Sashe 83
Abun Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Masha Allah naji daɗin umma da zata riƙe su, nasan sai ta fiki kulawa da su tunda ke kina fama da mijinki ga harkar siyasa da kuke yi, sannan batun kaisu makaranta akwai driver da zai dawo nan da motarsu in yaso zai cigaba da kaisu ina biyansa, dama ɗan nan Kaduna ne kinga ya riƙa barin mota a nan gidan da safe ya riƙa zuwa, sannan duk inda Umma zata da Anwar sai ya kaisu kinga ya zama drivern gidan gabaɗaya. In Sha Allah cikin kwanakin nan zanyi komai na makarantar nazo na kaisu nan turkish ɗin, sannan zan haɗo kayansu gaba ɗaya ma, tare da sauran abubuwan da suka dace.
Yayi maganar cikin fara'a fuska sake, murmushi Sameeha tayi jin zolayar da yayi mata a maganarsa ta farko, tace masa shikenan duk abinda ya yanke yayi dama ita yau zata koma Abuja, yayi mata fatan alkhairi sai suka yi sallama. Ba jimawa ya kira umma a wayarta bayan sun gaisa yake ce mata zai riƙa kiranta a waya suna gaisawa da kuma duk abinda ya shafi yaran ta riƙa faɗa masa yanzu ba yida mahaifiyar data fita, umma taji daɗin haka ta saka masa albarka tare da yi masa fatan gamawa lafiya, nan ta bawa su Abi wayar suka fita suna waya da babansu, Umma ta kalli Sameeha tana cewa.
Wlh Aminu mutum ne, banda ƙaddara ta rabaku da zanso ya cigaba da zama sirikina, yana da kirki dan tausayi ma yake bani yanzu,Allah dai ya bashi lafiya ya warke ya samu mata tagari ya aura.
Ameen umma ni ma kaina fatan lafiya nake yi masa kenan, domin a yanzu ina yi masa kallo tamkar É—an uwana na jini.
Allah ya rabamu da mummunar ƙaddara, da ace Najwa ta kirki ce da in ya samu lafiya sai ya mayar da aurensu.
Haba umma wlh bana masa fatan Najwa, dan a yanzu haka ina masa kwaɗayin auren ƙanwar Shamsu wanda suke uba ɗaya, in har Aminu ya samu lafiya kuma bata yi aure ba wlh ita zan nima masa ya aura, yarinyar ga hankali ilimin addini da sanin ya kamata, ta kammala jami'a yanzu tana koyarwa a nan Nuhu Bamalli poly dake zaria, itama ƙaddara ya rabata da mijinta sanadin auren da ya ƙara yaranta biyu.
Allah sarki kinji kowa dai da irin ƙaddararsa, zan so hakan ya faru kuwa, amma karki faɗawa kowa tukuna sai mun tabbatar da ya samu lafiyar ni da kaina zan shiga gaba wajen nima masa aurenta nasan Aminu zai yi mini biyayya.
Murmushi Sameeha tayi tana gasgata maganar umma dan sosai taji daɗin yadda ta amsa maganar, haka suka cigaba da hira har zuwa lokacin da Ibrahim yazo ɗaukarta ya shigo har gida ya gaisa da umma kana ya bar musu maƙudan kuɗi kamar yadda ya saba, shima yaso umma ta bar musu yaran dan sunyi maganar da Sameeha amma tunda umma ta hana dole ya bar maganar, haka suka tafi su Abi suna yi musu bye bye.
*
Abuja.
Bayan sun isa Sameeha ta É—aura musu girki, Ibrahim yazo ya tsaya a bayanta yana cewa.
Gaskiya yau matata ba zata girka komai ba, shiryawa za kiyi muje muci abincin waje, saboda akwai aiki na musamman da za kiyi anjima kinga in kin gajiyar da kanki yanzu aikin anjima bazai samu yadda naje so ba.
