Sashe 85
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida suka ɗauki sati biyu a cel ba tare da an turasu kotu ba saboda tsaikon da aka samu daga gurin 'yan sanda na haɗa bayanai, sosai Binafa da Hanan suka shiga cikin tashin hankali ganin yadda aka mayar dasu kamar bayi an tsaresu ba duka ba zagi amma kuma su sauro suna ta sukuwa a jikinsu ga yunwa da ƙishir ruwa, abincin da ake basu sai kace 'yan bursina, da farko ƙin ci suka yi amma ganin yunwa zata yi musu lahani yasa suka fara ci, wannan wahalar da suke ciki yasa Binafa sarewa akan gwara ta sanar da iyayenta a kawo mata ɗauki duk da ta san zata fuskanci matsala dasu amma gwara a rabata da wannan wajen in yaso ko me zasu yi mata to suyi, ita dai ta bar cikin cel ɗin a rufe maganar ko dan kare mutuncin gidansu Iyayenta ma zasu so haka, lokacin da wani ɗan sanda ya kawo musu abincin dare a sannan ne take yi masa bayanin a bata wayarta zata kira 'yan uwanta susan da maganar, ɗan sanda yace su da suka ce ba su da kowa ai kawai su cigaba da zama har lokacin da za aje kotu, Binafa ta nima bashi cin hanci akan in sun fita zata biyashi da tsoka, yace shi ba irin waɗannan 'yan sandan bane da suke ɓarna a cikin aikinsu, dan haka ta kama kanta tun kafin ta ƙarawa kanta laifi kuma wayarta ma bata hannunsu bai san a inda take ba, yana gama faɗar haka ya wuce, jikinsu ne ya ƙara yin sanyi da labarin dan duk yadda suka ɗauka yafi ƙarfin lissafinsu, sosai hankalinsu ya ƙara tashi da damuwar makomar halin da suke ciki dan ba zasu jure zaman gurinba in ba haka ba wani ciwo sai ya shige su. Mako guda da auren Nafeesa a ranar monday aka tafi dasu babban offishin alkali dake nan high court, an gabatar da su tare da waɗanda suke yi ƙara zuwa office ɗin Alkali domin ko za a samu maslaha a daidaita lamarin, amma ana karanto wa Alkali laifinsu yace dole sai an je kotu saboda laifinsu ba ƙarama bace domin ayi musu hukuncin da zai zama izina ga masu irin halinsu dan haka ya tsaida ranar Alhamis zaman kotu, sai ya sallame su aka mayar dasu cel aka cigaba da tsaresu, a wannan lokacin kuka suka fara da dana sanin taɓa yarinyar mutane domin tabbas sune suka jawota jikinsu da kashe mata kuɗi har ta basu haɗin kai suka ɗaurata a hanyar, dana sani ne ya fara rufe su Binafa ta kalli Hanan cikin zubda hawaye.
Ina tsoron duniya tasan me muke aikatawa ban san ya 'yan uwana zasu É—auka ba, ni gwara tun yanzu na sanar dasu komai kafin a kaimu kotu.
Hmmmm ai aikin gama ya gama dan ɓacin suna kam mun gama kirawa kanmu, bawai tsoron dan an kaimu kotu nake ba, Allah yasa kar a kaimu gidan yari dan wlh bazan jurewa wahalar ba.
To sunƙi bamu ma haɗin kai balle na kira gida a kawo mana ɗauki, nasan dadyna zaiyi komai dan a rufe maganar, sai ma yanzu ma nake ganin wautata da na nima ɓoye maganar duk da a da ina hangen zan iya magance matsalar da kaina, ashe kuɗi basu isa su kwacemu ba, muna cikin babbar matsala fa Hanan.
Binafa ta ƙarasa maganar tana matso hawaye cike da tsantsar damuwa, haka suka dinga mayar da magana wanda tarin dana sanin da suke ciki suke fitarwa.
Kotu.
