Sashe 70
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sameeha ta faɗa cikin ɗaure fuska, sai Ikram taja bakinta tayi shuru zuciyarta tana tafarfasa dan burinta ta samu damar da zata nakaɗawa Najwa duka ta yadda nan gaba zata shiga shakkarsu. Wajen ƙarfe sha ɗaya da kwata aka ɗaura auren Najwa a masallacin bakin titi na unguwarsu, wanda ɗumbin mutane suka shaida kuma Aminu da 'yan uwansa sun je dan Alhasan ne ya karɓan masa auren, Zaidu yana daga can gefe yana kallon ikon Allah dan sosai lamarin ya bashi mamaki tare da girgiza lissafinsa, wai Aminu ne ya Auri Najwa, ya rasa yadda zai lissafa lamarin yayi daidai da kwakwalwarsa, haka jikinsa yayi sanyi kalau ya kasa miƙewa ya fito daga masallacin har sai da mutane suka watse kafin ya iya yunƙurawa ya fito, a daidai lokacin su Aminu suna tsaye da wasu abokansa mutum biyu, ido cikin ido suka kalli juna da Zaidu amma ya kasa ce masa komai ya saka takalminsa ya wuce zuwa gidansu Najwa, koda ya ƙaraso ƙofar gidan yaga Anwar sai yace masa yayi sauri ya kira masa Ikram da Sameeha su zo, yace to kana ya shiga gidan ya samu ganin Ikram ya faɗa mata Sameeha kuwa tana can gurin saka tuwo a leda ana kullewa, Ikram bata kirata ba dan tasan halinta ko tace tazo ba zata zo ba, sai ta fito waje ta hango Zaidu fuska a mugun ɗaure, ta ƙarasa tana cewa.
Yaya lafiya naga fuskarka a É—aure, ko ba a faura auren bane?
Ikram ina Sameeha?
Tana cikin gida tana aiki kasanta ko na kirata ba lallai tazo ba.
Ki shiga ki kirata tazo mu tafi gida.
Saboda me? Meya faru yaya?
Hmmm Zaidu yayi ajiyar zuciya yana girgiza kai saboda ɓacin rai, yace cikin takaici.
Kinsan wai Aminu mijin Sameeha shine ya auri Najwa, ko baku ji sanarwa bane.
Mun ji mana ance Muhammad Al'amin, amma ai bamu gane shi bane, kutumelesi Najwa ta iya cin amana ta rasa wanda zata aura sai Aminu.
Ta faɗa cike da ɓacin rai ta juya a fusace tayi cikin gida a guje, tana faɗawa tayi sa'a Najwa tana tsakar gida da kawayenta suna hotuna, Ikram bata yi wata wata ba ta isa gabanta ta sharara mata mari tare shaƙo wuyanta ta maƙureta ta kaita ƙasa ta shiga dukanta kamar Allah ya aikota, ƙarfinsu bazai zo ɗaya ba saboda Ikram Aljanunta ne suka tashi suke hukunci, nan fa gida ya hautsine aka shiga ƙoƙarin kwatar Najwa amma ina Ikram ta hau ruwan cikinta tana dukanta iya ƙarfinta, nan fa aka fita aka kira maza wanda Zaidu yana ganin haka ya nufo gidan da gudu ya shigo, ga Sameeha ta yi kokarin kama hannun Ikram amma ina ƙarfinsu ba ɗaya ba, Ihu kawai Najwa take saki tana aceceta zata kasheta, da kyar Zaidu ya kama Ikram ta baya ya matse hannyenta da jikinta iya ƙarfinsa ya shiga tofa mata addu'a, yayan Najwa Junaid shima ya saka ƙarfi ya taimakawa Zaidu suka ɗaga Ikram daga cikin Najwa, Najwa kuwa marayan kuka ta saki ga bakinta ya fashe yana jini fuska tayi jajir dan wahala, a haka su Zaidu suka fitar da Ikram da kyar suka saka a motarsa ya rufe ta ta waje, ya koma cikin gidan ya samu ana gogewa Najwa fuska ya kalleta cikin jajayen idonsa ya koma da kallonsa gurin Sameeha yace cikin fusata.
Ina umma, je ki kirata mubar gidan nan yanzu.
Yaya meye haka? Dan Allah ka tafi sannan umma.
