Sashe 61
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shikenan zan haƙura da komai na kama Aminu hannu biyu, amma bazan iya ƙarasa wannan bikin ba dan kar zuciyata ta buga. Bayan biki zanje naga ɗakunansu daga nan kuma munyi hannu riga.
Ina wlh baki isa ba ai dole ki ɗaure a ƙarasa dake kiga yadda aka tsara gidajensu kema kisa a tsara naki haka.
Bazan iya cigaba da bin lamarinsu ba dan ban'bu abinda zai haifar mini illa ciwon zuciya, ki rabu dani kawai Nafeesa na fuskanci gaskiya, na yarda sun fini kuma ba zan ƙara ja da haka ba zan yi daidai rayuwar da Allah ya zaɓar mini, damuwata duk randa Aminu ya san ni ya aura bansan ya zamu kwashe ba.
Najwa ko zamu koma gurin malamin nan da Binafa ta kaimu sai ayi miki aiki akansa koda ya ganki ya kasa rabuwa dake.
Bazan je ba domin wancen aikin dana bashi bana tunanin yayi, har takalmin Sameeha na kai masa sai gashi ta auri mijin daya fi na baya.
To ai ba akan haka kika saka yayi miki aiki ba, akan Aminu kika ce ayi aikin kuma baga shi kin samu nasara ba tunda yana kulaki kuna hira har kyautuka yake yi miki, ki zauna kiyi tunani dan wlh ina jiye miki ɓacin rana, duk da kince Hauwa zata yi miki aiki akai kema ya kamata ki yiwa kanki tanadi.
Kin san tunanin daya faÉ—o mini yanzu?
Najwa ta faÉ—a tana É—an murmushi, Nafeesa tace.
Sai kin faÉ—a.
Nafeesa babu abinda zanyi, idan ma yana ganina ya sake ni bazan damu ba domin yanzu Shamsu ne a tunanina, na ɗana arzikin gidan Aminu to ina da buƙatar ɗana gidan Sarauta, Shamsu ni ya fara so a rashina ne ya auri Ikram, na tabbatar in ya ƙara samun dama ta biyu a guna zai saurare ni.
Wani irin kallo Nafeesa takewa Najwa wanda yake ƙunshe da tarin magana, Najwa ta muskuta tana cewa.
Yadda na samu galaba akan raba Sameeha da Amunu ba tare da tayi mini komai ba, to tabbas sai na shaga tsakanin Shamsu sa Ikram tunda ta yi kokarin shiga gonata, domin ni ya fara so ta zo ta aureshi.
Taya zaki hukuntata da abinda bata sani ba? na tabbatar bata san saurayinki bane shi, Najwa ki tsaida tunanin ki guri É—aya ki tsaya a auren Aminu kawai.
Nafeesa ko bazan auri Shamsu ba wlh sai na saka Ikram ta shiga ƙunci, idan banyi haka ba bazan samu sassauci a zuciyata ba.
Kallonta kawai Nafeesa take yi dan ta kasa cewa komai saboda tsantsar mamakin Najwa, ta kula ba hassada kaɗai ke damunta dasu Sameeha ba har da mugunta da keta, ganin wanda yayi nisa baya jin kira yasa ta miƙe tana cewa.
Ni zan koma gidanmu tunda kin ce ba zakin koma gidan bikin ba, sai bayan kwana biyu.
Allah ya kaimu sai ta kwanta dan bata jin zata iya yi mata rakiya, Nafeesa ta fice tana mamakin Najwa da irin mugun tunaninta, ta rasa me su Sameeha suka yi mata da suka cancanci wannan ƙiyayya, gashi basu san tana yi ba kuma su sai nasara suke samu, a wannan karan ji tayi bata fata Najwa ta samu nasara akan abinda tace zata yiwa Ikram, tace a cikin ranta.
Nima zan bi sahunki ya saka takalmi irin naki na yi miki cindunduniya kamar yadda kika yiwa wasu, nima na rama musu, dan Ins' Sha Allah nima sai na auri Aminu.