Sameeha ta juyo tana fuskantarsa É—auke da murmushi.
Mahboob É—ina yau da kanka zaka ci abincin waje, ni dai ka barni na samu lada biyu na yanzu da kuma anjima.
Naƙi wayon muje ki shirya mu fita dan gaskiya ina son more soyayya ne yau, nayi kewarki kwana biyu so badly.
Ya ƙare maganar yana jan dogon hancinta ita kuma matsowa tayi tayi masa kiss a kuncinsa kana tayi masa a wuyansa, wanda ya saka shi sakin wani ƙara sai ta zame ta ruga a guje yabi bayanta yana cewa.
Ai tunda kika fara kunna ni tun yanzu zan bankaÉ—a asirin soyayyarmu.
Haka suka dinga zagaye falon suna dariya da junansu, saida Sameeha ta gaji kana ta zube a cushing tana mayar da numfashi, shima ya dawo gefenta ya zauna tare da cewa.
Wa na kama.
Ni, amma dan Allah karka mini komai muje muyi wanka mu fita nima ina muradin shaƙar iskar waje tare da gaurayyen numfashin mijina a kusa dani.
Ta ƙare tana kanne masa ido, murmushi yayi wanda ya bayya kyawun fuskarsa.
Allah yayi miki albarka Haskena ina alfahari da samunki, ban taɓa zaton aure yanada farin ciki da natsuwa ba a duniyarmu ta Hausawa ba sai dana sameki nasan haka, Sameeha na tabbatar samun irinki a duniyar nan sai an tona, duk da ina busy ina harkar siyasata amma wlh inna tuna dake sai naji babu gajiya ina samun kwarin guiwar gunadar da komai cikin salama.
Wannan shine fatana a kullun ka kasance cikin farin ciki, ni baiwarka ce, masoyiyarka ce, sai yadda kayi dani domin zuciyata da gangan jikina mallakinka ne, ina sonka Ibrahim.
Tana gama faɗar haka ta miƙe ta wuce tana rausaya cike ta jan hankalinsa, nan take ƙaunata da yake yi mata yaji ya nunku har wani hucin numfashi yake fitarwa, banda ya ɗaukarwa kansa alƙawari babu saki a rayuwar aurensa da Nabila amma da ya saketa ya kasance da Sameeha ita kaɗai, dan sai yayi ma da gaske zai iya yin adalci a tsakaninsu, to zuciya tana son mai kyautata mata haka kuma tana ƙaunar mai ƙaunarta domin Allah, ji yake kamar shi kaɗai ne namijin daya yi sa'an samun matar kwarai, Sameeha ta zame masa bangon jingina farin cikin rayuwarsa a nan duniya da kuma a aljanna da yake fata, haka ya miƙe yabi bayanta wanda koda ya shiga ya sameta cikin wani irin rigar barci da bai santa da shi b,a dan kuwa alƙawari ta yiwa kanta na faranta masa a duk lokacin data gane yana muradinta, Ibrahim bai tsaya ɓata lokaci ba ya bi lafiyar gado tare da ƙanƙameta yana shakar kamshin dake fita daga wuyanta, daga nan sai suka lula duniyar masoya sai da suka samarwa kansu natauwa kafin suka yi wanka tare suka shirya cikin ƙananun kaya, Ibrahim t-shirt blue ya sanya ya saka jins baƙi ya feshe jiki da turare, Sameeha kuwa top ta sanya pink da rashin blue a jiki, sai ta saka siket fari mai buɗewa kana ta ɗauki after dressing mai shara shara blue ta ɗaura akan kayanta ta yane kanta da gyalensa, yadda tayi masifar kyau sai da Ibrahim ya ɓata lokaci wajen yi mata hotuna sannan shima suka ɗauka tare itama tayi masa kafin ya saƙala hannunsa a nata suka fice daga gidan cike da tsantsar soyayya, shine da kansa yaja motar security kuma suna binsu a baya, a haka suka fita tare da buɗe saman mota iskar gari yana kaɗasu gidauniyar soyayya tana fizgarsu.
