Sashe 84
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A ranar Juma'a aka ɗaura aurensu a Masallacin jikin gidan, ba wani taro aka yi ba sai dai 'yan uwa na kusa sun zo kuma kowa yayi mamakin wannan aure na gaggawa, sun dai bayar ƙila Nafeesan taƙi fito da mijine Alhajinsu ya yanke mata wannan hukuncin, ita dai a ɗaki ta yini dan ko fita ta kasa yi nan duk 'yan uwanta suka sameta suna bata haƙuri. Zuwa bayan magrib tayi wanka ta saka wani leshi da abbansu ya siya aka ɗinka mata, kana 'yan biko suka zo aka kaita gidan mijinta. Kowa yayi mamakin gidan da aka kai Nafisa dan gidane filat mai kyau da ɗakuna a katon falo guda huɗu ko wanne da bayi kuma an zuba kayan zamani masu kyau da tsada, hatta kitchen ɗin ya tsaru, sannan ɗakin da aka kai Nafeesa sun tadda setin akwatuna guda biyu da me set huɗu da kuma me set uku, koda suka buɗe sun same ahi cike da kaya masu tsada da kyau, Nafeesa ganin wannan ba zata ya sa ta samu ɗan natauwa a zuciyarta har take jin zata zauna da Sadi tunda bata muzanta ba ta samu gida mai kyau da kayan lefe, 'yan uwa sai sam barka domin malam Sadi ya basu mamaki kuma yayi bajinta, kuma dagasken shine ya yi mata wannan kayan dan ya jima yana tara kaya a gurin yarsa akan koda ya tashi aure bazai sha wuyan haɗa akwati ba, to ganin karamcin dasu Abba suka yi masa yasa shima yace zai gwangwaje Nafeesa da kayan lefe domin ya saka alkhairin da suka yi masa. Bayan kowa ya watse abokansa suka rakoshi yazo ya kirata ta fito cikin babban mayafi ta zauna a cushing nan suka rattafo musu nasiha akan zamantakewar aure dama koyi da sunnar Ma'aiki s.a.w da kuma matansa, wanda yasa jikin Nafeesa ya kuma yin sanyi ta ƙara saduda da karɓan ƙaddararta, bayan abokansa sun gama suka yi musu sallama suka tafi. A wannan dare Sadi ya angonce wanda ko kaɗan Nafeesa bata yi masa musu ba ta bada kai bori ya hau, da Safe bayan sun natsa ya bata sabuwar waya iPhone 13 a cikin kwalinta kyauta wanda yaya Taju ne ya bashi yace ya bata domin dai ta ƙara sakin jiki dashi tayi zaman auren, Nafeesa sai da tayi kukan murna dan sosai taji daɗin wayar sai dai ya sauta mata layi, nan ta yi masa godiya Sadi ya katseta da cewa.
Nine ya dace na gode miki da kika amince da ni a matsayin mijinki baki yi mini jayayya ba ganin ni ba kowa nace almajirin gidanku.
Haba kafi ƙarfin haka a guna domin bazan taɓa gujewa zaɓin iyayena ba, kuma yanzu na tabbata ba suyi mini zaɓin banza ba. Sai dai zan nima alfarma a gunka ka bani tsohon layina dan na cire numbobin daya dace.
Layinki baya hannuna Nafeee, amma bada gmail kike saving ba.?
Wasu suna cikin wayar amma akwai wasu a gmail.
To kiyi amfani da gmail É—inki In Sha Allah zaki samu duk number din da kike so a ciki.
To tace masa kana ya miƙe yayi mata sallama ya fita, Nafeesa ta miƙe cike da farin ciki ta shiga zaga gidanta sai taga komai yayi mata yadda take so babu abinda ta rasa, nan ta shiga jero godiyarta ga Allah dan sosai ta yaba da Sadi saboda' jiya ya shayar da ita wani ruwa mai mugun zaƙi.
Ashe Ustazai sun iya soyayya haka?