Kamar yadda Alkali ya sanar ranar Alhamis aka shiga kotu, wanda su Binafa sunyi matuƙar mamakin ganin mutanen da suka taru, ciki har yayanta Hassan da Yaya Taju dama sauran yayyinta da kuma wasu a family ɗinsu maza, wanda take tunanin ya aka yi suka san tana gurin, kuma komai da yake faruwa Hassan yana da masaniya domin DPO yana sanar dashi saboda sun amsa bumber ɗin juna, tashin hankali gobarar gemu! Domin kuwa Binafa samun kanta tayi da jin tsoro da fargaban tonuwar asirinsu a bainan Nasi, hawaye ya soma zarya a kuncinta ta sunne kai jikinta ya ɗauki ɗumi tare da kaɗawa tamkar zazzaɓi take ji, Hanan kuwa da yake babu nata a gurin bata damu ba sai damuwar hukuncin da za a yanke musu take yi dan bata fatan a yanke musu zaman gidan kaso bata shiryawa hakan ba, kowanne dai da abinda ya dameta. Sai da aka fara gabatar da wani ƙara na masu bashi daga bisani aka gabatar da ƙaran su Binafa, haka aka tisa keyarsu aka sanya a cikin wajen amsa tambaya, nan Hassan ya fara ɗauka a wayarsa a ɓoye dan yayi alƙawarin nunawa iyayensu wannan abu tunda bai sanar dasu ba sai iya 'yan uwansa maza da wasu maza cousin ɗinsu, nan aka gabatar da Baristan masu ƙara ya miƙe yayi bayani tare da gabatar da kansa, Alkali ya buƙaci ganin baristan su Binafa, aka sanar da ba su da shi nan take ya wakilta wani daga cikin lauyoyin gomnati akan ya tsaya musu, cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gudanar da komai. Aka ce ranar wanka ba a ɓoyon cibi su Binafa basu wahalar da Shari'a ba sun amsa laifinsu, hakan yasa alkhairi ya yanke musu hukunci kamar haka.
An yanke musu tarar kuɗi million huɗu da rabi sannan da zaman gidan yarin na shekara biyu tare da aiki mai tsanani, idan kuma basu bayar da kuɗin tara ba da za a bawa yarinyar da suka cutar, to zasu yi zaman kaso shekara shida shida. (Wannan hukuncin daga alƙalamin marubuciya ce Rahma, ban tsaya na yi bincike kan case irin nasu ba na yanke hukunci ne domin gajarce ɓata lokaci, da kuma sauƙaƙa ƙarshen labarin.)
Kuka suka fashe dashi domin ba suyi zaton wannan hukuncin ba, su bayar da taran kuɗin bai dame su sai zaman gidan yari ne ya ɗaga musu hankali sosai, nan Alkali ya ce za a iya ɗaukaka ƙara tare da sallamar case ɗin, haka aka tasa ƙeyar su Binafa aka fito dasu farfajiyar kotu, duk da Hassan yayi ƙoƙari sosai dan kar a bawa 'yan gidan tv da radio damar shigowa, sai dai duk da haka ansamu wasu sun ɗauki hotunan su Binafa a wayarsu, Binafa ta tsaya gaban 'yan uwanta ta tsuguna tana rusa kuka da cewar su ceceta su ɗaukaka ƙara a samar musu lauyan da zai karesu su fita daga wannan case ɗin, tasan suna da kuɗin da zasu yi mata haka, kuma in dady ya sani zaiyi wani abu su taimaka su sanar dashi, Hassan ne yace cikin ɓacin rai.
Wlh ko dady ya sani to ni da kaina zan hana ya taimake ki Binafa, domin ina so jikinki ya gaya miki ki gane Allah ɗaya ne, wataƙila zaki dawo cikin hankalinki ki daina yin ƙazantacciyar rayuwar da kika zaɓarwa kanki, ina mai tabbatar miki da nasan kina gurin 'yan sanda da komai da ke faruwa, ban sanar da su Dady ba saboda azo wannan gaɓar da zaki muzanta asirinki ya tonu kowa yasan wacece ke, dan haka kisa a ranki zaman gidan yari wajibi ne a gareki babu taimakon da zaki samu a gunmu sama da abinci da ɗan abin buƙata a gidan, pyan sanda ku wuce da ita.