Bata rufe baki ba ya daga hannu zai kwasa mata mari saboda haushin musun data tsaya yi masa, sai ya riƙe hannunsa tunawa da wani abu da yayi ya kalleta rai ɓace a mugun fusace.
Dan ubanki ki tattaro yaranki kizo mu wuce, Umma Umma kina ina.
Gani nan Zaidu wai lafiya kake abu kamar wanda ya sha kwaya, Ikram ta gama nata kaima zaka É—aura.
Haba Zaidu in rai ya ɓaci bai kamata hankali ya gushe ba, kayi haƙuri ka faɗa mana me ya faru, ina kuma ka kai Ikram.
Cewar Innar Najwa, Zaidu ya danƙara mata wani mummunar kallo yace cikin ɓacin rai.
Dole zaki faÉ—i haka mana tunda burunku ya cika kin aurawa Najwa Aminu mijin Sameeha daya saka, sai yanzu ma kwakwalwata suke haÉ—o mini abubuwa akan 'yarki Najwa mara godiyar Allah rashin kunya da tarbiyya.
Ya faɗa yana zuba guntun murmushi, Umma ce ta matso ta wanke shi da mari akan rashin kunyar da yayi wa Inna, duk da taji maganar Najwa ta auri Aminu ya daki zuciyarta amma haka ta danne, Sameeha kuwa tun sa'ilin daya faɗa ta wuce suf suf ta fice daga gidan, Zaidu ya kalli umma yana son yin magana ta daka masa tsawa akan ya fita tare da nuna masa hanyar fita, bai ce komai ba ya fice ransa a matuƙar ɓace, Inna kuwa mutuwar tsaye tayi tana jin abinda yafi ƙarfin kunnen ta, Umma kuwa ɗakin Inna ta shiga ta ɗauko hijab ta saka bata cewa kowa komai ba ta fito daga gidan, ta samesu a wajen motar Zaidu, tace.
BuÉ—e motar mu wuce anjima zai kazo ka É—auki motar Sameeha.
Ba musu ya buɗe motar umma da Sameeha suka zauna gidan baya suka saka Ikram a tsakiya da taketa kukan baƙin ciki, Anwar dasu Abi suka shiga gaban mota sai Zaidu ya zauna mazaunin driver ya tada mota suka nufi gida.
_Hmmm an zo gurin..._
[4/27, 8:45 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
42.
Inna kuwa bayan mutuwar tsaye da ta yi numfashinta ne ya soma barazanar barin jikinta wanda nan take ta nima yanke jiki ta faÉ—i amma mutane suka tarota, suka kaita zuwa É—akinta suka kwantar a gado tana mayar da numfashi da Æ™arfi tare da zufa daya rufeta, sai sannu 'yan uwa suke jera mata idonta a rufe. Æangaren Najwa kuwa Nafeesa ce ta taimaka mata ta tashi tare da wata Æ™awarsu, sai suka shiga kakkaÉ“e mata jiki kuka kawai take yi tana alwashin sai ta rama abinda Ikram tayi mata, ko kaÉ—an bata yi dana sanin dan sun san Aminu ta aura ba, ita taso ma ba a lokacin suka sani ba sai in an kaita suga gidan Sameeha ne ya zama mallakinta, duk da tana jin mutanen cikin gidan suna surutunta amma bai dame ta ba dan tasan watan maganar ne ya tsaya, da É—ingishi ta shiga É—akinta ta zauna bakin gado tana shafa gashinta daya yi kura, dan tuni É—ankwalin da aka É—aura mata yayi nashi wajen, a lokacin ne ta buÆ™aci wayarta domin ta kira 'yan daban da suka taÉ“a yiwa Jamila duka ta sakasu su je su rama mata abinda Ikram tayi mata, sai ta kalli Nafeesa tana cewa.
Ina wayata.?
Kin manta wayar tana hannunki da kuka soma kokawa, tuni kuka bi ta kanta taci screen, ko haske bata yi duk ta fashe tayi baƙi.
Wlh Ikram taci bashi yadda ta dukeni sai jikinta ya gaya mata, kuma wlh sai na saka tayi asara kamar yadda nima nayi asarar wayata.
Ta faÉ—a tana girgiza kai, Nafeesa ta isa gefenta ta zauna ta dafa kafaÉ—arta.