Ta faɗa a zuciyarta. A hankali ƙin auren ya riƙa barin zuciyarta har ta fara samar masa gurbi a ciki. Nan ta koma ɗakinta ta kunna wayar dan dama ya sanar da ita anyi chargynta, ta duba ko akwai kuɗi a ciki taga kusan dubu biyar ga kuma data kusan 2gb ta saki murmushin farin ciki sai ta kunna data ta fara setting komai na wayar ta ɗaura gmail ɗinta, duk contact ɗinta suka dawo, nan take ta kira Najwa domin ita ce wacce take son fara kira ta sanar da ita damuwarta dama komai daya faru.
Najwa tana kwance a É—akin yara wanda yanzu ya zama nata, game take yi a wayar Siyama É—iyar Saleema wanda a yanzu ya zama nata dan ta saka sim É—inta a ciki, kiran daya shigo wayarta yasa ta duba taga number ne bata san me layin ba, kamar ba zata É—aga ba sai kuma ta yanke É—auka ta kara a kunne, muryar Nafeesa data ji yasa ta tashi ta zauna tana faÉ—in sunanta. Nafeesa ta amsa tana cewa.
Ƙawata abubuwa da yawa sun faru dani ina son yin magana dake ban samu hali ba, sai yau da aka bani waya a hannuna.
Ina jinki amma kafin nan da fatan kin bar mini Aminu ko, dan kin san har yau ban huce ba.
Dalla waketa Aminu yanzu, ni da aka É—aura aurena jiya da Sadi malamin yaran gidanmu.
Kai dan Allah, garin ya haka ta faru.?
Najwa ta faɗa tana dafe ƙirji da zaro ido waje dan taji lamarin yazo mata a bazata, Nafeesa ta nisa ta soma bata labari tun sadda Taju yaje gida ya sanar da saƙp da aka tura masa wanda Hamisu ne ya tura, tiryan tiryan take bata labari babu abinda ta ɓoye mata, har zuwa auren da aka mata gidan da aka kawota da kuma akwatina ga kuma kyautar waya da Sadi ya bata yau, nan take Najwa taji wani abu ya ɗarsu a zuciyarta wanda sam bata so ƙarshen Nafeesa yazo a haka ba, taso ace ta fita wulaƙanta sai gashi tona mata asirin da tayi yaja mata wani nasara har ta fita mutunci yanzu, Nafeesa jin Najwa tayi shuru bata ce komai ba yasa tace.
Ƙawata kinyi shuru baki ce komai, wlh ke ce na fara kira domin mu shirya kiji kuma abinda ya sameni ki taya ni jaje da murna, sannan kinga yanzu bani ba Aminu sai mu cigaba da ƙawancen mu, ki bani labarin ya kika ƙare da Aminu daya ga ke ce Amaryarsa.
Najwa wasu zafafan hawaye ne suka shiga zarya a kuncita ji take yi komai daya faru ya dawo mata sabo, ga baƙin cikin Nafeesa ta yi nasara akanta ita kam kamar tsiya akanta ya ƙare, cikin sanyin murya tace.
Ai Nafeesa faɗan da muka yi dake a falon Amuni ya lalata komai domin yana ciki yaji komai hakan ya jawo mini duka a gunsa da safe kuma ya ɗaukeni har gidansu Sameeha ya tona mini asiri ya kuma sakeni saki biyu a gabansu, yanzu haka ina kano gurin ƙanwar babana Saleema, kowa ya juya mini baya.
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, amma banji daɗin faruwar haka ba kiyi haƙuri ki yafe min domin nice naja komai.
Ai dole ki bani haƙuri bayan kin cutar dani, to bari in faɗa mini ni ce nan na turawa yayanki saƙon nan a matsayin Hamisu ne domin tunda na rasa Aminu kema in tona miki asiri da Binafa.
Najwa dama kece kika tona mini asiri? Yanzu na cancanci kiyi mini haka duk iya halaccin dana yi miki.
Wlh Nafeesa fiye da haka zanyi miki domin kin rabani da farin ciki na.
