← Book details Zainazain Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 78

Sashe 11

Zainazain Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Direct Gidan Alhaji Usman aka yi musu masauki,awani Shashe Dake gefe wanda bama Boysquaters bane Flat mai kyau aka kuma ingantasu da komai na More Rayuwa,Babu Abunda zasu iya cema Iyalan Dr.Saulawa sai Fatan gamawa da Duniya Lafiya,Cikin ikon Allah Maryama ta zama mai Taimakama Fatima da Aisha Duk da kasancewarta yarinya Domin Lokacin bata wuce Shekara 19 ba ammh akwai kwazo na matan kauye da kuma Biyayyah gata Shuru Shuru ba Ruwanta ga kwaici ga kunya,Anty Fatima Anty Aisha Sama Shi kuma Alhaji Usman Daga ita Har Abdullahi Yaya Suke Kiranshi yayinda Suke Kiran Dr Saulawa da Alhaji Dr.

Ayayinda Gefe Daya kuma Abdullahi na Cigaba da kula da Kifayen da Alhaji Usman ke kiwo aikinsa kenan,Gidan Dr.Saulawa kuwa kowani Lokaci Suna Zuwa Shida Maryama Domin ganawa da iyayensa Danginsu na chan gada kan kawo musu Ziyara Lokaci Bayan Lokaci Ita ma Maryama Yayarta Halima tazo Taga inda take ta Dinga murna da Fatan alheri Ganin Maryama ta samu iyayen Daki na Gari Tunda Daga Fatima Har Aisha Suna matukar Tsausayin Fatima Shiyasa komai suka samu itace Shi kanshi Alhaji Usman din kallonta yake kamar Hannatu ko Rukayyah Shiyasa suka Rikesu Hannun Bibbiyu tun Bale ma Dr.Saulawa wanda akullun Usman yaje gaisheshi sai yayi Fadan Kula da Hakkokin mutanen Dake kansa Tunda Tamkar Amanace gareshi.

Sannu Sannu Bata Hana zuwa sai dai Adade ba"a je ba Cikin Hajiya Fatima da Hajiya Aisha na kara Girma suna kuma samun Dukkan kulawa Domin Likita guda Dr.Saulawa Ya samu Daga asibitinsa tana Zuwa Duk bayan 4 weekes Tana Dubasu Tana musu awo Hankalinsu kwance Har Cikinsu ya Shiga Watan Haihuwa Wata Ranar Jumma"a Babba Rana Allah ya Saukeki Hajiya Fatima Lafiya inda ta Haifi santalelen Danta mai kama da Dr Saulawa,ko Mintuna Talatin ba"ayi ba itama yar"uwanta Hajiya Aisha ta Haifi Santaleliyar yarta mace mai kama da Alhaji Usman acikin asibitin Daya ke mallakin Surukinsu Wato Saulawa Speacialist Hosp Bauchi.

Dama Hajiya Fatima na Fara mukurkusun naguda Abu kamar wasa Maryama ta Kira Hajiya mama ta gayamata Tunda Alhaji Usman baya Gida Ita tazo Da Direba ita da Atine Bayan ta Kira Dr.Saulawa yace ta kawosu nan asibitin yanzu,kamar wasa fa Harda Hajiya Aishan da Maryama Suka Shiga Motar zuwa asibiti sai dai kafin su kai asibitin Itama Hajiya Aishan Ta Fara Nagudan maimakon Hajiya Fatima Sai Dr Saulawa yaga Duka Surukan nashi ne ke kan gwiwa ganin haka yasa aka Shiga Dasu Bangaransu masu Haihuwa Domin basu Taimakon gaggawa.

Haihuwan batayi Tambari ba Sai da aka gama Shirya masu Jego da yaran kana Hajiya mama ta Shiga kiran Waya tana Fadan Haihuwa murna ba"a mgana Alhaji Usman haka yazo asibitin kamar bakinsa zai Yage saboda Murna Maryama ita ke Tare da masu jegon a Dakin Hutu kuma Duka Jariran na Hannunta itama bakinta yaki Rufuwa iyayen Dakinta sun Haihu...

Atare da Dr.Saulawa da D'ansa Alhaji Usman Suka Shigo Dakin na musamman da aka Kai su Hajiya Fatima,Hajiya mama da Atine na Binsu abaya suna Shiga bayan sannu da Barka daya Biyo baya sai Dr.Saulawa ya kalli Maryama yana Fadin"Maryama Mikominsu nan naji Dumin Jikokina..Allah yakai Raina.!

Tana Mirmishintaa na kunya ta Tashi Ta mikamai Su Duka ya Hada ya Dauka Har Hajiya Mama namai Tsiyan bai bari Uban Yara ya Dauka ba yayi mirmishi yana Fadin"Nima Uba nake garesu Amina..Ko ba Haka ba Usman Bin Fodiyo..?

