Sashe 82
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aminu tunda ya bar gidan ya wuce gidansa sai da ya ɗauki kusan awa biyu a kwance a ɗakinsa, kiran sallar ya tashe shi ya gabar kana ya koma ya kwanta ko yunwa baya ji. A ranar dai baiyi barcin kirki ba domin kuwa ga yunwa ga kuma damuwa. Da safe da wuri ya shirya ya fita ta siyowa kansa abin kari yaci ya ƙoshi yana shirin sake fita sai gasu yaya Alhasan sun zo shi da Kamalu, da suka zauna suka gaisa kana suka jajanta masa abinda ya faru tare da bashi haƙuri akan ya yafewa Hauwa, Aminu ya nuna musu babu komai kuma komai ya wuce nan ya sanar dasu tafiyarsa London da zaiyi na shekara biyu, ya kuma faɗa musu yana so Baba Hansatu zata dawo nan babban gida ta zauna suna kula da ita kafin Allah yayi masa dawowa, suka yi masa murna da fatan alkhairi tare da tabbatar masa da zasu riƙe Baba a hannunsu, nan ya bar musu amanar gidansa su kula masa da shi har da yawo, ya kuma basu maƙudan kuɗi su raba da kuma kuɗin da zasu yi wa Salma gara in ta haihu, ya kuma sanar dasu hukuncin daya yanke akan yaransa na ya barsu a hannun Sameeha, sun ji daɗin haka kuma sun goyi da bayan duk hukuncin daya yanke, daga bisani suka yi hira sosai kana suka tafi ya rakasu har zuwa babban gida daga can ya wuce Zaria.
A ranar su Junaid suka zo da mota suka kwashe kayan Najwa, dama Aminu ya bar key ɗin gidan a hannun me gadi, tas suka gama kwashe komai suka rufe gidan tare da mayar da key ɗin a hannun me gadi suka wuce. A ɗakin Najwa suka zuba kayan tunda bata nan sai suka rufe ɗakin gabaɗaya, a lokacin ne kiran Saleema ya shigo wayar Baba yaƙi ɗauka.
******
Kano.
Tunda Saleema ta dawo sashinta sai ta shiga ɗakinta ta zauna bakin gado tana cike da damuwa kamar zata fasa kuka dan baƙin ciki, tunawa da tayi da Baban Najwa yasa ta fito ta amsa wayarta a hannun Najwa ta koma ɗaki ta kirashi, koda ya ɗauka ta zayyano masa duk abinda Mijinta ya ce da Najwa ba zata zauna masa a gida ba sai ta ɗaura da cewa.
Dan Allah yaya ka kirashi kayi masa bayanin abinda ya faru nasan in ka saka baki zai bari ta zauna da mu.
Hmmm Saleema kenan, kin ga tun kafin aje ko ina kin fara ganin sakamakon É—aukar Najwa, yarinyar nan amanar zumunci taci shiyasa ba zata ga dai dai tunda har yanzu bata yi nadama ba, dan haka babu abinda zan ce masa bazan hana shi yanke hukunci a gidansa ba, ke da kika ji zaki iya da ita ki san inda zaki kaita.
Haba yaya ya zaka ce haka...
Bata gama magana ba ya kashe wayarsa, Saleema takaici ya cikata da tunanin mafita, tana zaune a wannan yanayin ga yunwa daya dameta sai ga Malam ya shigo sashinta Allah yasa baiga Najwa a falonta ba ya wuce bedroom ɗinta ya sameta ta rafka tagumi, tana ganinsa ta miƙe tsaye a tsorace fuskarsa kamar zata fashe da kuka.
Me kike jira da baki sallameta ba?
Saleema samun kanta tayi da tsuguna masa akan guiwarta ta fashe da kuka tana cewa.