Dan Allah yaya dan son Manzon Allah s.a.w kayi mini rai ka fitar dani a wannan kuncin, wlh tallahi nayi maka alƙawarin ba zan sake aikata komai ba na tuba na tuba na tuba.
Ta ƙare cikin wani irin gunjin kuka dan ko miƙewa da kyau ta kasa. Hassan ya ce cikin dakiya.
Binafa baki tuba ba tukuna sai kin ganki a gidan yari kina bin layin abinci a nan ne zaki tabbatar da yadda ake tuba. Abokai mu wuce kar mu ɓata lokacinmu a nan.
Ya ƙare maganar yana duban 'yan uwansa, Taju da duk jikinsa yayi sanyi saboda tausayinta yace.
Wlh ta bani taussayi sosai ƙila da gaske ta tuba ko za muyi wani abu ne akai Hassan.
Wani irin harara Hassan yayi masa yana cewa.
Babu abinda za muyi mata wannan shine kaɗai gatan da zamu nuna mata gwara ta ɗanɗana zaman gidan kaso taga yadda mutane ke cikin wahalar rayuwa, jin daɗi da gata da sangarci yasa take ganin zata aikara komai, ciki kuwa harda saɓon Allah mafi muni, ita ta haka ne zata nuna godiyarta a gareshi, to kaga gwara taga ikon Allah ya nuna mata da gatanta da komai amma ta rasa wa zai taimaketa, wataƙila hakan zai sa tasan ya rayuwa take ba munzo duniya dan mu shagalta da jin daɗi ba ne mu sabawa Allah son ranmu, Allah ya haliccemu ne domin mu bauta masa mu kaɗaitashi sannan mu yi koyi da halayyar Manzon Allah s.a.w domin mu gina lahirarmu da ayyuka na kwarai don mu samu Aljanna. Bawai dan banji tausayinta bane, ba kuma dan bana sonta bane, ina so ta gyara rayuwarta ne domin gatan da ya rage muyi mata ganen mu nusar da ita yadda rayuwa take da kuma yadda zata bi da lafiyarta da jin daɗinta gurin bautawa Allah.
Maganganunsa sunyi matuƙar tasiri a zuƙansu wanda yasa suka ƙarfafa masa guiwa akan hukuncin da aka yanke musu shine dai dai, sannan ma ba zuba ido zasu yi ba su barta sakaka a can dole zasu na kai mata ziyara dan ganin wace rayuwar take gudanarwa a can fatan su dai Allah yasa hakan ya zama silar shiryuwarta.
Da suka isa gida ne Hassan ya zayyano wa iyayensu duk abinda ke faru tare da bayanin Taju, Dady cike da tsantsar mamaki ya dubi momynsu yace.
Me yasa tsawon kwanakin nan kika ɓoye mini Binafa bata nan, kullun na tambayeki sai ki ce kin aiketa ko tana gidan su Taju taje hutu.
Wlh Alhaji text ta tura mini da wayarta akan tayi tafiya zuwa kano to bana son na sanar da kai kayi faɗa shiyasa naketa ɓoye maganar.
Cewar mony cike da damuwa, Hassan yace.
Ina tsoron duniya tasan me muke aikatawa ban san ya 'yan uwana zasu É—auka ba, ni gwara tun yanzu na sanar dasu komai kafin a kaimu kotu.
Hmmmm ai aikin gama ya gama dan ɓacin suna kam mun gama kirawa kanmu, bawai tsoron dan an kaimu kotu nake ba, Allah yasa kar a kaimu gidan yari dan wlh bazan jurewa wahalar ba.
