Sashe 76
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sameeha kiyi haƙuri ba na dawo da maganar nan bane domin na tona miki asiri kona tozartaki ba, saboda ina so na ɗaura maganar akan yadda kowa zai fahimta. Ina son Sameeha amma haka na haƙura da ita badan na kamata da waɗannan 'yan matan ba sai dan na kuɓutar da ita daga faɗawa halaka, akan ta samu damar auren mai lafiya wanda zata tsira da mutuncinta dana yaranmu, wanda daga ni sai ita sai kuma in ta faɗawa su umma sune suka san da wannan maganar, dan ko 'yan uwana babu wanda yasan da maganar dan ban faɗa musu dalilin rabuwarmu ba sannan basu san bani da lafiya ba. A bayan rabuwarmu ne Hauwa ta matsa mini da zancen sai nayi aure, hakan yasa nace ta samo mini mata domin na samu hanyar da zan ƙuntata mata na rama duk wani abu da suka yiwa Sameeha nima suka yi mini, ita kuma bata san da wannan kuɗurin na amsa mata da auren ba, sai tace ta samo mini mata Najwa, wallahi Tallahi ban san wannan Najwan bace dan ban taɓa kawota a raina ba domin ban ma wayeta sosai ba dan haɗuwarmu da ita baifi sau biyu ba a gidanmu lokacin Samewha tana nan, haka ta haɗamu a waya muka cigaba da magana bamu taɓa haɗuwa ba sai jiya da aka ɗaura aurenmu har nasan wacece Hauwa ta aura mini, sai a lokacin ne na tuna irin kallon da Zaidu kayi mini ashe na tuhuma ce wanda ni ban fahimci haka ba. Najwa da Hauwa bansan a ina suka haɗu ba har suka haɗa kai wajen ganin sun cutar da Sameeha sun ƙuntata mata, ko da yake wannan ba shine abin mamakin ba dan nasan halin Hauwa zata iya aikata komai wajen ganin ta jawo Najwa a jikinta, sai dai kuma ita Hauwa tana nata Najwa ma tana nata haɗa tuggun.
Kamar ya fa? ka warware mana maganar nan kai tsaye yadda zamu fahimta.
Cewar Zaidu da duk ya ƙosa yaji ƙarshen maganar, Aminu ya yi guntun murmushin takaici ya girgiza kai yana cewa.
Sameeha wannan lesbian dana kamaki da 'yan mata, ashe ba kowa ya haɗa wannan makircin ba sai Najwa da ƙawarta Nafeesa.
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un
Duk suka haɗa baki wajen faɗa, Sameeha kuwa har da dafe ƙirji tana kallon Najwa dake rufe da gyale jikinta yana mugun rawa, Ikram tace da ƙarfi.
Anzo wajen, yau dai Allah ya bayyana gaskiya kowa yasan wacece ke Najwa, Allah ya tsine miki albarka ya wadaranki.
Karna sake jin maganarki Ikram.
Cewar Umma data waigo tana gargaɗinta da nuna mata yatsa, Baba kuwa cire hular kansa yayi yana jin wani zafi yana hura shi, inna ma sosai ta soma gumi dan gashi nan akan fuskarta tayi matuƙar girgiza da wannan labari, Junaid ko girgiza kai kawai yake cike da ta'ajibi, Yaya Zaidu kam murmushin takaici yake saki yana cije gefen leɓensa zuciyarsa tana harbawa da sauri. Aminu ya cigaba da basu labarin bayan kawo Najwa da aka yi jiya da kuma hirarsu daya ji na faɗa ita da Nafeesa, babu abinda ya ɓoye duk wanda bai manta ba ya faɗa, ya ɗaura da cewa.