Najwa an riga an ɗaura aurenki ya kamata ki gane yanzu rigima ba naki bane, ki barta da Allah ki fuskanci ƙalubalen dake gabanki tunda su inna sun san mijin Sameeha kika aure, sai ki tanadi maganar da zaki kare kanki.
Nafeesa dan sun sani sai me, an dai riga an É—aura ni banda damuwa da su domin dai nayi nasara da aurensa, ni yanzu in har ban rama abinda Ikram tayi mini ba ban cika sunana ba wlh.
To shikenan Nafeesa tace ta koma gefe tana zuba abinci dan dama zasu ci ne suka fita waje yin hoto in sun gama su dawo su ci, Najwa sai kumbure kumbure take tana girgiza kai, ta cire sim ɗinta ta ce Nafeesa ta saka mata a wayarta saboda kar a kirata aji ba'a samu tunda akwai ƙawayenta da basu san gidansu ba, ba musu ta cire ɗayan layinta da bata cika amfani dashi ba ta saka ajaka kana ta sakawa Najwa nata sim ɗin.
Baba ne da yayyin Najwa su uku suka shigo gidan, basu zame ko ina ba sai ɗakin inna, sun samu ta dawo hayyacinta tana zaune gefen gado sai dai har lokacin gumi take yi da alama in aka gwada jininta a lokacin to ya hau, ganin sun shigo yasa mutanen ɗakin suka fita baba ya samu gefe ya tsaya yana dubanta yaran kuma duk zama suka yi a ƙasa, baba yace cikin kulawa.
Sannu Zulai ya jikin?
Da sauki Alhamdulillahi, kaina ne ke sara mini kamar zai rabe.
Allah ya sauke ya baki lafiya. Wai abinda naji da gaske ne akan Najwa mijin Sameeha ta aura, yanzu Junaid ya sameni da maganar wai har aljanun Ikram sun tashi sun yi faÉ—a da Najwa.
Wlh malam nima a bakin Zaidu muka ji maganar tunda kasan shi yasan mijin 'yar uwarsa, sannan da shi aka daura aure, abinda ya bani mamaki da tsoro taya duk aka amsa musu bamu gane komai dan gane da haka ba, Najwa dai nasan ta san komai da haÉ—in bakinta da shi mijin Sameeha suka shirya komai, kuma 'yan uwansa sun san ita ce shiyasa suka ki bari aje kai kaya ashe da walakin goro a miya, hatta kayan lefe maza suka kawo dan kar mata su kawo a gane 'yan uwansa ne dan duk mun sansu.
Amma wannan yarinya ta haÉ—a gurmi, da wani ido zamu kalli Halima, ai ana barin halal dan kunya, banji daÉ—in wannan lamari ba, dama ba a É—aura ba sai a fasa amma aikin gama ya riga da ya gama.
Cewar baba cike da ɓacin rai, Yaya Junaid ya miƙe a fusace ya fita zuwa ɗakin Najwa, yadda ta ganshi a fusace tasan dalili sai ta miƙe tana kallonsa yace cikin tsawa.
Muje É—akin inna za muyi magana.
Yaya lafiya naga fuskarka a É—aure, ko ba a faura auren bane?
Ikram ina Sameeha?
Tana cikin gida tana aiki kasanta ko na kirata ba lallai tazo ba.
Ki shiga ki kirata tazo mu tafi gida.
Saboda me? Meya faru yaya?
Hmmm Zaidu yayi ajiyar zuciya yana girgiza kai saboda ɓacin rai, yace cikin takaici.
Kinsan wai Aminu mijin Sameeha shine ya auri Najwa, ko baku ji sanarwa bane.
Mun ji mana ance Muhammad Al'amin, amma ai bamu gane shi bane, kutumelesi Najwa ta iya cin amana ta rasa wanda zata aura sai Aminu.