Don Allah kayi haƙuri malam ka duba zumunci ka barta ta zauna, yarinyar Yayanmu ne na Kaduna wacce aka yi bikinta jiya mijinta ya saketa a yau saboda baida lafiyar da zai kusanceta, ya ɓoye mana haka sai da aka yi biki muka sani yau daya sakota dan cewa tayi ba zata zauna da shi, yanzu ma na gama waya da yaya akan ya kiraka ya baka haƙuri yace bazai kira ba ba zai hanaka yanke hukuncin gidanka ba.
Saleema ta samu kanta da shimfiɗa ƙarya akan labarin Najwa, Malam ya sauke ajiyar zuciya yace ta tashi ta zauna gefen gado, Saleema ta miƙe da sauri ta zauna, shima zama yayi kusa da ita yana cewa.
Ni bawai na nuna ba zata zauna bane saboda na muzguna miki ba, kawai ina so na nuna miki ina da muhimmanci a gareki domin ki riƙa sanar dani duk abinda ya zama wajibi na sani, kinga da kin sanar dani komai a waya da babu yadda za ayi nace ba zata zauna ba, dan haka babu damuwa ta zauna damu Allah yasa hakan ya zama mata alkhairi ya zaɓa mata miji nagari, sai dai kinsan ina da sharuɗɗa, ki sanar da ita bana son yawo sannan ta zauna a nan ɓangaren karna ganta a farfajiya, idan ta samu natsuwa zan duba me ya dace da ita ko makaranta ko kuma auren.
Nagode Malam Allah ya saka da alkhairi amma ni nafi son tayi wani auren dan mu bawa maƙiya kunya masu yi mana dariya.
Ba dan Allah kike so tayi auren ba kenan, karma ki saka hakan a ranki ki taya ta da addu'ar mafi alkhairi a gareta. Duk abinda take so ta sanar dake ki faɗa mini Allah ya taya mu riƙo.
Saleema ta amsa da amin kana ta yi masa godiya sai ya tashi ya fita itama ta bi bayansa har sai da yabar sashinta kafin ta dawo cikin falon tana kwalawa Najwa kira, data fito daga É—akin yaranta ta zauna sai Saleema ta sanar da ita amincewar da malam yayi ta zauna a gidan, Najwa taji daÉ—i sosai domin ga dukkan alamu zata shimfiÉ—a duk abinda take so a gidan tunda suma masu kuÉ—i ne ba laifi gida ne me kyau, sai dai data sanar da ita baya son yawo tace ba damuwa amma a ranta tana cewa bata ga wanda zai hanata yin abinda take so ba. A ranar Najwa ta samu barcin da ta jima bata yi ba domin tuni ta watsar da damuwa ta fara tunanin yadda zata kafa sabuwar rayuwa, duk da haushin Aminu dasu Sameeha yana manne a zuciyarta.
Washe gari ne bayan sun karya sai Saleema ta tasa ƙeyar Najwa zuwa ɓangaren malam domin ta gaishe shi, koda suka shiga sun same shi da baƙi maza biyu nan suka gaisa Saleema ta gabatar masa da Najwa yace.
Baƙuwa da fatan zaki zauna damu da zuciya ɗaya, bana son yawo bana son na riƙa ganinki a farfajiya in ba kwakkwaran dalili ba, sannan ban yarda da bin shashin matana ba saboda bana son rikici.
Najwa tace to amma a zuciyarta tana mamakin rashin karan da Malam ya nuna mata ƙarara, haka suka bar falon Saleema jikinta a sanyaye dan taji kunyar maganganun malam ga Najwa, suna fita Saleema ta kira Yaya domin ta sanar dashi malam ya yarda da zaman Najwa sai dai harya ringing bai ɗauka ba, da suka isa sashinsu ne ta kuma kira shine ya ɗauka take sanar dashi komai yace ba damuwa kana ya sanar da ita an kwaso kayan Najwa ɗazun.
[5/8, 8:11 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
49.
Su Saleema suna fita daga falon malam, sai É—aya daga cikin mutanen dake falon yace cikin sosa kai.
Malam in ba damuwa ina da magana akan wancen yarinyar da suka fita yanzu, amma Allah yasa ba matar aure bace.
Malam sai da yayi 'yar dariya kafin yace.