Ga najwa nan a gabanku ku ji tabbaci idan sharri nayi mata, sannan ma akwai CCTV ɗin falona daya yi recoding komai, kuma akwai ƙawarta Nafeesa da zan iya kiranta yanzu tazo domin ta ƙara gasgata wannan labari. Sannan a hanyarmu ta zuwa saura kaɗan motar Tifa tabi ta kanmu Najwa data kama sitiyarin mota akan gwara ta kashemu dana tona mata asiri, idan muka fita zaku ga layin da motar tifar ya gogi gefen motata. Wannan dalilin yasa na buƙaci mu haɗu anan domin na bayyana komai na kuma wanke Sameeha akan sharrin da suka yi mata, yadda na godewa Allah maganar babu wanda yasanta sai mu nan kawai a yanzu. Amma Najwa ita ce ta aikata komai sannan ita tasan yadda ta haɗu da Hauwa har ta zaɓa mini ita a matsayin mata.
Salati kawai suke yi Inna kuwa ta kasa daurewa sai kuka take yi, Baba kam girgiza kai yake yi Yaya Junaid ya kalleta cike da takaici.
Kinyi asara Najwa ki rasa wacce zaki cuta sai Sameeha 'yar uwarki ta jini saboda son zuciyarki, babu mai mugun halinki a gidanmu bansan a ina kika samo shi ba, gaki da Ilimi amma sam baki yi aiki da shi ba Allah ya shiryeki.
Najwa kuka mai sauri ta fashe dashi dan tuni ma ta saki fitsarin daya matseta a gurin, ga gumi data ke fitarta na rashin gaskiya, tunda take bata taɓa jin ta muzanta ba a duniya irin yau, Sameeha ce ta jefa mata magana wanda yasa ta ɗago da sauri da take cewa.
Najwa me na tare miki a rayuwa dana cancanci irin wannan hukuncin a gareki? meye ribarki idan kin yi mini sharri an sakeni, ashe dama duk zuwan da kike yi kina gane mini sirrin gidana ne kina son ki auri mijina, nayi zaton Jamila 'yar aikina itace abin tsoro da nake takatsantsan da ita ashe kece abin tsoro ban sani ba.
Itama Jamila ai wu Hauwa suka turota domin ta riƙa faɗa musu duk halin da kike ciki, sannan Jamila da ita aka haɗa duk wani makirci, kuma Hauwa itace shugaban haɗa komai.
Najwa ta faÉ—a cikin kuka, Junaid ne ya wanka mata mari yana nunata da yatsa.
Saboda baki da kunya har kin samu damar yin magana ko, 'yar iskan yarinya mai mugun hali, wlh Najwa saina karyaki kinyi jinya, sheÉ—aniya mara imani da tausayi.
Najwa miƙewa tayi jikinta yana yararin fitsari tana kuka da ƙarfi dafe da kuncinta.
Yaya karka barni da rai ka kashe ni ku huta dama nasan ba ƙaunata kuke yi ba, da wanne zanji kowa ya tsaneni ya ɗaura mini laifi bayan ba ni kaɗai na aikata komai ba. Laifi ne dan naso mijinta? laifine dan na aureshi? ai ko a musulunci banyi haramci ba tunda ba da iskanci na yi ba, laifine dan na zaɓawa kaina auren mijin dana san zan huta a gidansa fiye da gidanmu, shikenan komai na ɗaukaka sai dai a ganshi a gunsu nice a baya.
Ai dolw ki ganki a baya tunda kin saka hassada da mugunta a zuciyarki, wlh Najwa kin bamu mamaki babu wanda zaiyi tunanin zaki aikata mana haka, to Alhamdulillahi kin rabata da gidan Aminu gashi ta samu kanta a gidan daya fi nashi ɗaukaka da komai, idan kina yi musu hassada to taki kike ƙara musu na daukaka, kuma ba dasu kike faɗar ba da Allah kike yi shiyasa ya nuna miki ikonsa, kaɗan ma kika gani.
Cewar Zaidu yana nunata da tsaya, Najwa taja guntun tsaki tana yatsine fuska.
Kai dai kaji haushi ne saboda nace bana sonka, kuma bana sonka É—in domin ba kada komai da zaka bani, dan a jikin Sameeha kake samun na kashewa, Allah ya kyauta.