(Ko wani aure akwai farin ciki a cikinsa muddun akwai kyakkyawar fahimta da kauna).
****
Aminu.
A cikin sati guda yaje Abuja ya koma Kaduna ya kai su Abi makarantar daya amso transfer ɗinsu, tare da driver suka zo ya gabatar dashi ga su Umma, sannan yaje kasuwa yayi wa yaran siyayya mai yawa da kayan abinci daya siyawasu Umma da yawa, kana ya turawa Zaidu kuɗi masu yawa akan cefanen gida mai ɗin mota da sauransu, ya yiwa su Umma sallama ya wuce babban gida nan ma ya sallami 'yan uwansa. A washe gari ya koma Abuja wanda bayan mako guda jirginsu ya ɗaga ya bar ƙasar zuwa London.
*****
Nafeesa.
Tunda aka amshe wayarta ta zama kamar mararniya saboda ta yi mugun sabo da waya, ba ƙaramin hukuntata akayi da shi ba dan ji tayi gwara kullum a bigeta akan a rabata da wayar, tana son yin magana da Najwa sannan ta amsa number Sameeha amma ina ba a barinta ta fita balle ta samu damar yin magana da su. Kuma a satin Taju ya samu Sadi yayi masa zancen Nafeesa sai dai ya sanar da shi Fyaɗe aka yi mata idan zai aureta to, yace ya amince domin kuwa ya yarda da ƙaddara tunda ba yin kanta bane Fyaɗe aka yi mata, sannan ma babu namiji kamarsa da za a bashi auren Nafeesa yace baya so domin daidai gargwado tana da kyau ga hasken fata kuma akwai diri, abu ne da bai taɓa zato ba ko ya kawowa kansa samun matar aure irinta dan haka ya amince. A satin iyayensu suka zo nima masa aurenta da sadaki dubu Hamsin wanda SaDi ya basu, Alhaji ya ce ya basu sannan da zasu tafi ya basu key ɗin gidan daya mallakawa Sadi, yace ya yafe masa akwati nan gaba in ya samu hali sai ya ɗinka mata suturar daya dace, ba ƙaramin daɗi suka ji ba tare da yin godiya.
Yayi maganar cikin fara'a fuska sake, murmushi Sameeha tayi jin zolayar da yayi mata a maganarsa ta farko, tace masa shikenan duk abinda ya yanke yayi dama ita yau zata koma Abuja, yayi mata fatan alkhairi sai suka yi sallama. Ba jimawa ya kira umma a wayarta bayan sun gaisa yake ce mata zai riƙa kiranta a waya suna gaisawa da kuma duk abinda ya shafi yaran ta riƙa faɗa masa yanzu ba yida mahaifiyar data fita, umma taji daɗin haka ta saka masa albarka tare da yi masa fatan gamawa lafiya, nan ta bawa su Abi wayar suka fita suna waya da babansu, Umma ta kalli Sameeha tana cewa.
Wlh Aminu mutum ne, banda ƙaddara ta rabaku da zanso ya cigaba da zama sirikina, yana da kirki dan tausayi ma yake bani yanzu,Allah dai ya bashi lafiya ya warke ya samu mata tagari ya aura.
Ameen umma ni ma kaina fatan lafiya nake yi masa kenan, domin a yanzu ina yi masa kallo tamkar É—an uwana na jini.
Allah ya rabamu da mummunar ƙaddara, da ace Najwa ta kirki ce da in ya samu lafiya sai ya mayar da aurensu.