Tayi maganar tana murmushi ta wuce zuwa bakin titi ta samu napep ta wuce gida.
******
Can gidan biki an cigaba da shagali kowa yanata hada hada ga ɗaukar hotuna da ake ta yi, amare suna shiga suna sauyawa gwanin sha'awa har zuwa bayan sallar la'asar, lokacin ne su Salma suka yiwa Sameeha sallama akan zasu wuce amma Hauwa da Laure sunce zasu je kai amarya ba dan komai ba sai dan su samu damar tariwo gulma yadda zasu ji daɗin bada labari, suga kuma irin daular da Sameeha ta samu, Sa'a dai tabi Salma da Adama dan tasan halin mijinta Kamalu bayi da sauki. Sameeha har cikin zuciyarta taji daɗin yadda su Hauwa suka muna mata kara duk da tasan da biyu zasu je kaita amma tasan sai dai su ga abinda zai damesu dan na gaba yayi gaba. Ikram tana zaune da ƙawayenta a ɗakin kusa dana Zaidu ta idar da salla suna hira, sai taji saƙo ya shigo wayarta, tana dubawa taga baƙuwar Number ta shiga wajen massage ta soma karanta saƙon kamar haka.
Amarya bakya laifi, ina taya ki murnan Auren Shamsu sai dai ba nan gizo ke saƙa ba domin kuwa ina ɗauke da cikinsa na wata biyar daya ƙunsa mini ya gudu ya barni, a gunku mutumin kirki ne shi amma tantirin mazinaci ne na nunawa sa'a, idan kuma baki yarda ba ni ina da hujja, kisha amarci lafiya tare da baban ɗan shege ko shegiya.
Wani irin gumi ne ya shiga karyowa Ikram innalillahi kawai take ambata a zuciyarta, da kyar tayi yaƙi da zuciyarta ta aro jarumta ta miƙe da sauri, wata ƙawarta tana cewa.
Lafiya Ikram waye yayi miki saƙo? ko Aliyu ne ya tono miki da tsohuwar soyayya.
Yaƙe tayi mata kawai tace eh, sai ta fice daga ɗakin saye da hijab ɗin data idar da sallah sai jakarta a hannu, ɗakin umma ta wuce ta shiga can uwar ɗakan da Sameeha ke zaune da Khairy da wata ƙawarta sai ɗiyan Inna Rukayya, Tana zuwa ta kama hannun Sameeha ta ce.
Anty zo mu je ki gani.
Ikram ki barni na huta ina fama da gajiya.
Dan Allah ki zo mu je.
Yadda Ikram tayi maganar kamar zata yi kuka yasa Sameeha miƙewa tabi bayanta, har tsakar gida suka fice zuwa ɗakin yaya Zaidu, Ikram ta ciro key a cikin ƙaramar jakarta ta buɗe bakin kana suka shiga ta rufo ƙofa, ta miƙawa Sameeha wayarta tana cewa.
Kinga saƙon da aka turo mini yanzu da wata number.
Sameeha ta amsa ta shiga karantawa ko ɗar bata ji ba a ranta dan wlh tasan sharri ne, a yadda Khairy take faɗar Shamsu ba zai taɓa aikata haka ba, ta duba Ikram tana cewa.
Ki kwantar da hankalinki wannan ba komai bane face sharrin maƙiya, zan bincika komai In Sha Allah gaskiya zata yi halinta. Yanzu ki saki ranki kar a gane kina cikin damuwa kisa a ranki dukkan nasara yana tare da ƙalubale.
Humm tace kana suka fita daga ɗakin Sameeha tana riƙe da wayar Ikram bata mayar mata ba, ta koma ɗakin umma Ikram kuma ta koma ɗakin da take tare da ƙawayenta. Sameeha bata sanar da kowa ba ta adana wayar Ikram a hannunta sai ta cigaba da hidimar ta.