Ke banason shashanci kinyi laifi amma kina da bakin da zaki yi magana, kaji min 'yar banza mara mutunci, zaki zauna ko sai na saka junaid yayi miki mugun duka da sai kinyi jinya dan mu huce takaicinmu.
Cewar baba cike da ɗaure fuska, Najwa ta koma ta zauna tana gunguni, itafa har yanzu ta ƙi karɓan laifinta shiyasa take zuba borin kunya, ta kuma nuna musu ba tada kunyar. Sameeha kam shuru tayi dasu umma dan abin nata yafi ƙarfin lissafinsu, Baba yace sai Najwa ta bawa Sameeha Haƙuri akan abinda tayi mata, Najwa tayi shiru taƙi magana, baba zai fara faɗa Umma ta dakatar dashi akan.
Malam ka rabu da ita har yanzu babu alamar nadama a tare da ita, dan haka ita Sameeha ko ta yafe ko bata yafe ba ta ga kyakkyawar sakamako kuma bata ma gama ganin Nasara ba In Sha Allah, Addu'a za mu taru mu yiwa Najwa akan Allah ya shirye ta, dan tuntuni na fahimci ta sauka daga tarbiyyar da kuka bata, sai kun saka ido sosai akan abokan da take hulÉ—a dasu.
Baba girgiza kai kawai yake yi yana cewa.
Dan Allah Halima kuyi haƙuri an cutar daku Allah ya saka muku, Aminu in ka gama magana mu zamu tafi.
Aminu ya gyara zama yana ciro farar takarda a haljiunsa ya aje a gaban Najwa yana cewa.
Ni Aminu na saki Najwa saki biyu ban ɗaura mata idda ba in ta samu muji tayi aure, sannan kuma na bada damar aje a kwashe kayanta a cikin makon nan dan zan rufe gidan na koma bakin aikina. Baba kuyi haƙuri akan hukuncin dana yanke domin koda Najwa bata yiwa Sameeha sharri ba bazan iya zaman aure da ita ba tana a matsayin 'yar uwarta, sannan ma ni bani da lafiyar da zan zauna da wata mace a yanzu. Sameeha ki yafe mini nasan na shiga hakkinki keda yara dana rabaku, dan haka a yanzu na yanke hukuncin yara sun dawo hannunki idan mijinki ya amince zai zauna dasu to ba damuwa, in kuma bai yarda ba ki barsu a gurin Umma nasan zasu samu tarbiyya mai kyau da kulawa, sannan zan riƙa biya musu kuɗin makaranta da duk wani hakkinsu dake kaina ban yarda kowa yayi ba, ina tunanin a cikin wata mai kamawa zan bar ƙasar nan zanje London yin wani aiki na shekara biyu In Sha Allah zan riƙa kira ina waya dasu Abi, umma ni zan tafi na barku lafiya ku yafe mini.
Allah ya yafe mana gabaÉ—aya kuma Baka mana komai ba Aminu, Allah yasa albarka a cikin tafiyarka ya baka nasara da lafiya mai inganci.
Kamar ya fa? ka warware mana maganar nan kai tsaye yadda zamu fahimta.
Cewar Zaidu da duk ya ƙosa yaji ƙarshen maganar, Aminu ya yi guntun murmushin takaici ya girgiza kai yana cewa.
Sameeha wannan lesbian dana kamaki da 'yan mata, ashe ba kowa ya haɗa wannan makircin ba sai Najwa da ƙawarta Nafeesa.
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un
Duk suka haɗa baki wajen faɗa, Sameeha kuwa har da dafe ƙirji tana kallon Najwa dake rufe da gyale jikinta yana mugun rawa, Ikram tace da ƙarfi.
Anzo wajen, yau dai Allah ya bayyana gaskiya kowa yasan wacece ke Najwa, Allah ya tsine miki albarka ya wadaranki.
Karna sake jin maganarki Ikram.