Ta faɗa cike da ɓacin rai ta juya a fusace tayi cikin gida a guje, tana faɗawa tayi sa'a Najwa tana tsakar gida da kawayenta suna hotuna, Ikram bata yi wata wata ba ta isa gabanta ta sharara mata mari tare shaƙo wuyanta ta maƙureta ta kaita ƙasa ta shiga dukanta kamar Allah ya aikota, ƙarfinsu bazai zo ɗaya ba saboda Ikram Aljanunta ne suka tashi suke hukunci, nan fa gida ya hautsine aka shiga ƙoƙarin kwatar Najwa amma ina Ikram ta hau ruwan cikinta tana dukanta iya ƙarfinta, nan fa aka fita aka kira maza wanda Zaidu yana ganin haka ya nufo gidan da gudu ya shigo, ga Sameeha ta yi kokarin kama hannun Ikram amma ina ƙarfinsu ba ɗaya ba, Ihu kawai Najwa take saki tana aceceta zata kasheta, da kyar Zaidu ya kama Ikram ta baya ya matse hannyenta da jikinta iya ƙarfinsa ya shiga tofa mata addu'a, yayan Najwa Junaid shima ya saka ƙarfi ya taimakawa Zaidu suka ɗaga Ikram daga cikin Najwa, Najwa kuwa marayan kuka ta saki ga bakinta ya fashe yana jini fuska tayi jajir dan wahala, a haka su Zaidu suka fitar da Ikram da kyar suka saka a motarsa ya rufe ta ta waje, ya koma cikin gidan ya samu ana gogewa Najwa fuska ya kalleta cikin jajayen idonsa ya koma da kallonsa gurin Sameeha yace cikin fusata.
Ina umma, je ki kirata mubar gidan nan yanzu.
Yaya meye haka? Dan Allah ka tafi sannan umma.
Bata rufe baki ba ya daga hannu zai kwasa mata mari saboda haushin musun data tsaya yi masa, sai ya riƙe hannunsa tunawa da wani abu da yayi ya kalleta rai ɓace a mugun fusace.
Dan ubanki ki tattaro yaranki kizo mu wuce, Umma Umma kina ina.
Gani nan Zaidu wai lafiya kake abu kamar wanda ya sha kwaya, Ikram ta gama nata kaima zaka É—aura.
Haba Zaidu in rai ya ɓaci bai kamata hankali ya gushe ba, kayi haƙuri ka faɗa mana me ya faru, ina kuma ka kai Ikram.
Cewar Innar Najwa, Zaidu ya danƙara mata wani mummunar kallo yace cikin ɓacin rai.
Dole zaki faÉ—i haka mana tunda burunku ya cika kin aurawa Najwa Aminu mijin Sameeha daya saka, sai yanzu ma kwakwalwata suke haÉ—o mini abubuwa akan 'yarki Najwa mara godiyar Allah rashin kunya da tarbiyya.
Ya faɗa yana zuba guntun murmushi, Umma ce ta matso ta wanke shi da mari akan rashin kunyar da yayi wa Inna, duk da taji maganar Najwa ta auri Aminu ya daki zuciyarta amma haka ta danne, Sameeha kuwa tun sa'ilin daya faɗa ta wuce suf suf ta fice daga gidan, Zaidu ya kalli umma yana son yin magana ta daka masa tsawa akan ya fita tare da nuna masa hanyar fita, bai ce komai ba ya fice ransa a matuƙar ɓace, Inna kuwa mutuwar tsaye tayi tana jin abinda yafi ƙarfin kunnen ta, Umma kuwa ɗakin Inna ta shiga ta ɗauko hijab ta saka bata cewa kowa komai ba ta fito daga gidan, ta samesu a wajen motar Zaidu, tace.
BuÉ—e motar mu wuce anjima zai kazo ka É—auki motar Sameeha.
Ba musu ya buɗe motar umma da Sameeha suka zauna gidan baya suka saka Ikram a tsakiya da taketa kukan baƙin ciki, Anwar dasu Abi suka shiga gaban mota sai Zaidu ya zauna mazaunin driver ya tada mota suka nufi gida.
_Hmmm an zo gurin..._
[4/27, 8:45 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
42.