To sunƙi bamu ma haɗin kai balle na kira gida a kawo mana ɗauki, nasan dadyna zaiyi komai dan a rufe maganar, sai ma yanzu ma nake ganin wautata da na nima ɓoye maganar duk da a da ina hangen zan iya magance matsalar da kaina, ashe kuɗi basu isa su kwacemu ba, muna cikin babbar matsala fa Hanan.
Binafa ta ƙarasa maganar tana matso hawaye cike da tsantsar damuwa, haka suka dinga mayar da magana wanda tarin dana sanin da suke ciki suke fitarwa.
Kotu.
Kamar yadda Alkali ya sanar ranar Alhamis aka shiga kotu, wanda su Binafa sunyi matuƙar mamakin ganin mutanen da suka taru, ciki har yayanta Hassan da Yaya Taju dama sauran yayyinta da kuma wasu a family ɗinsu maza, wanda take tunanin ya aka yi suka san tana gurin, kuma komai da yake faruwa Hassan yana da masaniya domin DPO yana sanar dashi saboda sun amsa bumber ɗin juna, tashin hankali gobarar gemu! Domin kuwa Binafa samun kanta tayi da jin tsoro da fargaban tonuwar asirinsu a bainan Nasi, hawaye ya soma zarya a kuncinta ta sunne kai jikinta ya ɗauki ɗumi tare da kaɗawa tamkar zazzaɓi take ji, Hanan kuwa da yake babu nata a gurin bata damu ba sai damuwar hukuncin da za a yanke musu take yi dan bata fatan a yanke musu zaman gidan kaso bata shiryawa hakan ba, kowanne dai da abinda ya dameta. Sai da aka fara gabatar da wani ƙara na masu bashi daga bisani aka gabatar da ƙaran su Binafa, haka aka tisa keyarsu aka sanya a cikin wajen amsa tambaya, nan Hassan ya fara ɗauka a wayarsa a ɓoye dan yayi alƙawarin nunawa iyayensu wannan abu tunda bai sanar dasu ba sai iya 'yan uwansa maza da wasu maza cousin ɗinsu, nan aka gabatar da Baristan masu ƙara ya miƙe yayi bayani tare da gabatar da kansa, Alkali ya buƙaci ganin baristan su Binafa, aka sanar da ba su da shi nan take ya wakilta wani daga cikin lauyoyin gomnati akan ya tsaya musu, cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gudanar da komai. Aka ce ranar wanka ba a ɓoyon cibi su Binafa basu wahalar da Shari'a ba sun amsa laifinsu, hakan yasa alkhairi ya yanke musu hukunci kamar haka.
An yanke musu tarar kuɗi million huɗu da rabi sannan da zaman gidan yarin na shekara biyu tare da aiki mai tsanani, idan kuma basu bayar da kuɗin tara ba da za a bawa yarinyar da suka cutar, to zasu yi zaman kaso shekara shida shida. (Wannan hukuncin daga alƙalamin marubuciya ce Rahma, ban tsaya na yi bincike kan case irin nasu ba na yanke hukunci ne domin gajarce ɓata lokaci, da kuma sauƙaƙa ƙarshen labarin.)
Kuka suka fashe dashi domin ba suyi zaton wannan hukuncin ba, su bayar da taran kuɗin bai dame su sai zaman gidan yari ne ya ɗaga musu hankali sosai, nan Alkali ya ce za a iya ɗaukaka ƙara tare da sallamar case ɗin, haka aka tasa ƙeyar su Binafa aka fito dasu farfajiyar kotu, duk da Hassan yayi ƙoƙari sosai dan kar a bawa 'yan gidan tv da radio damar shigowa, sai dai duk da haka ansamu wasu sun ɗauki hotunan su Binafa a wayarsu, Binafa ta tsaya gaban 'yan uwanta ta tsuguna tana rusa kuka da cewar su ceceta su ɗaukaka ƙara a samar musu lauyan da zai karesu su fita daga wannan case ɗin, tasan suna da kuɗin da zasu yi mata haka, kuma in dady ya sani zaiyi wani abu su taimaka su sanar dashi, Hassan ne yace cikin ɓacin rai.
