Sashe 57
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka zaki faɗa ko? Wai ke kuɗi zai iya sayan darajarki da komai ko, ana maganar kishiya kina niman nuna baki damu ba akan kuɗi. To Allah ya tsayar akan ki, idan kin so zaki iya zuwa gidana muje gidan wani malami domin ayi aikin da zai hana auren, idan kin manta bari na tuna miki itama amayar zata zo ta haihu kuma duk dukiyar da Ibrahim ya tara da ita za aci, kuma yana faɗi ya mutu gado ya zana keda ita da yara kinga kin samu naƙasu a kasonki.
ÆŠan jim Nabila tayi dan sosai maganar Shema'u ya zauna a zuciyarta, sai ta nisa tana cewa.
Zan zo muyi maganar da safe In Sha Allah dan ban yarda kowa ya rabi dukiyar Ibrahim ba wlh.
Da dai ki zauna ki ga zama. Sai kin zo É—in.
Cewar Shema'u, nan suka yi sallama suka kashe wayar Nabila ta miƙe tana kwalawa mai aikinta kira ta fito daga ɗaki da sauri, sai tayi mata umarnin ta kwashe plate ɗin data ci abinci ta kai kitchen ta gyara gurin, sai ta wuce ɗakinta tayi shirin barci sai dai tunanin maganar auren Ibrahim ya tsaya mata a rai, gani take kamar wasa yake yi mata, sai dai maganar Shema'u na zancen ta miƙe taye akan kar wata tazo gidan ta rage mata samun wasu kaso na dukiyarsa, yayi matuƙar tasiri wanda take jin zata iya aikata komai ma dan kar hakan ta faru.
Ibrahim wajen tara da kwata na dare ya isa ƙofar gidansu Sameeha wanda ya samu motar Shamsu a Kofar gidan, hakan ya tabbatar masa da yana cikin gidan, ya kirashi yana ɗauka yace.
Sarkin zumuɗi ashe har ka iso, to ka yiwa Ikram magana ta sanar da yayarta ina ƙofar gida ta fito ina cikin mota.
Shamsu yana 'yar dariya yace to kana ya kashe wayar ya duba Ikram ya sanar da ita sakon Ibrahim, da sauri ta miƙe ta wuce cikin gida ta samu Umma a falo ta sanar mata, Umma tace.
Ki shiga ki faÉ—a mata tana ciki nasan dai bata yi barci ba.
Ikram ta wuce ciki ta samu tana kwance tare da danna waya kamar chart take yi.
Anty Yaya Ibrahim yazo yana waje a cikin mota.
Kije kice nayi barci bana cikin yanayin da zan fita masa.
Haba anty ba zai ji daÉ—i ba fa, kin san yau ne farkon zuwansa ki daure ki saurare shi tunda anriga an gama magana yana da damar da zai ganki, sannan ki aje batun Aminu dan wlh yayi hakane dan ya farraka farin cikinki.
Hmmm sarkin tsara zance, to jeki ce ina zuwa.
Sameeha ta faɗa tana zuro ƙafarta ƙasa, Ikram murmushi tayi ta fice. Sameeha babban Hijab ta zura ta saka wani plat shoe ta fito Umma tana cewa.
Ki dai saki fuskarki karki yarda ya gane kina cikin damuwa, kuma lokaci yayi da zaki yakice matsalar Aminu da 'yan uwansa ki fuskanci farin cikin daya tunkaro ki.
Humm tace bata iya magana ta fice, har jikin motar ta isa ta tsaya a waje, ya sauke gilass É—in mota yana cewa.
Ranki yadaÉ—e ayi mini alfarma a shigo mota saboda bana so mutane su gane nine a nan dan Allah, naso na shiga gida to Shamsu ya riga ni.
Bata ce komai ba ta je back seat ta kama zata buɗe sai ya cire motar a key ta buɗe ta shiga baya ta zauna ƙafarta suna waje, shima ya ɗaga glass ɗin motar ya ƙara AC ya juya yana dubanta, a hankali ta buɗe baki ta gaishe shi ya amsa fuska sake yana cewa.
Gimbiya ɗazun nine na kira na samu call waiting sai kuma na ƙara kira baki ɗaga ba, Allah yasa ba da x mijinki kike waya da shi ba, dan jikina ya ba ni da namiji kike magana.