Cewar Umma data waigo tana gargaɗinta da nuna mata yatsa, Baba kuwa cire hular kansa yayi yana jin wani zafi yana hura shi, inna ma sosai ta soma gumi dan gashi nan akan fuskarta tayi matuƙar girgiza da wannan labari, Junaid ko girgiza kai kawai yake cike da ta'ajibi, Yaya Zaidu kam murmushin takaici yake saki yana cije gefen leɓensa zuciyarsa tana harbawa da sauri. Aminu ya cigaba da basu labarin bayan kawo Najwa da aka yi jiya da kuma hirarsu daya ji na faɗa ita da Nafeesa, babu abinda ya ɓoye duk wanda bai manta ba ya faɗa, ya ɗaura da cewa.
Ga najwa nan a gabanku ku ji tabbaci idan sharri nayi mata, sannan ma akwai CCTV ɗin falona daya yi recoding komai, kuma akwai ƙawarta Nafeesa da zan iya kiranta yanzu tazo domin ta ƙara gasgata wannan labari. Sannan a hanyarmu ta zuwa saura kaɗan motar Tifa tabi ta kanmu Najwa data kama sitiyarin mota akan gwara ta kashemu dana tona mata asiri, idan muka fita zaku ga layin da motar tifar ya gogi gefen motata. Wannan dalilin yasa na buƙaci mu haɗu anan domin na bayyana komai na kuma wanke Sameeha akan sharrin da suka yi mata, yadda na godewa Allah maganar babu wanda yasanta sai mu nan kawai a yanzu. Amma Najwa ita ce ta aikata komai sannan ita tasan yadda ta haɗu da Hauwa har ta zaɓa mini ita a matsayin mata.
Salati kawai suke yi Inna kuwa ta kasa daurewa sai kuka take yi, Baba kam girgiza kai yake yi Yaya Junaid ya kalleta cike da takaici.
Kinyi asara Najwa ki rasa wacce zaki cuta sai Sameeha 'yar uwarki ta jini saboda son zuciyarki, babu mai mugun halinki a gidanmu bansan a ina kika samo shi ba, gaki da Ilimi amma sam baki yi aiki da shi ba Allah ya shiryeki.
Najwa kuka mai sauri ta fashe dashi dan tuni ma ta saki fitsarin daya matseta a gurin, ga gumi data ke fitarta na rashin gaskiya, tunda take bata taɓa jin ta muzanta ba a duniya irin yau, Sameeha ce ta jefa mata magana wanda yasa ta ɗago da sauri da take cewa.
Najwa me na tare miki a rayuwa dana cancanci irin wannan hukuncin a gareki? meye ribarki idan kin yi mini sharri an sakeni, ashe dama duk zuwan da kike yi kina gane mini sirrin gidana ne kina son ki auri mijina, nayi zaton Jamila 'yar aikina itace abin tsoro da nake takatsantsan da ita ashe kece abin tsoro ban sani ba.
Itama Jamila ai wu Hauwa suka turota domin ta riƙa faɗa musu duk halin da kike ciki, sannan Jamila da ita aka haɗa duk wani makirci, kuma Hauwa itace shugaban haɗa komai.
Najwa ta faÉ—a cikin kuka, Junaid ne ya wanka mata mari yana nunata da yatsa.
Saboda baki da kunya har kin samu damar yin magana ko, 'yar iskan yarinya mai mugun hali, wlh Najwa saina karyaki kinyi jinya, sheÉ—aniya mara imani da tausayi.
Najwa miƙewa tayi jikinta yana yararin fitsari tana kuka da ƙarfi dafe da kuncinta.
Yaya karka barni da rai ka kashe ni ku huta dama nasan ba ƙaunata kuke yi ba, da wanne zanji kowa ya tsaneni ya ɗaura mini laifi bayan ba ni kaɗai na aikata komai ba. Laifi ne dan naso mijinta? laifine dan na aureshi? ai ko a musulunci banyi haramci ba tunda ba da iskanci na yi ba, laifine dan na zaɓawa kaina auren mijin dana san zan huta a gidansa fiye da gidanmu, shikenan komai na ɗaukaka sai dai a ganshi a gunsu nice a baya.
