← Book details Zakin Sarakai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 87

Sashe 4

Zakin Sarakai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

sarkin dogarai wanda yake sshine sarkin dogarai kuma shine wanda ke kula da lamarin dawakan wajen Tunda ta karaso yake kallonta da ciyawar dake jibge a hannunsa wadda ya kwaso dan ya ciyar da bakin doki, domin dokin ne yakeda fada babu mai rabarsa da garaje Dakatawa ya yi sosai yana kallonta har ta karaso A hankali ta dan dago idannuwanta da suka shanye tamkar wace ta shanye su da gangan , bayan haka suke, da farko an zatama ciwon ido me da ita, domin idannuwanta a shanye suke koda yaushe irin tana kallon kasan idon nan, kuma girmansu da tudun samansu ya daka idan ta lumshe din kamar mai barci, ba kasafai take maka kallon cikin ido ba dan akan ce da ita wai kallonta na kayar da gaba, ta dan dago ta yi masa kallo a fuzge sannan ta maida dubanta wajen dokin dake kakawar da kai irin jibgegen dokin nan Murmushi ta yi har kananun hakoranta duka bayana jere reras ta daga hannunta fari kallll tana kallonsa ta ce" Zan so na shafa Dokin nan" Dokin ya kalla, sai kuma ya dake kallonta Shekarun matarsa sun ja, shi din kansa ya fi a irga yana neman hutu ko dan yarsa kwalin kwal da Allah ya bashi a duniya dan su koma inda take so su rayu su kula da ita, ama abin ya gagara, yarinyar ta ki yarda ta zauna a masarautar zai je ya daukota ya kawota ama tana gannin mijin kanwar maman nata zai koma kauyen *LABA* zata silale ta gudu, tamkar wace ake cizo a masarautar, a rayuwarta ita dama lamarin rayuwar sarauta ce sam ba tata ba, bata so bata kauna, ita tana kaunar rayuwa ce irin ta yanci, yadda zata bararaje ta walwala abinta, shi yasa take guduwa tana barinsu su kadai hankalinta kwonce Dokin ya sake kallo, sai ya yi murmushi ya kade hannayensa yana girgiza kansa ya shiga nufar bangarensu yana fadin" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, al alaminmu ancinmu.``` *https://www.facebook.com/106494781436168/* *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0 Dokin ya sake kallo ya yi murmushi, sai ya kade hannayensa ya shiga nufar bangarensu yana fadin" So kike yi a garin Tanut a gile min kaina? Domin wannan dokin mahaukacin doki ne, idan ya bale nima a tsorace nake, kina so ya bige ki na soke shi? Bayan zuciyar sarkin garin nan ne?......... Fadime ni kam ina mamakin me saraki ya gani a dokin nan da ya kamu da kaunarsa, doki bakin kirin ba annuri ko daya? Gashin idannuwansama bakake ne sidik" Dan murmushi ta yi tana tafe jikinta tamkar bata da lakka, hakan ya dakashi fakatawa yans dubanta sosai ya ce" INNARTA?, kamar hankalinki a tashe yake?" Dakatawar ta yi itama da tafiar da take yi ta juyo tana kallonsa A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta karasa wajen zama ta zauna fuskarta na nuna alhinun da zuciyarta ke ciki Jiki ba karfi ya karasa yana sakin labulen kofarsu ya zauna a gefenta kadan yana kallonta da yaren buzanci ya ce" Yauma wani abin ya faru da ke da uwar gijiyarki ne?" Idannuwan nata ta dake dagowa tana kallonsa Numfashi ta ja mai zafi, kai itafa a yanzu bama wannan ne damuwarta ba, danma rai da riko ne ta kasa sabawa da wulakancin dake bilowa lokaci zuwa lokaci a tsakaninta da Gimbiya, lalle a karkashinta take, ama an jima da goge bauta irin ta zama nin bayi, albashi garesu, aiki suke yi, dandai aiki ne na mudin rai, ama an jima da goge irin rayuwar nan ta rashin yanci, shi yasa take shan wahala, shi yasa ta kasa yin rayuwaa irin ta daba, shi yasa take yawan jin wani abu a cen kasan zuciyarta idan aka wulakantata Dan murmushi ta yi tana kallonsa ta ce" ABANTA, ka san da ta kai shekara goma sha tara har ta dora a duniya? Nakan damu da tarin zulumin tarbiyarta, ka san wacece kanwata ka san halayanta, duda na san ba zata taba bari ta zamto mai irin halayar nan ba, ama ina cike da tsoron ta zamto wata iri daban, ina matukar son na ajiye aikina na koma kusa da yarinyata, da ace a zaman kalau ne ka dan da yanzu tana dakinta, irin halayarta na rashin zama waje daya kan dagan hankali, kar aje tana cen tana cafta tarai a dajin Allah, kar aje abubuwan da take gwadawa na jarumtar da ya dace ace namiji ke nuna su ta damka ta mayar ruwan darenta, kana tune dawowa ka yi ka tarar ta yanka sanuwar Ladan dan ta tungujeni, ........ni kam damuwar yarinyata ta fara taba min nutsuwata, idan har zan iya ci gaba da wannan aiki to fa sai idan na mikata dakin mijinta" Ajiyar zuciy ya sauke ya gyara zamansa yana sake fuskantarta Murmushi ya yi yana kada kai, ba dan komai ba sai dan tino damarar yarinyar tasa, Rawani take yi tamkar dan saurayi tana shagalinta hankali kwonce Dira take ta haye