Da sauri ta ɗago tana kallonsa dan taji mamakin fururucinsa, Ibrahim ya ɗage mata gira yana murmushin gefen baki sai ta sunne kai ƙasa ya cigaba da cewa.
Idan ina son abu na saka shi a raina ina iya hasashe akansa koda ba haka bane abinda na faɗa za a iya jiyo ƙamshin gaskiya. Dalilin daya saka na zo kenan dan ƙin ɗaukar wayata da kika yi, koda yake ƙila bakya ɗaukar number saboda tsaro. Da fatan kina cikin koshin lafiya.
Lafiya lau.
Ta bashi amsa a takaice, Ibrahim ya kira sunanta ta É—ago kai tana kallonsa ba tare da ta amsa ba.
Ina sonki har cikin zuciyata tun ranar dana yi tozali dake, ban taɓa kawo zan ƙara aure ba domin ni bani da ra'ayin haka, amma yanda kika samu gurbi a zuciyata naji bazan bari damar hakan ya kuɓuce mini ba tun sa'ilin dana samu labarin ba ki da aure, na tabbatar mijinki yana cikin cizon yatsa da kaicon rabuwa da ke domin kuwa ke Zara ce a cikin taurari, a ɗan binciken dana yi na tabbatar kina da tarbiya da kuma kyakkyawan hali, dan haka nake muradin zamowarki mata a gareni domin ki zame mini sanyin idaniyata, da fatan zaki zamo mini cikon addini na.
Tun sadda ya soma magana ta sunne kai ƙasa take saurarensa har saida ya kai aya kafin ya yi shuru, amma ta kasa magana, saboda tunaninta yafi karkata akan Aminu da maganganun da ya gaya mata ɗazun, sai tsinkayo maganar Ibrahim tayi yana cewa.
Nasan ban isa na samu gurbi lokaci guda ba a zuciyarki, saboda bansan irin ginin da Mijinki na baya ya gina ba a zuciyarki, hakan yasa nake jin rauni da sarewa musamman a yadda naga kin fito fuskarki ba walwala, hakan ya sa mini tunanin ko na takuraki ne da aurena, dan na san nayi miki katsalandan ban fara jin ra'ayinki ba na turo magabata na, dan haka har yanzu kina da zaɓi ina son duk abinda kike so, ni zan iya janyewa na haƙura muddun hakan zai saka ki cikin farin ciki Sameeha, nasan zan jima ina jinyar zuciyata amma dole zan haƙura na jure.
Nan ma Sameeha bata yi magana ba sai hawaye data ji yana ciko idanunta, ba zata ce Ibrahim yana da makusa ba dan tabbas taji zata iya zama da shi, amma tasan ba zata sake son wani sama da Aminu ba, tabbas ƙaddara tayi mata kutse a rayuwarta dan tunaninta da komai ya koma gun Aminu, gani take so da kishi yasa shi kasa danne damuwarsa har ya kirata ɗazun, mamakinta taya aka yi ya samu labarin aurenta. Ibrahim shuru yayi shima dan ya kula ba zata yi magana ba sai da suka ƙara minti goma a haka kafin ya kuma cewa cikin sanyin murya wanda yake nuna damuwa a tare da shi.
Sameeha zan baki lokaci ki zauna kiyi tunani da addu'a, idan har ban kwanta miki ba zan janye daga maganar aurenki domin farin cikinki shi nake so, amma ki sani ina ƙaunarki ina jinki har cikin jini na da ruhina, bana jin na taɓa jin irin ɗanɗanon sonki akan wata mace, ko Mubeena dana sota a baya banji irin haka akanta ba, ki je gida ni zan wuce sai da Safe ki gaida su Umma.
Ya ƙare maganar cikin rawar murya dan sosai yake jin ya fashe da kuka ko zai samu sauƙin yanayin daya samu kansa a ciki, sai a lokacin Sameeha ta ɗago kai sai caraf suka haɗa ido dan akwai hasken wutar mota ɗaya kunna na ciki, wani irin abu ne nan take ya kai sako a idanunsa tamkar walkiya, kuma hakan yayi tasiri a illahirin jikinsu, dan wani shokin ne ya tafi da sauri cikin jijiyoyin jikinsu, wanda hakan yasa Sameeha ta sunne kai tana sauke ɓoyayyan ajiyar zuciya siririn hawaye ya sauka a kuncinta, Ibrahim ya hura iska mai dumi daga bakinsa yana jin wani yanayi na sanyin AC yana ratsa shi tamkar zazzaɓi yake ji, sai ya juya ya gyara zamansa yana jiran ta fita daga motar ya ja, amma sai ya tsinkayi muryanta tana cewa.