Wlh ko dady ya sani to ni da kaina zan hana ya taimake ki Binafa, domin ina so jikinki ya gaya miki ki gane Allah ɗaya ne, wataƙila zaki dawo cikin hankalinki ki daina yin ƙazantacciyar rayuwar da kika zaɓarwa kanki, ina mai tabbatar miki da nasan kina gurin 'yan sanda da komai da ke faruwa, ban sanar da su Dady ba saboda azo wannan gaɓar da zaki muzanta asirinki ya tonu kowa yasan wacece ke, dan haka kisa a ranki zaman gidan yari wajibi ne a gareki babu taimakon da zaki samu a gunmu sama da abinci da ɗan abin buƙata a gidan, pyan sanda ku wuce da ita.
Dan Allah yaya dan son Manzon Allah s.a.w kayi mini rai ka fitar dani a wannan kuncin, wlh tallahi nayi maka alƙawarin ba zan sake aikata komai ba na tuba na tuba na tuba.
Ta ƙare cikin wani irin gunjin kuka dan ko miƙewa da kyau ta kasa. Hassan ya ce cikin dakiya.
Binafa baki tuba ba tukuna sai kin ganki a gidan yari kina bin layin abinci a nan ne zaki tabbatar da yadda ake tuba. Abokai mu wuce kar mu ɓata lokacinmu a nan.
Ya ƙare maganar yana duban 'yan uwansa, Taju da duk jikinsa yayi sanyi saboda tausayinta yace.
Wlh ta bani taussayi sosai ƙila da gaske ta tuba ko za muyi wani abu ne akai Hassan.
Wani irin harara Hassan yayi masa yana cewa.
Babu abinda za muyi mata wannan shine kaɗai gatan da zamu nuna mata gwara ta ɗanɗana zaman gidan kaso taga yadda mutane ke cikin wahalar rayuwa, jin daɗi da gata da sangarci yasa take ganin zata aikara komai, ciki kuwa harda saɓon Allah mafi muni, ita ta haka ne zata nuna godiyarta a gareshi, to kaga gwara taga ikon Allah ya nuna mata da gatanta da komai amma ta rasa wa zai taimaketa, wataƙila hakan zai sa tasan ya rayuwa take ba munzo duniya dan mu shagalta da jin daɗi ba ne mu sabawa Allah son ranmu, Allah ya haliccemu ne domin mu bauta masa mu kaɗaitashi sannan mu yi koyi da halayyar Manzon Allah s.a.w domin mu gina lahirarmu da ayyuka na kwarai don mu samu Aljanna. Bawai dan banji tausayinta bane, ba kuma dan bana sonta bane, ina so ta gyara rayuwarta ne domin gatan da ya rage muyi mata ganen mu nusar da ita yadda rayuwa take da kuma yadda zata bi da lafiyarta da jin daɗinta gurin bautawa Allah.
Maganganunsa sunyi matuƙar tasiri a zuƙansu wanda yasa suka ƙarfafa masa guiwa akan hukuncin da aka yanke musu shine dai dai, sannan ma ba zuba ido zasu yi ba su barta sakaka a can dole zasu na kai mata ziyara dan ganin wace rayuwar take gudanarwa a can fatan su dai Allah yasa hakan ya zama silar shiryuwarta.
Da suka isa gida ne Hassan ya zayyano wa iyayensu duk abinda ke faru tare da bayanin Taju, Dady cike da tsantsar mamaki ya dubi momynsu yace.
Me yasa tsawon kwanakin nan kika ɓoye mini Binafa bata nan, kullun na tambayeki sai ki ce kin aiketa ko tana gidan su Taju taje hutu.
Wlh Alhaji text ta tura mini da wayarta akan tayi tafiya zuwa kano to bana son na sanar da kai kayi faɗa shiyasa naketa ɓoye maganar.
Cewar mony cike da damuwa, Hassan yace.