa ba da sauri na bude kofar falon na fita ina jan akwatin kaya na.
Duk da babu wata tazara mai tsayi sai da na nemi adaidaita sahu ya sauke ni har kofar gida, dari biyu na bashi naja akwatin kayana na shiga gidan gabana har yanzu bai daina faduwa ba.
Yau Gwaggo towon alkama take sha'awa dan haka sau ta tuka abin ta da miyar bushashshiyar ku'bewa ta idar da sallar isha'i ta janyo kwanukan abincin domun taci nayi sallama a gidan.
Labule ta d'aga da fadin."Kamar muryar Sa'ida nake ji da daddaran nan." Nace."Itace Gwaggo.
Tana kallona tace."To maraba lale shigo daga ciki nima danshi (ra'ba) ne ya hana ni zaman tsakar gidan kin san kwana biyu an tafka ruwan sama.
Ina kokarin shiga dakin nace."Eh Kwarai hakane kwana biyu ana ruwa sosai."
"Amma dai lafiya dai domin na gan ki da akwati Allah dai yasa ba yaji kikayi ba.
A sanyaye na zauna gefan tabarmarta nace." Ya sake ni Gwaggo."
Wani irin shocking taji a jikinta da sauri tace."Sa'ida me kike fad'a"?
hawaye na zuba nace."Gwaggo ina nufin Alhaji Nura ya sake ni kinga ma shedar nan." Takardar hannuna na mika mata.
A sanyaye tace."Yo ni ina nayi karantawa Sa'ida me ya faru mutumin nan yayi miki wulakanci kuma saki nawa yayi miki."
"Saki uku ne."? Na fada muryata na rawa, Gwaggo innalillahi wa'ina ilaihi raji'un kawai take nanata wa cikin furgici tace."Sa'ida anya mutumin nan kuwa yana da hankali saki uku a lokaci guda ke kuwa wane irin laifi kikayi masa."?
Cikin kokarin danne damuwata nace." Asiri ne ya tono Alhaji Nura ya gane 'boyayyan sirrin dake lullu'be shine ya yanke min wannan hukuncin."
"Sa'ida ta ina zai gane ke ba budurwa bace bayan da farko kinyi masa bayani kuma ya amince.
hawaye na share nace." Nifa Gwaggo bana zargin kowa da mutuwar aurena sai Khalid." Da sauri tace."Tofa! bakya zargin kowa sai Khalid to me yayi miki yaron da tuntuni ya tafi gurin sana'arsa.
Hannu nasa na share fuskata nace."Gwaggo Khalid yaje gidana kuma har cikin 'kuryar dakina sai da ya shiga kuma Alhaji ya shigo ya sameshi.
Gwaggo rike baki tayi da fad'in "Ashe dai duk jan kunnan da nayi wa yaron nan be ji ba sai da yaje to me yaje yayi miki."?
Nace."Gwaggo ya kike tambayata me yaje yayi min gashinan abu a zahiri Khalid yaje gidana dan ya lalata min aure to bukatarsa ta biya sai ya zuba ruwa a kasa yasha.
Gwaggo ta dinga girgiza kai tana fadin."Kai amma wannan al'amari beyi dadi ba Khalid kuma bai kyauta duk da khalid ya kasance dan uwanki amma ai bai cancanta yana baligi irin wannan ba ya shiga gidan matan aure ba tare da neman izina ba dik abinda Alhaji Nura yayi masa na hukunci daidai ne tunda shi ya taka sharia.