Bayan sallar magrib aka kawo motoci da zasu ɗauki amare, Ikram aka fara kaiwa wanda Sameeha sai da tayi mata rakiya zuwa gidanta dake umguwar sarki, babban filat mai kyau iya ganin mai kallo, yaji kaya na zamani da komai ga sabuwar motarta a tsakar gidan an parker, sai da suka yi sallar Isha'i kafin aka ɗauki Sameeha daga gidan Ikram aka wuce da ita gidan mijinta dake unguwar rimi, wato gidansu Khairy a babban part wato gidan sama dake tsakiya, nan Ibrahim ya gyara mata aka zuba komai akan in an gama biki zai wuce da ita Abuja gidansa dake can dan a Abuja zasu zauna, sai dai ya riƙa zuwa yana duba Hajiya da uwargidansa, can gidansa na Abuja a gyare yake an ƙara zuba masa kaya na buƙata sosai, Abujan da Sameeha ta guda da farko gashi Allah ya nufa dole sai ta zauna a can. Bayan sun isa sai da aka fara kaita sashin Hajiya ta gaishe su kafin aka kawota nata sashin, faɗar haduwarsa ma bata lokaci ne dan falon ƙasa komai nata ne da Yaya Zaidu yayi musu oder, falon sama ne Ibrahim yayi nashi hidimar, su Hauwa dai anga abinda ya kusa sasu suma dan kuwa sun gama santin gidan Ikram da gidan Aminu ko rabin kyansa bai kai ba, sai gashi na Sameeha ya ninka na Ikram kuma gidan sama ne, gida ne da yake da gate kusan uku, gate ɗin farko za a wuce a shiga na biyu wanda za a ga titi gabas kudu yamma, to a titin dake ɓangaren kudu za a miƙe a isa gate ɗin gidan Sameeha, dama sashin Hajiya daga ɓangaren gabas yake a cikin gate na biyu, haka mutune suka dinga yiwa su Sameeha murna domin sun taka gadar nasarar rayuwa, daga bisani aka mayar da kowa gida aka bar amare a gidansu.
Wajen ƙarfe goma sai ga Ibrahim ya shigo sashinsu ba kowa a falo sai ya wuce ɗakin da yake matsayin na Sameeha a nan falon ƙasa, ya tura ƙofa da sallama ya sameta saman gado ta kwanta a gefe, shigowarsa yasa ta miƙe ta zauna tana amsa sallamarsa, ya zauna a gefen gadon ta shiga gaishe shi ya amsa fuska sake yana cewa.
Barka da baƙunta amayar Iro, kiyi haƙuri an barki ke kaɗai a hankali zaki saba. Bari na watsa ruwa ina zuwa.
Ya faɗa yana miƙewa, sai Sameeha ta tareshi da cewa.
Dan Allah ina so ka bani lokaci kaÉ—an zamu yi wata magana.
Ibrahim sai ya koma ya zauna yana sauraren ta, jakarta dake gefe ta ɗauko ta ciro wayar Ikram ta buɗe wajen massage ta miƙa masa tana cewa.
Ɗazun da yamma aka turowa Ikram wannan saƙon shine nace bari na fara tattaunawa da kai dan bamu faɗawa kowa ba.
Ya amsa wayar ya karanta ya ƙara karantawa cike da mamaki, bai ce komai ba sai wayarsa daya ciro a aljihun gabar rigarsa ya danna number ɗin Shamsu ya kirashi, yana ɗauka yace.
Ka isa gida ne?
Eh na iso amma Ikram tana ta kuka tunda na shigo, sai maganganu take faÉ—a mini na rasa ina zancenta ya dosa.
Oka gamu nan zuwa.
Abin da Ibrahim ya faÉ—a kenan, ya kalli Sameeha yana cewa.
Tashi mu je gidan.
Hmmm ai shiyasa na amsa wayar dan nasan halin Ikram ba tada haƙuri wlh, kuma sai da nace mata tabar komai a hannuna shiyasa ban tun kari kowa da maganar ba sai kai yanzu.