Ba sai ka bani lokaci ba domin na amince da aurenka, fatanmu Allah yasa hakan ya zama alkhairi a garemu. Kayi haƙuri da yanayi na yau bana jin dadi ne, idan kaje gida ka gaida mini da Hajiya da kowa sai da safe.
Ta ƙare maganar tana yunƙurawa zata fito daga motar, da Sauri Ibrahim ya buɗe ya riga fitowa ya isa inda take zaune ya tsaya a jikin ƙofa yana dubanta, itama miƙewa tayi ta tsaya suna kallon juna, Ibrahim ya saki miskilin murmushi.
Kina son aurena kika yi da fuska kamar kinga mutuwa, bai kamata matar Ibrahim ta kasance a haka ba.
Kaifa kace baka son mutane susan kaine a nan, ya kamata ka bani hanya na wuce ka koma cikin mota,
Sameeha kowa ma ya ganni in dai dake nake a tare bani da damuwar komai, yanzu dai ki saki fuskarki kuma ki gaya mini me yasa ki fidda kwalla.
Hmmm ka bani hanya na wuce.
Ibrahim sai ya matso gabda ita kamar zaiyi kisin ɗinta, sai tayi baya da sauri ta zauna daɓar a seat, sai ya koma ya risina yana cewa.
Hawayen zan goge miki dan akwai sauran damshinsa a fuskarki, kar ki shiga gida ace na bigeki daga zuwa hira kija mini Yaya Zaidu yace ya fasa bani ke.
Wannan karan murmushi tayi tana cewa.
Tunda nace naji na gani ba wanda zai hana maka ni.
Allah da gaske kike yi? In dai haka ne zo ki shiga gida. Amma dai duk in kina cikin tunanin wani abu ki tuna ni Ibrahim Khalil ina sonki ina kaunar kasancewa dake.
Yana gama faɗar haka ya matsa ya buɗe mota ya shiga ya kunna, Sameeha ta fito ta rufe masa ƙofar ta tsaya jikin tagarsa tana dan murmushi.
Allah ya tsare hanya ya huta gajiya.
Amin matar Khalil ki É—aure ki aje number na a wayarki, kuma inna kira a É—auka kinji ranki yadade.
ÆŠan jim Nabila tayi dan sosai maganar Shema'u ya zauna a zuciyarta, sai ta nisa tana cewa.
Zan zo muyi maganar da safe In Sha Allah dan ban yarda kowa ya rabi dukiyar Ibrahim ba wlh.
Da dai ki zauna ki ga zama. Sai kin zo É—in.
Cewar Shema'u, nan suka yi sallama suka kashe wayar Nabila ta miƙe tana kwalawa mai aikinta kira ta fito daga ɗaki da sauri, sai tayi mata umarnin ta kwashe plate ɗin data ci abinci ta kai kitchen ta gyara gurin, sai ta wuce ɗakinta tayi shirin barci sai dai tunanin maganar auren Ibrahim ya tsaya mata a rai, gani take kamar wasa yake yi mata, sai dai maganar Shema'u na zancen ta miƙe taye akan kar wata tazo gidan ta rage mata samun wasu kaso na dukiyarsa, yayi matuƙar tasiri wanda take jin zata iya aikata komai ma dan kar hakan ta faru.
Ibrahim wajen tara da kwata na dare ya isa ƙofar gidansu Sameeha wanda ya samu motar Shamsu a Kofar gidan, hakan ya tabbatar masa da yana cikin gidan, ya kirashi yana ɗauka yace.
Sarkin zumuɗi ashe har ka iso, to ka yiwa Ikram magana ta sanar da yayarta ina ƙofar gida ta fito ina cikin mota.
Shamsu yana 'yar dariya yace to kana ya kashe wayar ya duba Ikram ya sanar da ita sakon Ibrahim, da sauri ta miƙe ta wuce cikin gida ta samu Umma a falo ta sanar mata, Umma tace.
Ki shiga ki faÉ—a mata tana ciki nasan dai bata yi barci ba.
Ikram ta wuce ciki ta samu tana kwance tare da danna waya kamar chart take yi.