Ina jinka Atiku faÉ—i maganarka kai tsaye.
Yauwa dama ina kamun iri ne idan ba matar wani bace, zan ƙara ta biyu da ita.
Atiku manya daga ganinta sai kaji kana son ƙara aure anya kuwa?.
Dama ina son na ƙara to har yanzu ban samu bane shiyasa, to yanzu ne na ga wacce ta dace dani dan sosai ta kwanta mini a zuciyata.
To madallah kuma kayi rasa akan gaɓa domin kuwa ba tada aure sakin wawane ko nace auren rana guda ne da yini aka sauta, saboda mijin baida lafiya ya ɓoye musu gaskiya, ko idda bai ɗaura mata ba.
Alhamdulillah gaskiya nayi farin ciki, ni dama nasan zuwa na nan alkhairi ne, ga cigaba na kasuwanci da nake samu bisa tallafin addu'o'inka gashi kuma zan samu mata. Allah yasa na samu karɓuwa a gunta.
In dai wannan ne zata soka dan bata isa in kawo miji ta ce bata so ba, tuni zan yi maganinta, in dai da gaske kake to ka bar mini komai a hannuna.
Nan Atiku ya shiga jero masa godiya kamar zai kwansa masa, malam ya gama aikin da zai yi musu ya sallame su akan zasu yi magana a waya. Suna fita malam ya yi duba akan Atiku da Najwa, nan ya hango aure zai tabbata kuma shima hanyar samunsa a jikin Atiku zai ƙara buɗewa dan ba ƙaramin morarsa yake yi ba, duk abinda ya gindaya masa na kuɗi baya taɓa kaucewa sai ya bayar, hakan yasa yaji dole ma Najwa ta aureshi dan ba zai yarda ya rasa wannan gwaggwaɓar samun ba.
****
Bayan kwana.
A Kaduna.
Sameeha mijinta ya kirata akan ta shirya zasu koma Abuja a ranar saboda akwai wani taro da za ayi ranar Alhamis wato gobe In Allah ya kaimu, kuma tarone na manyan mutane da matansu, to yana so Sameeha ta kasance tare da shi a wannan guri dan yasan ita É—in matar fita taro ce, hakan yasa dole ta shirya dan dama taso ta yi sati guda ne sai ta koma, tumi Ikram ta koma gida sai dai suyi waya, hakan yasa Sameeha ta kira Aminu kan batun yara, koda ya daga wayar suka gaisa sai ta É—aura da ce masa.
Abban Amrah dama na kira ka ne kan batun su Abi, Umma tace a gunta zasu zauna, shine nace bari na sanar da kai ko za a yi musu transfer ɗin makarantarsu zuwa nan Kaduna, tunda turkish school ne kuma nan ma akwai, ko yaya Zaidu zai riƙa kaisu makarantar.
A ranar su Junaid suka zo da mota suka kwashe kayan Najwa, dama Aminu ya bar key ɗin gidan a hannun me gadi, tas suka gama kwashe komai suka rufe gidan tare da mayar da key ɗin a hannun me gadi suka wuce. A ɗakin Najwa suka zuba kayan tunda bata nan sai suka rufe ɗakin gabaɗaya, a lokacin ne kiran Saleema ya shigo wayar Baba yaƙi ɗauka.
******
Kano.
Tunda Saleema ta dawo sashinta sai ta shiga ɗakinta ta zauna bakin gado tana cike da damuwa kamar zata fasa kuka dan baƙin ciki, tunawa da tayi da Baban Najwa yasa ta fito ta amsa wayarta a hannun Najwa ta koma ɗaki ta kirashi, koda ya ɗauka ta zayyano masa duk abinda Mijinta ya ce da Najwa ba zata zauna masa a gida ba sai ta ɗaura da cewa.
Dan Allah yaya ka kirashi kayi masa bayanin abinda ya faru nasan in ka saka baki zai bari ta zauna da mu.