Ai dolw ki ganki a baya tunda kin saka hassada da mugunta a zuciyarki, wlh Najwa kin bamu mamaki babu wanda zaiyi tunanin zaki aikata mana haka, to Alhamdulillahi kin rabata da gidan Aminu gashi ta samu kanta a gidan daya fi nashi ɗaukaka da komai, idan kina yi musu hassada to taki kike ƙara musu na daukaka, kuma ba dasu kike faɗar ba da Allah kike yi shiyasa ya nuna miki ikonsa, kaɗan ma kika gani.
Cewar Zaidu yana nunata da tsaya, Najwa taja guntun tsaki tana yatsine fuska.
Kai dai kaji haushi ne saboda nace bana sonka, kuma bana sonka É—in domin ba kada komai da zaka bani, dan a jikin Sameeha kake samun na kashewa, Allah ya kyauta.
Ke banason shashanci kinyi laifi amma kina da bakin da zaki yi magana, kaji min 'yar banza mara mutunci, zaki zauna ko sai na saka junaid yayi miki mugun duka da sai kinyi jinya dan mu huce takaicinmu.
Cewar baba cike da ɗaure fuska, Najwa ta koma ta zauna tana gunguni, itafa har yanzu ta ƙi karɓan laifinta shiyasa take zuba borin kunya, ta kuma nuna musu ba tada kunyar. Sameeha kam shuru tayi dasu umma dan abin nata yafi ƙarfin lissafinsu, Baba yace sai Najwa ta bawa Sameeha Haƙuri akan abinda tayi mata, Najwa tayi shiru taƙi magana, baba zai fara faɗa Umma ta dakatar dashi akan.
Malam ka rabu da ita har yanzu babu alamar nadama a tare da ita, dan haka ita Sameeha ko ta yafe ko bata yafe ba ta ga kyakkyawar sakamako kuma bata ma gama ganin Nasara ba In Sha Allah, Addu'a za mu taru mu yiwa Najwa akan Allah ya shirye ta, dan tuntuni na fahimci ta sauka daga tarbiyyar da kuka bata, sai kun saka ido sosai akan abokan da take hulÉ—a dasu.
Baba girgiza kai kawai yake yi yana cewa.
Dan Allah Halima kuyi haƙuri an cutar daku Allah ya saka muku, Aminu in ka gama magana mu zamu tafi.
Aminu ya gyara zama yana ciro farar takarda a haljiunsa ya aje a gaban Najwa yana cewa.
Ni Aminu na saki Najwa saki biyu ban ɗaura mata idda ba in ta samu muji tayi aure, sannan kuma na bada damar aje a kwashe kayanta a cikin makon nan dan zan rufe gidan na koma bakin aikina. Baba kuyi haƙuri akan hukuncin dana yanke domin koda Najwa bata yiwa Sameeha sharri ba bazan iya zaman aure da ita ba tana a matsayin 'yar uwarta, sannan ma ni bani da lafiyar da zan zauna da wata mace a yanzu. Sameeha ki yafe mini nasan na shiga hakkinki keda yara dana rabaku, dan haka a yanzu na yanke hukuncin yara sun dawo hannunki idan mijinki ya amince zai zauna dasu to ba damuwa, in kuma bai yarda ba ki barsu a gurin Umma nasan zasu samu tarbiyya mai kyau da kulawa, sannan zan riƙa biya musu kuɗin makaranta da duk wani hakkinsu dake kaina ban yarda kowa yayi ba, ina tunanin a cikin wata mai kamawa zan bar ƙasar nan zanje London yin wani aiki na shekara biyu In Sha Allah zan riƙa kira ina waya dasu Abi, umma ni zan tafi na barku lafiya ku yafe mini.
Allah ya yafe mana gabaÉ—aya kuma Baka mana komai ba Aminu, Allah yasa albarka a cikin tafiyarka ya baka nasara da lafiya mai inganci.