Dariya yayi yana Fadin"Kwarai Abba..Tabbatas kai Uba kake garesu kai zaka musu Hudubu yanzu yanzu ka Sa ka musu Sunan da kaga yayi maka..Ai Dani da Matana Da ya"yan Dana Haifa duk ikon ka ne..!

Kowa Mirmishi yake adakin Dr.Saulawa ya kalleshi yana Fadin"Allah yayi maka albarka kaida Matanka Usman Fodiyo..!

Duka suka amsa da Ameen kujera Usman ya bashi ya Zauna ya Fara Daga macen ya mata Huduba aduka kunnuwanta kana ya Matsamata Dabino a baki kana ya mikama Usman yana Fadin"Allah ya Raya ZAREENA USMAN ABUBAKAR SAULAWA..!

Ya karbeta yana Fadin"Masha Allah Ameen Ameen Abba.."Namijin ya Daga Shima yayi mai Huduba kuma ya Bashi Dabino Shi harda Ruwan zamzam ya mikama Alhaji Usman yana Fadin"Wannan yaron Magaji na ne..Tun a Suna na sakamai DR.ZAINULLAHI USMAN ABUBAKAR SAULAWA..Allah ya Rayamana Shi.."
Gabadayansu suka amsa da Ameen kafin ya mike Alhaji Usman ya mikama Hajiya mama Jaririan ta Dauka kana ta mikama Atine itama ta Dauka ta saka Albarka kana ta mikama Maryama su Wanda Ta Nufi Hajiya Fatima Ta mika mata Zainullahi sai taki karba sai kawai ta saka Hannu Ta karbi Zareena Tana Fadin"Nifa ga yata nan..Mikama Aisha yaronta..!

Kowa sai ya saki baki yana kallonta Jin Haka yasa Hajiya Aisha Tace"Naji bakomai..Maryama Mikomin Da'na..Dama mun Riga mun gama mgana nayi miki alkawarin in mace na Haifa taki ce Har Abada ke kuma in kika Haifi Namiji nawa ne Har Abada..Allah ya cikamana Burinmu sai dai muyi Fatan Allah ya tayamu Tarbiya..!

Maryama Tana Mirmishi Tace"Nice Shaida..Ni kuma nayi alkawarin Tayaku kula dasu Tankamar ya"yan da zan Haifa da Cikina..!

Gabadaya Dakin suka amsa da Ameen Mirmishin Farinciki da kuma Annushuwa ya wanzu a zuciyar Dr.Saulawa hakama Hajiya Mama da Atine Shi kuwa Alhaji Usman mamaki ya kamashi na yarda har suka Tsaida wannan alkawarin bai sani Hadin kan matanshi na Burgeshi kuma yana jin Duk Duniya ba wanda yakai shi Dace..
*Comments*
*Share and vote*
*Shakira...*
*Intelligent writer"s asso...*
*ZAINAZAIN..!*
_(Is a love Story and Betrayal)_
*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janaftyshakira*
*BOOK 1*
"Dr.Abubakar Saulawa yafi kowa Murna da wannan Sabon Hadin kai Tare da alkawarin Dake Tsakanin Hajiya Fatima da Hajiya Aisha,sai dai kuma ya katse musu Hanzari Wajen basu Umarnin kowacce ta Shayar da Abunda ta Haifa da kanta Ammh alkawarinsu na nan bai Tashi ba Da Suka nemi sanin Dalili sai yace musu Saboda Halin Rayuwa Ko bakomai Tunda Dukkansu Suna Raye ya Zama Dole kowacce ta Shayar da Abunda ta Haifa da wannan matsayar aka Tsaya Inda aka Mikama Fatima Zainullahi ta Shayar dashi Ita kuma Aisha aka Mika mata Zareena ta bata Nono kuma Dukkansu suka kama Bayan Sun gama ba Jaririnansu Nono ne bayan sun Samu Natsuwa aka Sallamesu suka Dunguma Zuwa Gida Cikin Tsantsan Farincikin da baki bazai iya Furta shi ba.

Kafin kace kwabo Haihuwan Tagama Karade Dangi kafin Suna ta Zagayo yan"uwa na Nesa Dana Kusa Sun iso kamar su Hannatu da Rukayyah Bashir da iyalansa Hakama Aliyu Shima Da nashi Iyalin Wacce Itama Cikinta Dan Kimanin Wata Shida ya bayyyana Dukkansu Sun Taru Domin Taya Dan"uwansu Murna samun karuwar ya"ya a karo na Biyu bayan Matansa Daya Aura Rana Daya.