saman doki ta warci linzaminsa ta kada akalarsa tun bata wuce sha uku ba Hm........... Lalle ya san ya dace ya nemi zama wa matarsa koda shi bai zauna ba, domin gidan Hindu ba gidan rainin budurwa bane, to wane ba wanema a cikinsu daga ita har mijinta? Ai tamkar makaho ne a saman makahon doki........... Da son kwontar mata da hankali ya sake fuskantarta, hannayenta masu laushi da hasken fari dan tsaftarta da kuma zama a cikin ACn da take koda taushe a bangaren Gimbiya ya dan karra murzawa a hankali ya ce" In sha Allah, zan kamanta sake shigar da takardar ajiyewar aikinki, idan amsa ta fito mana sai mu je mu daukota, ama nima ba zan so ku fita nesa da ni ba, domin ina da bukatarku a gefena kin ji INNARTA?" kai ta gyada tana sauke dan murmushi, duda tana cike da tunanin kamar aikin banza ne, domin an taba shugar da takardar a gabanta uwar gijiyarta ta yaga takardar tana fadin shirmen banza ba zata ajiye aiki yanzu ba, ama a yanzun tana tunanin ko a dace, domin ta kula ta ishi Gimbiya, bata san itama har ga Allah ta fara gajiyawa ba, zata so ta samu yanci irin na kowa ta kula da y'arta da kuma mijinta, ba bauta a banza ba! ___________________________________ Shigar yamaci suka yiwa baban garin na AGADAZ bayan tafia ta kwana biyu a hanya sanadiyar nisan dake tsakanin ziyarar da ya kai garin Dogon dutsi da kuma dan tsayawar da suka yi a hanya dan yada zango a wata masarautar da ziyara irin ta zumunci Tunda suka shigo baban garin ya haye saman bijimin dokinsa fari kal mai dauke da kwaliya irin ta ALBE da azurfa harda salkar zinari Kamar yadda yake da haske a fatar jikinsa, haka suturar jikinsa take, da kuma kamanin DOKINSA, takalmin kafarsa kafa ciki ne shima sai nasa walwalin yake Jama'ar gari du an fito tarbansa, tamkar wanda ya yi doguwar tafia Yawanci masoya ne, wasun kuwa yan su ga ya dawo da ransa da lafiyarsa ne? Taro dai taro na alkhairi ne, domin babu yaro babu baba, babu talaka ko mai kudi, sunna girmamashi sunna kaunarsa A hankali ya ringa tafiyar da dokinsa ga dogarai a gefe da gefe rike da lema tafkekiya itama sai walwali take ta haske ko'ina Kafafuwan dokin kan bada sauti cas cas idan ya ajiye kofaton kafarsa dalilin kwaliyar dake jikin kafar A haka har suka karasa baban masalacin masarautar suka yada zango dan gabatar da sallar Magariba da kuma ta isha'i Sai da suka gama sallar sannan ya shige Fada a nutse ya nufi bangarensa direct domin a mugun gajiye yake, danma an saba da hawa da saukar da kuma doguwar tafiyar? Ga umarah da zai tafi wace zai yi tafiyar sirri domin baya so a san inda ya nufa A nutse ya kama hannun falonsa bayan sun gama gaisawa da UMMA, wace take jalabiyarsa uwar goyonsa shi da kanwarsa sama sama domin ba zai zauna ba ya gaji over ya shige falon nasa da yar salamar dake saman leben bakinsa Idannuwansu ne suka sarke da junna a lokacin da ya shigo gaba dayansa Tsadaden murmushi mai sanyayar da zuciya ta dakar masa daga tsayen da take sannan ta nufo shi da yannayin taku irin nata cike da girmamawa ta dan gyara doguwar rigarta ta baza alkyabarta a kasa ta sada kanta sosai a sanyaye ta furta" Barka da karasowa ITIFAL" A hankali ya saki kofar dakin nasa ta dawo ta rufe, wanda hakan ya rufe kallonsu da UMMA ke yi daga nesa Murmushi ta yi ta girgiza kanta ta juya ta koma nasu bangaren, watau bangaren matan masarautar Idannuwansa ya lumshe mata yana sake binta da kallo a lokacin da ta duka har kasa ta saka hannayenta wajen kafarsa ta shiga sulube masa takalmansa dan ta san baya shiga ciki da takalmansa, yakan cire su a saka a wajen ajiyar takalmansa A hankali ta kara dukawa sosai wajen fara kal din safar kafarsa ta kai bakinta da niyar yiwa wajen kisss sai dai baai bata damar hakan ba ya janye kafarsa da dan sauri yana sake wara dubansa a kanta dan ba zai barta ta aikata hakan ba Murmushi ta yi ta mike ta saka hannayenta ta dalube alkyabarsa mai nauyi da masifar kyau ta karasa wajen ratayawa ta ratayata sannan ta juya Da ido kawai yake binta domin bayan ta samu amsa irin ta fatar idannuwansa dan son gane me take yi haka? Ita kuwa cike da takun kasaitar nan tata ta nufi wajen cin abinci tana fadin" Menene bukatar Uban gidana? A nan zaka ci abinci ko a dakinka? Domin burina na ciyar da kai da hannuna ko zan samu albarkar mai Albarka" Jin shirun ya yi yawa dosai fiye da da, domin a da din takan samu dan gyaran murya ko kula irin ta dan sasaukan murmushi ya sakata juyowa itama ta zuba masa idon Sake gyara tsayuwarsa ya yi a tsayen da yake yana harde hannayensa a dake ya furta" ME KIKE YI HAKA?" Ido ta zuba masa na dan sekwani, sai kuma ta sada kanta a sanyaye ta ce" Allah ya huci zuciyarka, shin na aikata
Chapter 4 · 0% Book details