Tashi dai muje In Sha Allah zamu gano wacce ta turo da wannan saƙon.
Ina wlh baki isa ba ai dole ki ɗaure a ƙarasa dake kiga yadda aka tsara gidajensu kema kisa a tsara naki haka.
Bazan iya cigaba da bin lamarinsu ba dan ban'bu abinda zai haifar mini illa ciwon zuciya, ki rabu dani kawai Nafeesa na fuskanci gaskiya, na yarda sun fini kuma ba zan ƙara ja da haka ba zan yi daidai rayuwar da Allah ya zaɓar mini, damuwata duk randa Aminu ya san ni ya aura bansan ya zamu kwashe ba.
Najwa ko zamu koma gurin malamin nan da Binafa ta kaimu sai ayi miki aiki akansa koda ya ganki ya kasa rabuwa dake.
Bazan je ba domin wancen aikin dana bashi bana tunanin yayi, har takalmin Sameeha na kai masa sai gashi ta auri mijin daya fi na baya.
To ai ba akan haka kika saka yayi miki aiki ba, akan Aminu kika ce ayi aikin kuma baga shi kin samu nasara ba tunda yana kulaki kuna hira har kyautuka yake yi miki, ki zauna kiyi tunani dan wlh ina jiye miki ɓacin rana, duk da kince Hauwa zata yi miki aiki akai kema ya kamata ki yiwa kanki tanadi.
Kin san tunanin daya faÉ—o mini yanzu?
Najwa ta faÉ—a tana É—an murmushi, Nafeesa tace.
Sai kin faÉ—a.
Nafeesa babu abinda zanyi, idan ma yana ganina ya sake ni bazan damu ba domin yanzu Shamsu ne a tunanina, na ɗana arzikin gidan Aminu to ina da buƙatar ɗana gidan Sarauta, Shamsu ni ya fara so a rashina ne ya auri Ikram, na tabbatar in ya ƙara samun dama ta biyu a guna zai saurare ni.
Wani irin kallo Nafeesa takewa Najwa wanda yake ƙunshe da tarin magana, Najwa ta muskuta tana cewa.
Yadda na samu galaba akan raba Sameeha da Amunu ba tare da tayi mini komai ba, to tabbas sai na shaga tsakanin Shamsu sa Ikram tunda ta yi kokarin shiga gonata, domin ni ya fara so ta zo ta aureshi.
Taya zaki hukuntata da abinda bata sani ba? na tabbatar bata san saurayinki bane shi, Najwa ki tsaida tunanin ki guri É—aya ki tsaya a auren Aminu kawai.
Nafeesa ko bazan auri Shamsu ba wlh sai na saka Ikram ta shiga ƙunci, idan banyi haka ba bazan samu sassauci a zuciyata ba.
Kallonta kawai Nafeesa take yi dan ta kasa cewa komai saboda tsantsar mamakin Najwa, ta kula ba hassada kaɗai ke damunta dasu Sameeha ba har da mugunta da keta, ganin wanda yayi nisa baya jin kira yasa ta miƙe tana cewa.
Ni zan koma gidanmu tunda kin ce ba zakin koma gidan bikin ba, sai bayan kwana biyu.
Allah ya kaimu sai ta kwanta dan bata jin zata iya yi mata rakiya, Nafeesa ta fice tana mamakin Najwa da irin mugun tunaninta, ta rasa me su Sameeha suka yi mata da suka cancanci wannan ƙiyayya, gashi basu san tana yi ba kuma su sai nasara suke samu, a wannan karan ji tayi bata fata Najwa ta samu nasara akan abinda tace zata yiwa Ikram, tace a cikin ranta.
Nima zan bi sahunki ya saka takalmi irin naki na yi miki cindunduniya kamar yadda kika yiwa wasu, nima na rama musu, dan Ins' Sha Allah nima sai na auri Aminu.
Tayi maganar tana murmushi ta wuce zuwa bakin titi ta samu napep ta wuce gida.