Haba umma wlh bana masa fatan Najwa, dan a yanzu haka ina masa kwaɗayin auren ƙanwar Shamsu wanda suke uba ɗaya, in har Aminu ya samu lafiya kuma bata yi aure ba wlh ita zan nima masa ya aura, yarinyar ga hankali ilimin addini da sanin ya kamata, ta kammala jami'a yanzu tana koyarwa a nan Nuhu Bamalli poly dake zaria, itama ƙaddara ya rabata da mijinta sanadin auren da ya ƙara yaranta biyu.
Allah sarki kinji kowa dai da irin ƙaddararsa, zan so hakan ya faru kuwa, amma karki faɗawa kowa tukuna sai mun tabbatar da ya samu lafiyar ni da kaina zan shiga gaba wajen nima masa aurenta nasan Aminu zai yi mini biyayya.
Murmushi Sameeha tayi tana gasgata maganar umma dan sosai taji daɗin yadda ta amsa maganar, haka suka cigaba da hira har zuwa lokacin da Ibrahim yazo ɗaukarta ya shigo har gida ya gaisa da umma kana ya bar musu maƙudan kuɗi kamar yadda ya saba, shima yaso umma ta bar musu yaran dan sunyi maganar da Sameeha amma tunda umma ta hana dole ya bar maganar, haka suka tafi su Abi suna yi musu bye bye.
*
Abuja.
Bayan sun isa Sameeha ta É—aura musu girki, Ibrahim yazo ya tsaya a bayanta yana cewa.
Gaskiya yau matata ba zata girka komai ba, shiryawa za kiyi muje muci abincin waje, saboda akwai aiki na musamman da za kiyi anjima kinga in kin gajiyar da kanki yanzu aikin anjima bazai samu yadda naje so ba.
Sameeha ta juyo tana fuskantarsa É—auke da murmushi.
Mahboob É—ina yau da kanka zaka ci abincin waje, ni dai ka barni na samu lada biyu na yanzu da kuma anjima.
Naƙi wayon muje ki shirya mu fita dan gaskiya ina son more soyayya ne yau, nayi kewarki kwana biyu so badly.
Ya ƙare maganar yana jan dogon hancinta ita kuma matsowa tayi tayi masa kiss a kuncinsa kana tayi masa a wuyansa, wanda ya saka shi sakin wani ƙara sai ta zame ta ruga a guje yabi bayanta yana cewa.
Ai tunda kika fara kunna ni tun yanzu zan bankaÉ—a asirin soyayyarmu.
Haka suka dinga zagaye falon suna dariya da junansu, saida Sameeha ta gaji kana ta zube a cushing tana mayar da numfashi, shima ya dawo gefenta ya zauna tare da cewa.
Wa na kama.
Ni, amma dan Allah karka mini komai muje muyi wanka mu fita nima ina muradin shaƙar iskar waje tare da gaurayyen numfashin mijina a kusa dani.
Ta ƙare tana kanne masa ido, murmushi yayi wanda ya bayya kyawun fuskarsa.
Allah yayi miki albarka Haskena ina alfahari da samunki, ban taɓa zaton aure yanada farin ciki da natsuwa ba a duniyarmu ta Hausawa ba sai dana sameki nasan haka, Sameeha na tabbatar samun irinki a duniyar nan sai an tona, duk da ina busy ina harkar siyasata amma wlh inna tuna dake sai naji babu gajiya ina samun kwarin guiwar gunadar da komai cikin salama.
Wannan shine fatana a kullun ka kasance cikin farin ciki, ni baiwarka ce, masoyiyarka ce, sai yadda kayi dani domin zuciyata da gangan jikina mallakinka ne, ina sonka Ibrahim.