Inna kuwa bayan mutuwar tsaye da ta yi numfashinta ne ya soma barazanar barin jikinta wanda nan take ta nima yanke jiki ta faÉ—i amma mutane suka tarota, suka kaita zuwa É—akinta suka kwantar a gado tana mayar da numfashi da Æ™arfi tare da zufa daya rufeta, sai sannu 'yan uwa suke jera mata idonta a rufe. Æangaren Najwa kuwa Nafeesa ce ta taimaka mata ta tashi tare da wata Æ™awarsu, sai suka shiga kakkaÉ“e mata jiki kuka kawai take yi tana alwashin sai ta rama abinda Ikram tayi mata, ko kaÉ—an bata yi dana sanin dan sun san Aminu ta aura ba, ita taso ma ba a lokacin suka sani ba sai in an kaita suga gidan Sameeha ne ya zama mallakinta, duk da tana jin mutanen cikin gidan suna surutunta amma bai dame ta ba dan tasan watan maganar ne ya tsaya, da É—ingishi ta shiga É—akinta ta zauna bakin gado tana shafa gashinta daya yi kura, dan tuni É—ankwalin da aka É—aura mata yayi nashi wajen, a lokacin ne ta buÆ™aci wayarta domin ta kira 'yan daban da suka taÉ“a yiwa Jamila duka ta sakasu su je su rama mata abinda Ikram tayi mata, sai ta kalli Nafeesa tana cewa.
Ina wayata.?
Kin manta wayar tana hannunki da kuka soma kokawa, tuni kuka bi ta kanta taci screen, ko haske bata yi duk ta fashe tayi baƙi.
Wlh Ikram taci bashi yadda ta dukeni sai jikinta ya gaya mata, kuma wlh sai na saka tayi asara kamar yadda nima nayi asarar wayata.
Ta faÉ—a tana girgiza kai, Nafeesa ta isa gefenta ta zauna ta dafa kafaÉ—arta.
Najwa an riga an ɗaura aurenki ya kamata ki gane yanzu rigima ba naki bane, ki barta da Allah ki fuskanci ƙalubalen dake gabanki tunda su inna sun san mijin Sameeha kika aure, sai ki tanadi maganar da zaki kare kanki.
Nafeesa dan sun sani sai me, an dai riga an É—aura ni banda damuwa da su domin dai nayi nasara da aurensa, ni yanzu in har ban rama abinda Ikram tayi mini ba ban cika sunana ba wlh.
To shikenan Nafeesa tace ta koma gefe tana zuba abinci dan dama zasu ci ne suka fita waje yin hoto in sun gama su dawo su ci, Najwa sai kumbure kumbure take tana girgiza kai, ta cire sim ɗinta ta ce Nafeesa ta saka mata a wayarta saboda kar a kirata aji ba'a samu tunda akwai ƙawayenta da basu san gidansu ba, ba musu ta cire ɗayan layinta da bata cika amfani dashi ba ta saka ajaka kana ta sakawa Najwa nata sim ɗin.
Baba ne da yayyin Najwa su uku suka shigo gidan, basu zame ko ina ba sai ɗakin inna, sun samu ta dawo hayyacinta tana zaune gefen gado sai dai har lokacin gumi take yi da alama in aka gwada jininta a lokacin to ya hau, ganin sun shigo yasa mutanen ɗakin suka fita baba ya samu gefe ya tsaya yana dubanta yaran kuma duk zama suka yi a ƙasa, baba yace cikin kulawa.
Sannu Zulai ya jikin?
Da sauki Alhamdulillahi, kaina ne ke sara mini kamar zai rabe.
Allah ya sauke ya baki lafiya. Wai abinda naji da gaske ne akan Najwa mijin Sameeha ta aura, yanzu Junaid ya sameni da maganar wai har aljanun Ikram sun tashi sun yi faÉ—a da Najwa.
Wlh malam nima a bakin Zaidu muka ji maganar tunda kasan shi yasan mijin 'yar uwarsa, sannan da shi aka daura aure, abinda ya bani mamaki da tsoro taya duk aka amsa musu bamu gane komai dan gane da haka ba, Najwa dai nasan ta san komai da haÉ—in bakinta da shi mijin Sameeha suka shirya komai, kuma 'yan uwansa sun san ita ce shiyasa suka ki bari aje kai kaya ashe da walakin goro a miya, hatta kayan lefe maza suka kawo dan kar mata su kawo a gane 'yan uwansa ne dan duk mun sansu.
Amma wannan yarinya ta haÉ—a gurmi, da wani ido zamu kalli Halima, ai ana barin halal dan kunya, banji daÉ—in wannan lamari ba, dama ba a É—aura ba sai a fasa amma aikin gama ya riga da ya gama.
Cewar baba cike da ɓacin rai, Yaya Junaid ya miƙe a fusace ya fita zuwa ɗakin Najwa, yadda ta ganshi a fusace tasan dalili sai ta miƙe tana kallonsa yace cikin tsawa.
Muje É—akin inna za muyi magana.