Hmmmm to ai ni gwara ma da kika tona mini asiri domin kuwa gaba takaini yadda kike fatan na wulaƙanta ban yi ba domin Allah ya rufa mini asiri kuma na karɓi ƙaddarata, wannan maganar da kika sanar dani yasa na ƙara fahimtar ke butulu ce kuma dole in raba hanya dake saboda ke ba mutumiyar arziki ba ce, ni na karɓi ƙaddarata kuma ina niman Allah ya yafe mini sannan har gidansu Sameeha zanje in nima yafiyarsu dan ina so nayi rayuwa da mijina cikin salama, daga yau bani ba ke Najwa domin zuciyarki ba tada kyau.
Tana gama faɗar haka ta kashe wayar, na take tayi blocking number ɗin Najwa dan sosai take jin ba zata ƙara barin wata alaƙa ta shiga tsakaninsu ba saboda Najwa ba abokiyar arziki bace. Najwa kuwa kukan baƙin ciki ta fashe dashi da jin takaicin yadda Nafeesa ta samu rufin asiri cikin ƙanƙanin lokaci, taso ta wulaƙanta fiye da ita sai kuma hakan ya zama silar rufuwar nata asirin, dole itama ta yi aure cikin ƙanƙanin lokaci ko zata samu sassauci daga halin da take ciki.
Binafa...
[5/10, 8:32 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
50
Binafa.
Nine ya dace na gode miki da kika amince da ni a matsayin mijinki baki yi mini jayayya ba ganin ni ba kowa nace almajirin gidanku.
Haba kafi ƙarfin haka a guna domin bazan taɓa gujewa zaɓin iyayena ba, kuma yanzu na tabbata ba suyi mini zaɓin banza ba. Sai dai zan nima alfarma a gunka ka bani tsohon layina dan na cire numbobin daya dace.
Layinki baya hannuna Nafeee, amma bada gmail kike saving ba.?
Wasu suna cikin wayar amma akwai wasu a gmail.
To kiyi amfani da gmail É—inki In Sha Allah zaki samu duk number din da kike so a ciki.
To tace masa kana ya miƙe yayi mata sallama ya fita, Nafeesa ta miƙe cike da farin ciki ta shiga zaga gidanta sai taga komai yayi mata yadda take so babu abinda ta rasa, nan ta shiga jero godiyarta ga Allah dan sosai ta yaba da Sadi saboda' jiya ya shayar da ita wani ruwa mai mugun zaƙi.
Ashe Ustazai sun iya soyayya haka?
Ta faɗa a zuciyarta. A hankali ƙin auren ya riƙa barin zuciyarta har ta fara samar masa gurbi a ciki. Nan ta koma ɗakinta ta kunna wayar dan dama ya sanar da ita anyi chargynta, ta duba ko akwai kuɗi a ciki taga kusan dubu biyar ga kuma data kusan 2gb ta saki murmushin farin ciki sai ta kunna data ta fara setting komai na wayar ta ɗaura gmail ɗinta, duk contact ɗinta suka dawo, nan take ta kira Najwa domin ita ce wacce take son fara kira ta sanar da ita damuwarta dama komai daya faru.
Najwa tana kwance a É—akin yara wanda yanzu ya zama nata, game take yi a wayar Siyama É—iyar Saleema wanda a yanzu ya zama nata dan ta saka sim É—inta a ciki, kiran daya shigo wayarta yasa ta duba taga number ne bata san me layin ba, kamar ba zata É—aga ba sai kuma ta yanke É—auka ta kara a kunne, muryar Nafeesa data ji yasa ta tashi ta zauna tana faÉ—in sunanta. Nafeesa ta amsa tana cewa.
Ƙawata abubuwa da yawa sun faru dani ina son yin magana dake ban samu hali ba, sai yau da aka bani waya a hannuna.
Ina jinki amma kafin nan da fatan kin bar mini Aminu ko, dan kin san har yau ban huce ba.