Anty Yaya Ibrahim yazo yana waje a cikin mota.
Kije kice nayi barci bana cikin yanayin da zan fita masa.
Haba anty ba zai ji daÉ—i ba fa, kin san yau ne farkon zuwansa ki daure ki saurare shi tunda anriga an gama magana yana da damar da zai ganki, sannan ki aje batun Aminu dan wlh yayi hakane dan ya farraka farin cikinki.
Hmmm sarkin tsara zance, to jeki ce ina zuwa.
Sameeha ta faɗa tana zuro ƙafarta ƙasa, Ikram murmushi tayi ta fice. Sameeha babban Hijab ta zura ta saka wani plat shoe ta fito Umma tana cewa.
Ki dai saki fuskarki karki yarda ya gane kina cikin damuwa, kuma lokaci yayi da zaki yakice matsalar Aminu da 'yan uwansa ki fuskanci farin cikin daya tunkaro ki.
Humm tace bata iya magana ta fice, har jikin motar ta isa ta tsaya a waje, ya sauke gilass É—in mota yana cewa.
Ranki yadaÉ—e ayi mini alfarma a shigo mota saboda bana so mutane su gane nine a nan dan Allah, naso na shiga gida to Shamsu ya riga ni.
Bata ce komai ba ta je back seat ta kama zata buɗe sai ya cire motar a key ta buɗe ta shiga baya ta zauna ƙafarta suna waje, shima ya ɗaga glass ɗin motar ya ƙara AC ya juya yana dubanta, a hankali ta buɗe baki ta gaishe shi ya amsa fuska sake yana cewa.
Gimbiya ɗazun nine na kira na samu call waiting sai kuma na ƙara kira baki ɗaga ba, Allah yasa ba da x mijinki kike waya da shi ba, dan jikina ya ba ni da namiji kike magana.
Da sauri ta ɗago tana kallonsa dan taji mamakin fururucinsa, Ibrahim ya ɗage mata gira yana murmushin gefen baki sai ta sunne kai ƙasa ya cigaba da cewa.
Idan ina son abu na saka shi a raina ina iya hasashe akansa koda ba haka bane abinda na faɗa za a iya jiyo ƙamshin gaskiya. Dalilin daya saka na zo kenan dan ƙin ɗaukar wayata da kika yi, koda yake ƙila bakya ɗaukar number saboda tsaro. Da fatan kina cikin koshin lafiya.
Lafiya lau.
Ta bashi amsa a takaice, Ibrahim ya kira sunanta ta É—ago kai tana kallonsa ba tare da ta amsa ba.
Ina sonki har cikin zuciyata tun ranar dana yi tozali dake, ban taɓa kawo zan ƙara aure ba domin ni bani da ra'ayin haka, amma yanda kika samu gurbi a zuciyata naji bazan bari damar hakan ya kuɓuce mini ba tun sa'ilin dana samu labarin ba ki da aure, na tabbatar mijinki yana cikin cizon yatsa da kaicon rabuwa da ke domin kuwa ke Zara ce a cikin taurari, a ɗan binciken dana yi na tabbatar kina da tarbiya da kuma kyakkyawan hali, dan haka nake muradin zamowarki mata a gareni domin ki zame mini sanyin idaniyata, da fatan zaki zamo mini cikon addini na.
Tun sadda ya soma magana ta sunne kai ƙasa take saurarensa har saida ya kai aya kafin ya yi shuru, amma ta kasa magana, saboda tunaninta yafi karkata akan Aminu da maganganun da ya gaya mata ɗazun, sai tsinkayo maganar Ibrahim tayi yana cewa.
Nasan ban isa na samu gurbi lokaci guda ba a zuciyarki, saboda bansan irin ginin da Mijinki na baya ya gina ba a zuciyarki, hakan yasa nake jin rauni da sarewa musamman a yadda naga kin fito fuskarki ba walwala, hakan ya sa mini tunanin ko na takuraki ne da aurena, dan na san nayi miki katsalandan ban fara jin ra'ayinki ba na turo magabata na, dan haka har yanzu kina da zaɓi ina son duk abinda kike so, ni zan iya janyewa na haƙura muddun hakan zai saka ki cikin farin ciki Sameeha, nasan zan jima ina jinyar zuciyata amma dole zan haƙura na jure.