******
Can gidan biki an cigaba da shagali kowa yanata hada hada ga ɗaukar hotuna da ake ta yi, amare suna shiga suna sauyawa gwanin sha'awa har zuwa bayan sallar la'asar, lokacin ne su Salma suka yiwa Sameeha sallama akan zasu wuce amma Hauwa da Laure sunce zasu je kai amarya ba dan komai ba sai dan su samu damar tariwo gulma yadda zasu ji daɗin bada labari, suga kuma irin daular da Sameeha ta samu, Sa'a dai tabi Salma da Adama dan tasan halin mijinta Kamalu bayi da sauki. Sameeha har cikin zuciyarta taji daɗin yadda su Hauwa suka muna mata kara duk da tasan da biyu zasu je kaita amma tasan sai dai su ga abinda zai damesu dan na gaba yayi gaba. Ikram tana zaune da ƙawayenta a ɗakin kusa dana Zaidu ta idar da salla suna hira, sai taji saƙo ya shigo wayarta, tana dubawa taga baƙuwar Number ta shiga wajen massage ta soma karanta saƙon kamar haka.
Amarya bakya laifi, ina taya ki murnan Auren Shamsu sai dai ba nan gizo ke saƙa ba domin kuwa ina ɗauke da cikinsa na wata biyar daya ƙunsa mini ya gudu ya barni, a gunku mutumin kirki ne shi amma tantirin mazinaci ne na nunawa sa'a, idan kuma baki yarda ba ni ina da hujja, kisha amarci lafiya tare da baban ɗan shege ko shegiya.
Wani irin gumi ne ya shiga karyowa Ikram innalillahi kawai take ambata a zuciyarta, da kyar tayi yaƙi da zuciyarta ta aro jarumta ta miƙe da sauri, wata ƙawarta tana cewa.
Lafiya Ikram waye yayi miki saƙo? ko Aliyu ne ya tono miki da tsohuwar soyayya.
Yaƙe tayi mata kawai tace eh, sai ta fice daga ɗakin saye da hijab ɗin data idar da sallah sai jakarta a hannu, ɗakin umma ta wuce ta shiga can uwar ɗakan da Sameeha ke zaune da Khairy da wata ƙawarta sai ɗiyan Inna Rukayya, Tana zuwa ta kama hannun Sameeha ta ce.
Anty zo mu je ki gani.
Ikram ki barni na huta ina fama da gajiya.
Dan Allah ki zo mu je.
Yadda Ikram tayi maganar kamar zata yi kuka yasa Sameeha miƙewa tabi bayanta, har tsakar gida suka fice zuwa ɗakin yaya Zaidu, Ikram ta ciro key a cikin ƙaramar jakarta ta buɗe bakin kana suka shiga ta rufo ƙofa, ta miƙawa Sameeha wayarta tana cewa.
Kinga saƙon da aka turo mini yanzu da wata number.
Sameeha ta amsa ta shiga karantawa ko ɗar bata ji ba a ranta dan wlh tasan sharri ne, a yadda Khairy take faɗar Shamsu ba zai taɓa aikata haka ba, ta duba Ikram tana cewa.
Ki kwantar da hankalinki wannan ba komai bane face sharrin maƙiya, zan bincika komai In Sha Allah gaskiya zata yi halinta. Yanzu ki saki ranki kar a gane kina cikin damuwa kisa a ranki dukkan nasara yana tare da ƙalubale.
Humm tace kana suka fita daga ɗakin Sameeha tana riƙe da wayar Ikram bata mayar mata ba, ta koma ɗakin umma Ikram kuma ta koma ɗakin da take tare da ƙawayenta. Sameeha bata sanar da kowa ba ta adana wayar Ikram a hannunta sai ta cigaba da hidimar ta.