Hmmm Saleema kenan, kin ga tun kafin aje ko ina kin fara ganin sakamakon É—aukar Najwa, yarinyar nan amanar zumunci taci shiyasa ba zata ga dai dai tunda har yanzu bata yi nadama ba, dan haka babu abinda zan ce masa bazan hana shi yanke hukunci a gidansa ba, ke da kika ji zaki iya da ita ki san inda zaki kaita.
Haba yaya ya zaka ce haka...
Bata gama magana ba ya kashe wayarsa, Saleema takaici ya cikata da tunanin mafita, tana zaune a wannan yanayin ga yunwa daya dameta sai ga Malam ya shigo sashinta Allah yasa baiga Najwa a falonta ba ya wuce bedroom ɗinta ya sameta ta rafka tagumi, tana ganinsa ta miƙe tsaye a tsorace fuskarsa kamar zata fashe da kuka.
Me kike jira da baki sallameta ba?
Saleema samun kanta tayi da tsuguna masa akan guiwarta ta fashe da kuka tana cewa.
Don Allah kayi haƙuri malam ka duba zumunci ka barta ta zauna, yarinyar Yayanmu ne na Kaduna wacce aka yi bikinta jiya mijinta ya saketa a yau saboda baida lafiyar da zai kusanceta, ya ɓoye mana haka sai da aka yi biki muka sani yau daya sakota dan cewa tayi ba zata zauna da shi, yanzu ma na gama waya da yaya akan ya kiraka ya baka haƙuri yace bazai kira ba ba zai hanaka yanke hukuncin gidanka ba.
Saleema ta samu kanta da shimfiɗa ƙarya akan labarin Najwa, Malam ya sauke ajiyar zuciya yace ta tashi ta zauna gefen gado, Saleema ta miƙe da sauri ta zauna, shima zama yayi kusa da ita yana cewa.
Ni bawai na nuna ba zata zauna bane saboda na muzguna miki ba, kawai ina so na nuna miki ina da muhimmanci a gareki domin ki riƙa sanar dani duk abinda ya zama wajibi na sani, kinga da kin sanar dani komai a waya da babu yadda za ayi nace ba zata zauna ba, dan haka babu damuwa ta zauna damu Allah yasa hakan ya zama mata alkhairi ya zaɓa mata miji nagari, sai dai kinsan ina da sharuɗɗa, ki sanar da ita bana son yawo sannan ta zauna a nan ɓangaren karna ganta a farfajiya, idan ta samu natsuwa zan duba me ya dace da ita ko makaranta ko kuma auren.
Nagode Malam Allah ya saka da alkhairi amma ni nafi son tayi wani auren dan mu bawa maƙiya kunya masu yi mana dariya.
Ba dan Allah kike so tayi auren ba kenan, karma ki saka hakan a ranki ki taya ta da addu'ar mafi alkhairi a gareta. Duk abinda take so ta sanar dake ki faɗa mini Allah ya taya mu riƙo.
Saleema ta amsa da amin kana ta yi masa godiya sai ya tashi ya fita itama ta bi bayansa har sai da yabar sashinta kafin ta dawo cikin falon tana kwalawa Najwa kira, data fito daga É—akin yaranta ta zauna sai Saleema ta sanar da ita amincewar da malam yayi ta zauna a gidan, Najwa taji daÉ—i sosai domin ga dukkan alamu zata shimfiÉ—a duk abinda take so a gidan tunda suma masu kuÉ—i ne ba laifi gida ne me kyau, sai dai data sanar da ita baya son yawo tace ba damuwa amma a ranta tana cewa bata ga wanda zai hanata yin abinda take so ba. A ranar Najwa ta samu barcin da ta jima bata yi ba domin tuni ta watsar da damuwa ta fara tunanin yadda zata kafa sabuwar rayuwa, duk da haushin Aminu dasu Sameeha yana manne a zuciyarta.
Washe gari ne bayan sun karya sai Saleema ta tasa ƙeyar Najwa zuwa ɓangaren malam domin ta gaishe shi, koda suka shiga sun same shi da baƙi maza biyu nan suka gaisa Saleema ta gabatar masa da Najwa yace.