Ranar suna ansha Shagali Abunda sai wanda ya gani bayan Raguna Harda sa Dr.Saulawa ya sa aka Kada Saboda Haihuwan Jikokinsa aka Rabama Takalawa kowa fa ya Shaida wannan Haihun matuka kuma kowa ya Fahimci yadda Dr Saulawa ya Dauki Haihuwan da matukar Muhimmanci Shi da Hajiya Mama.

Bayan Suna Baki da yan'uwa kowa ya koma Gidajensa aka bar masu Jego Maryama na Tare Dasu na Kula da yara Sai kuma Atine Dake zuwa Tana yima Su Hajiya Fatima wankan Tare da Umarnin Hajiya Mama ganin Maryam bawata Babbace bace Sai aka bar mata kula da yaran Wanda ko yake Kiransu da yan Biyu ganin Rana Daya suka Zo Duniya Kuma Duk da kowa Uwarsa ke Shayar dashi Ammh Da Zarar Kowacce ta gama Shayar da nata Hajiya Fatima Zata Karbe Zareena Itama Hajiya Aisha Zata karbi Zainullahi Har suna Rige Rige Wani Lokacin Maryama Ke ganin Dirarmar nasu Tayi ta bama Alhaji Usman in ya Dawo Labari Shi kuwa yana Jin Labari Nishadi da kaunar matan nashi na Kara Wutar Ruruwa acikin Ranshi...

Wata Hudu da Haihuwan su Zareena Safiya Matar Aliyu ta Sauka achan Abuja Ta Haifi Santalelen Danta Jajir mai kama da Ubansa Wannan karon ma Dr.Saulawa ya Saka mai Suna Wato HADDIR ALIYU ABUBAKAR SAULAWA..!

Tun Daga sannan kuma Babu Wata karuwa da aka Kara samu Sai Duka Suka maida Hankulansu Wajen kula da yaran da Allah ya basu,Bangaran su Zareena da Zainullahi kuwa Maryama ce keda alhakin kula dasu Har ma Sun Saba da ita,domin itace komai nasu Wankansu Saka musu kaya kula da Cin Abincinsu da kuma Cire Musu pampers in sun bata Duka itace Lokaci kadan Yaran suka Shaku da ita Bama Ita kadai Harda Abdullahi mijinta Sun Shaku Dashi Domin In Tagama aikinta Sassan su Hajiya Fatima kwasan Yaran take su koma Barayinsu Su tayi ta kula Dasu Ita da Abdullahi Tunda Shima ba wani aikin yake ba kula da Kifaye ne,da basu abinci Safe da Yammah Da ka gansu zaka Fahimci Suna Cikin Farinciki da Jin Dadin Rayuwa.

Bashir Bai Haihu ba Sai da su Zareeena Suka Shekara Biyar a Duniya Yayinda Haddir keda Hudu da wani Abun Sun Girma Babu Inda kafarsu bata takawa Har an sakasu a Makaranta,Lokacin da Iklima ta Haihu Tasha Wuya Sai kuma Jaririn ya Fito bashi da lafiya haka akayi Suna yaro yaci Sunan Dr Saulawa Wato Abubakar bai kai Wata Biyar ba Allah yamai Rasuwa Tun kuma Daga Lokacin sai ya koma in ta Samu Ciki Sai ta Dinga Barinsa Ko kuma Sai yakai Wata bakwai ta Haifeshi Ba Rai,Sakamakon Ita Ikliman Binciken Likitoci Sun gano Tana da Raunin Mahaifa Sosai Gashi kuma ta Fara Palanning kafin Ta Haihu Shi ya jawo mata matsalan Bashir ya Damu Sosai Domin a Lokacin yana Bukatar Haihuwar ammh kuma Sai Allah ya Nuna ikonsa Dole babu yadda Suka iya suka koma Suka Rungumi Junansu Tunda bai isa ya Gujema Ikliman ba Koma meya Faru Shine Silan komai.

Su Zareena Da Zain nada Shekara Bakwai Aduniya Zain kamar yadda Zareena Take Kiranshi Tunda bakinta bai iya furta Zainullahi din Sosai ba,sai Sunan Gabadaya yabi bakin iyayen nasu kowa da Zain yake Kiransa Ita kuma Hajiya Aisha Zain ne Tunda ya Fara koyon mgana ya Fara Kiranta da NENE shikenan kuma Sunan ya Bita ayayinda Zareena ke kiran Hajiya Fatima da UMMAN ZAREENA,saboda yadda Duk Duniya Hajiya Fatima Bata da Abun kauna da Tattali Irin Zareena Shiyasa Dr Salauwa Ya sakamata Umman Zareena sai kuma ya Bita har ya"yan suka kama Maryama kuma Mama maryama Abdullahi kuma Suna Kiranshi da Baba ne ayayinda Suke Kiran Alhaji Usman da Abba Tun Suna yara.
Chapter 11 · 0% Book details