Nan ma Sameeha bata yi magana ba sai hawaye data ji yana ciko idanunta, ba zata ce Ibrahim yana da makusa ba dan tabbas taji zata iya zama da shi, amma tasan ba zata sake son wani sama da Aminu ba, tabbas ƙaddara tayi mata kutse a rayuwarta dan tunaninta da komai ya koma gun Aminu, gani take so da kishi yasa shi kasa danne damuwarsa har ya kirata ɗazun, mamakinta taya aka yi ya samu labarin aurenta. Ibrahim shuru yayi shima dan ya kula ba zata yi magana ba sai da suka ƙara minti goma a haka kafin ya kuma cewa cikin sanyin murya wanda yake nuna damuwa a tare da shi.
Sameeha zan baki lokaci ki zauna kiyi tunani da addu'a, idan har ban kwanta miki ba zan janye daga maganar aurenki domin farin cikinki shi nake so, amma ki sani ina ƙaunarki ina jinki har cikin jini na da ruhina, bana jin na taɓa jin irin ɗanɗanon sonki akan wata mace, ko Mubeena dana sota a baya banji irin haka akanta ba, ki je gida ni zan wuce sai da Safe ki gaida su Umma.
Ya ƙare maganar cikin rawar murya dan sosai yake jin ya fashe da kuka ko zai samu sauƙin yanayin daya samu kansa a ciki, sai a lokacin Sameeha ta ɗago kai sai caraf suka haɗa ido dan akwai hasken wutar mota ɗaya kunna na ciki, wani irin abu ne nan take ya kai sako a idanunsa tamkar walkiya, kuma hakan yayi tasiri a illahirin jikinsu, dan wani shokin ne ya tafi da sauri cikin jijiyoyin jikinsu, wanda hakan yasa Sameeha ta sunne kai tana sauke ɓoyayyan ajiyar zuciya siririn hawaye ya sauka a kuncinta, Ibrahim ya hura iska mai dumi daga bakinsa yana jin wani yanayi na sanyin AC yana ratsa shi tamkar zazzaɓi yake ji, sai ya juya ya gyara zamansa yana jiran ta fita daga motar ya ja, amma sai ya tsinkayi muryanta tana cewa.
Ba sai ka bani lokaci ba domin na amince da aurenka, fatanmu Allah yasa hakan ya zama alkhairi a garemu. Kayi haƙuri da yanayi na yau bana jin dadi ne, idan kaje gida ka gaida mini da Hajiya da kowa sai da safe.
Ta ƙare maganar tana yunƙurawa zata fito daga motar, da Sauri Ibrahim ya buɗe ya riga fitowa ya isa inda take zaune ya tsaya a jikin ƙofa yana dubanta, itama miƙewa tayi ta tsaya suna kallon juna, Ibrahim ya saki miskilin murmushi.
Kina son aurena kika yi da fuska kamar kinga mutuwa, bai kamata matar Ibrahim ta kasance a haka ba.
Kaifa kace baka son mutane susan kaine a nan, ya kamata ka bani hanya na wuce ka koma cikin mota,
Sameeha kowa ma ya ganni in dai dake nake a tare bani da damuwar komai, yanzu dai ki saki fuskarki kuma ki gaya mini me yasa ki fidda kwalla.
Hmmm ka bani hanya na wuce.
Ibrahim sai ya matso gabda ita kamar zaiyi kisin ɗinta, sai tayi baya da sauri ta zauna daɓar a seat, sai ya koma ya risina yana cewa.
Hawayen zan goge miki dan akwai sauran damshinsa a fuskarki, kar ki shiga gida ace na bigeki daga zuwa hira kija mini Yaya Zaidu yace ya fasa bani ke.
Wannan karan murmushi tayi tana cewa.
Tunda nace naji na gani ba wanda zai hana maka ni.
Allah da gaske kike yi? In dai haka ne zo ki shiga gida. Amma dai duk in kina cikin tunanin wani abu ki tuna ni Ibrahim Khalil ina sonki ina kaunar kasancewa dake.
Yana gama faɗar haka ya matsa ya buɗe mota ya shiga ya kunna, Sameeha ta fito ta rufe masa ƙofar ta tsaya jikin tagarsa tana dan murmushi.
Allah ya tsare hanya ya huta gajiya.
Amin matar Khalil ki É—aure ki aje number na a wayarki, kuma inna kira a É—auka kinji ranki yadade.