Bayan sallar magrib aka kawo motoci da zasu ɗauki amare, Ikram aka fara kaiwa wanda Sameeha sai da tayi mata rakiya zuwa gidanta dake umguwar sarki, babban filat mai kyau iya ganin mai kallo, yaji kaya na zamani da komai ga sabuwar motarta a tsakar gidan an parker, sai da suka yi sallar Isha'i kafin aka ɗauki Sameeha daga gidan Ikram aka wuce da ita gidan mijinta dake unguwar rimi, wato gidansu Khairy a babban part wato gidan sama dake tsakiya, nan Ibrahim ya gyara mata aka zuba komai akan in an gama biki zai wuce da ita Abuja gidansa dake can dan a Abuja zasu zauna, sai dai ya riƙa zuwa yana duba Hajiya da uwargidansa, can gidansa na Abuja a gyare yake an ƙara zuba masa kaya na buƙata sosai, Abujan da Sameeha ta guda da farko gashi Allah ya nufa dole sai ta zauna a can. Bayan sun isa sai da aka fara kaita sashin Hajiya ta gaishe su kafin aka kawota nata sashin, faɗar haduwarsa ma bata lokaci ne dan falon ƙasa komai nata ne da Yaya Zaidu yayi musu oder, falon sama ne Ibrahim yayi nashi hidimar, su Hauwa dai anga abinda ya kusa sasu suma dan kuwa sun gama santin gidan Ikram da gidan Aminu ko rabin kyansa bai kai ba, sai gashi na Sameeha ya ninka na Ikram kuma gidan sama ne, gida ne da yake da gate kusan uku, gate ɗin farko za a wuce a shiga na biyu wanda za a ga titi gabas kudu yamma, to a titin dake ɓangaren kudu za a miƙe a isa gate ɗin gidan Sameeha, dama sashin Hajiya daga ɓangaren gabas yake a cikin gate na biyu, haka mutune suka dinga yiwa su Sameeha murna domin sun taka gadar nasarar rayuwa, daga bisani aka mayar da kowa gida aka bar amare a gidansu.
Wajen ƙarfe goma sai ga Ibrahim ya shigo sashinsu ba kowa a falo sai ya wuce ɗakin da yake matsayin na Sameeha a nan falon ƙasa, ya tura ƙofa da sallama ya sameta saman gado ta kwanta a gefe, shigowarsa yasa ta miƙe ta zauna tana amsa sallamarsa, ya zauna a gefen gadon ta shiga gaishe shi ya amsa fuska sake yana cewa.
Barka da baƙunta amayar Iro, kiyi haƙuri an barki ke kaɗai a hankali zaki saba. Bari na watsa ruwa ina zuwa.
Ya faɗa yana miƙewa, sai Sameeha ta tareshi da cewa.
Dan Allah ina so ka bani lokaci kaÉ—an zamu yi wata magana.
Ibrahim sai ya koma ya zauna yana sauraren ta, jakarta dake gefe ta ɗauko ta ciro wayar Ikram ta buɗe wajen massage ta miƙa masa tana cewa.
Ɗazun da yamma aka turowa Ikram wannan saƙon shine nace bari na fara tattaunawa da kai dan bamu faɗawa kowa ba.
Ya amsa wayar ya karanta ya ƙara karantawa cike da mamaki, bai ce komai ba sai wayarsa daya ciro a aljihun gabar rigarsa ya danna number ɗin Shamsu ya kirashi, yana ɗauka yace.
Ka isa gida ne?
Eh na iso amma Ikram tana ta kuka tunda na shigo, sai maganganu take faÉ—a mini na rasa ina zancenta ya dosa.
Oka gamu nan zuwa.
Abin da Ibrahim ya faÉ—a kenan, ya kalli Sameeha yana cewa.
Tashi mu je gidan.
Hmmm ai shiyasa na amsa wayar dan nasan halin Ikram ba tada haƙuri wlh, kuma sai da nace mata tabar komai a hannuna shiyasa ban tun kari kowa da maganar ba sai kai yanzu.
Tashi dai muje In Sha Allah zamu gano wacce ta turo da wannan saƙon.