Dalla waketa Aminu yanzu, ni da aka É—aura aurena jiya da Sadi malamin yaran gidanmu.
Kai dan Allah, garin ya haka ta faru.?
Najwa ta faɗa tana dafe ƙirji da zaro ido waje dan taji lamarin yazo mata a bazata, Nafeesa ta nisa ta soma bata labari tun sadda Taju yaje gida ya sanar da saƙp da aka tura masa wanda Hamisu ne ya tura, tiryan tiryan take bata labari babu abinda ta ɓoye mata, har zuwa auren da aka mata gidan da aka kawota da kuma akwatina ga kuma kyautar waya da Sadi ya bata yau, nan take Najwa taji wani abu ya ɗarsu a zuciyarta wanda sam bata so ƙarshen Nafeesa yazo a haka ba, taso ace ta fita wulaƙanta sai gashi tona mata asirin da tayi yaja mata wani nasara har ta fita mutunci yanzu, Nafeesa jin Najwa tayi shuru bata ce komai ba yasa tace.
Ƙawata kinyi shuru baki ce komai, wlh ke ce na fara kira domin mu shirya kiji kuma abinda ya sameni ki taya ni jaje da murna, sannan kinga yanzu bani ba Aminu sai mu cigaba da ƙawancen mu, ki bani labarin ya kika ƙare da Aminu daya ga ke ce Amaryarsa.
Najwa wasu zafafan hawaye ne suka shiga zarya a kuncita ji take yi komai daya faru ya dawo mata sabo, ga baƙin cikin Nafeesa ta yi nasara akanta ita kam kamar tsiya akanta ya ƙare, cikin sanyin murya tace.
Ai Nafeesa faɗan da muka yi dake a falon Amuni ya lalata komai domin yana ciki yaji komai hakan ya jawo mini duka a gunsa da safe kuma ya ɗaukeni har gidansu Sameeha ya tona mini asiri ya kuma sakeni saki biyu a gabansu, yanzu haka ina kano gurin ƙanwar babana Saleema, kowa ya juya mini baya.
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, amma banji daɗin faruwar haka ba kiyi haƙuri ki yafe min domin nice naja komai.
Ai dole ki bani haƙuri bayan kin cutar dani, to bari in faɗa mini ni ce nan na turawa yayanki saƙon nan a matsayin Hamisu ne domin tunda na rasa Aminu kema in tona miki asiri da Binafa.
Najwa dama kece kika tona mini asiri? Yanzu na cancanci kiyi mini haka duk iya halaccin dana yi miki.
Wlh Nafeesa fiye da haka zanyi miki domin kin rabani da farin ciki na.
Hmmmm to ai ni gwara ma da kika tona mini asiri domin kuwa gaba takaini yadda kike fatan na wulaƙanta ban yi ba domin Allah ya rufa mini asiri kuma na karɓi ƙaddarata, wannan maganar da kika sanar dani yasa na ƙara fahimtar ke butulu ce kuma dole in raba hanya dake saboda ke ba mutumiyar arziki ba ce, ni na karɓi ƙaddarata kuma ina niman Allah ya yafe mini sannan har gidansu Sameeha zanje in nima yafiyarsu dan ina so nayi rayuwa da mijina cikin salama, daga yau bani ba ke Najwa domin zuciyarki ba tada kyau.
Tana gama faɗar haka ta kashe wayar, na take tayi blocking number ɗin Najwa dan sosai take jin ba zata ƙara barin wata alaƙa ta shiga tsakaninsu ba saboda Najwa ba abokiyar arziki bace. Najwa kuwa kukan baƙin ciki ta fashe dashi da jin takaicin yadda Nafeesa ta samu rufin asiri cikin ƙanƙanin lokaci, taso ta wulaƙanta fiye da ita sai kuma hakan ya zama silar rufuwar nata asirin, dole itama ta yi aure cikin ƙanƙanin lokaci ko zata samu sassauci daga halin da take ciki.
Binafa...
[5/10, 8:32 PM] Rahma Kabir: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
50
Binafa.