Baƙuwa da fatan zaki zauna damu da zuciya ɗaya, bana son yawo bana son na riƙa ganinki a farfajiya in ba kwakkwaran dalili ba, sannan ban yarda da bin shashin matana ba saboda bana son rikici.
Najwa tace to amma a zuciyarta tana mamakin rashin karan da Malam ya nuna mata ƙarara, haka suka bar falon Saleema jikinta a sanyaye dan taji kunyar maganganun malam ga Najwa, suna fita Saleema ta kira Yaya domin ta sanar dashi malam ya yarda da zaman Najwa sai dai harya ringing bai ɗauka ba, da suka isa sashinsu ne ta kuma kira shine ya ɗauka take sanar dashi komai yace ba damuwa kana ya sanar da ita an kwaso kayan Najwa ɗazun.
[5/8, 8:11 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
49.
Su Saleema suna fita daga falon malam, sai É—aya daga cikin mutanen dake falon yace cikin sosa kai.
Malam in ba damuwa ina da magana akan wancen yarinyar da suka fita yanzu, amma Allah yasa ba matar aure bace.
Malam sai da yayi 'yar dariya kafin yace.
Ina jinka Atiku faÉ—i maganarka kai tsaye.
Yauwa dama ina kamun iri ne idan ba matar wani bace, zan ƙara ta biyu da ita.
Atiku manya daga ganinta sai kaji kana son ƙara aure anya kuwa?.
Dama ina son na ƙara to har yanzu ban samu bane shiyasa, to yanzu ne na ga wacce ta dace dani dan sosai ta kwanta mini a zuciyata.
To madallah kuma kayi rasa akan gaɓa domin kuwa ba tada aure sakin wawane ko nace auren rana guda ne da yini aka sauta, saboda mijin baida lafiya ya ɓoye musu gaskiya, ko idda bai ɗaura mata ba.
Alhamdulillah gaskiya nayi farin ciki, ni dama nasan zuwa na nan alkhairi ne, ga cigaba na kasuwanci da nake samu bisa tallafin addu'o'inka gashi kuma zan samu mata. Allah yasa na samu karɓuwa a gunta.
In dai wannan ne zata soka dan bata isa in kawo miji ta ce bata so ba, tuni zan yi maganinta, in dai da gaske kake to ka bar mini komai a hannuna.
Nan Atiku ya shiga jero masa godiya kamar zai kwansa masa, malam ya gama aikin da zai yi musu ya sallame su akan zasu yi magana a waya. Suna fita malam ya yi duba akan Atiku da Najwa, nan ya hango aure zai tabbata kuma shima hanyar samunsa a jikin Atiku zai ƙara buɗewa dan ba ƙaramin morarsa yake yi ba, duk abinda ya gindaya masa na kuɗi baya taɓa kaucewa sai ya bayar, hakan yasa yaji dole ma Najwa ta aureshi dan ba zai yarda ya rasa wannan gwaggwaɓar samun ba.
****
Bayan kwana.
A Kaduna.
Sameeha mijinta ya kirata akan ta shirya zasu koma Abuja a ranar saboda akwai wani taro da za ayi ranar Alhamis wato gobe In Allah ya kaimu, kuma tarone na manyan mutane da matansu, to yana so Sameeha ta kasance tare da shi a wannan guri dan yasan ita É—in matar fita taro ce, hakan yasa dole ta shirya dan dama taso ta yi sati guda ne sai ta koma, tumi Ikram ta koma gida sai dai suyi waya, hakan yasa Sameeha ta kira Aminu kan batun yara, koda ya daga wayar suka gaisa sai ta É—aura da ce masa.
Abban Amrah dama na kira ka ne kan batun su Abi, Umma tace a gunta zasu zauna, shine nace bari na sanar da kai ko za a yi musu transfer ɗin makarantarsu zuwa nan Kaduna, tunda turkish school ne kuma nan ma akwai, ko yaya Zaidu zai riƙa kaisu makarantar.