Tana gama faɗar haka ta miƙe ta wuce tana rausaya cike ta jan hankalinsa, nan take ƙaunata da yake yi mata yaji ya nunku har wani hucin numfashi yake fitarwa, banda ya ɗaukarwa kansa alƙawari babu saki a rayuwar aurensa da Nabila amma da ya saketa ya kasance da Sameeha ita kaɗai, dan sai yayi ma da gaske zai iya yin adalci a tsakaninsu, to zuciya tana son mai kyautata mata haka kuma tana ƙaunar mai ƙaunarta domin Allah, ji yake kamar shi kaɗai ne namijin daya yi sa'an samun matar kwarai, Sameeha ta zame masa bangon jingina farin cikin rayuwarsa a nan duniya da kuma a aljanna da yake fata, haka ya miƙe yabi bayanta wanda koda ya shiga ya sameta cikin wani irin rigar barci da bai santa da shi b,a dan kuwa alƙawari ta yiwa kanta na faranta masa a duk lokacin data gane yana muradinta, Ibrahim bai tsaya ɓata lokaci ba ya bi lafiyar gado tare da ƙanƙameta yana shakar kamshin dake fita daga wuyanta, daga nan sai suka lula duniyar masoya sai da suka samarwa kansu natauwa kafin suka yi wanka tare suka shirya cikin ƙananun kaya, Ibrahim t-shirt blue ya sanya ya saka jins baƙi ya feshe jiki da turare, Sameeha kuwa top ta sanya pink da rashin blue a jiki, sai ta saka siket fari mai buɗewa kana ta ɗauki after dressing mai shara shara blue ta ɗaura akan kayanta ta yane kanta da gyalensa, yadda tayi masifar kyau sai da Ibrahim ya ɓata lokaci wajen yi mata hotuna sannan shima suka ɗauka tare itama tayi masa kafin ya saƙala hannunsa a nata suka fice daga gidan cike da tsantsar soyayya, shine da kansa yaja motar security kuma suna binsu a baya, a haka suka fita tare da buɗe saman mota iskar gari yana kaɗasu gidauniyar soyayya tana fizgarsu.
(Ko wani aure akwai farin ciki a cikinsa muddun akwai kyakkyawar fahimta da kauna).
****
Aminu.
A cikin sati guda yaje Abuja ya koma Kaduna ya kai su Abi makarantar daya amso transfer ɗinsu, tare da driver suka zo ya gabatar dashi ga su Umma, sannan yaje kasuwa yayi wa yaran siyayya mai yawa da kayan abinci daya siyawasu Umma da yawa, kana ya turawa Zaidu kuɗi masu yawa akan cefanen gida mai ɗin mota da sauransu, ya yiwa su Umma sallama ya wuce babban gida nan ma ya sallami 'yan uwansa. A washe gari ya koma Abuja wanda bayan mako guda jirginsu ya ɗaga ya bar ƙasar zuwa London.
*****
Nafeesa.
Tunda aka amshe wayarta ta zama kamar mararniya saboda ta yi mugun sabo da waya, ba ƙaramin hukuntata akayi da shi ba dan ji tayi gwara kullum a bigeta akan a rabata da wayar, tana son yin magana da Najwa sannan ta amsa number Sameeha amma ina ba a barinta ta fita balle ta samu damar yin magana da su. Kuma a satin Taju ya samu Sadi yayi masa zancen Nafeesa sai dai ya sanar da shi Fyaɗe aka yi mata idan zai aureta to, yace ya amince domin kuwa ya yarda da ƙaddara tunda ba yin kanta bane Fyaɗe aka yi mata, sannan ma babu namiji kamarsa da za a bashi auren Nafeesa yace baya so domin daidai gargwado tana da kyau ga hasken fata kuma akwai diri, abu ne da bai taɓa zato ba ko ya kawowa kansa samun matar aure irinta dan haka ya amince. A satin iyayensu suka zo nima masa aurenta da sadaki dubu Hamsin wanda SaDi ya basu, Alhaji ya ce ya basu sannan da zasu tafi ya basu key ɗin gidan daya mallakawa Sadi, yace ya yafe masa akwati nan gaba in ya samu hali sai ya ɗinka mata suturar daya dace, ba ƙaramin daɗi suka ji ba tare da yin godiya.