Sashe 76
Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ta tabe tace bai taba ce min I love you ba,haka ake caring wai a haka Sunan matarsa ce ni,ba wani love things ba komai,Naila tana jinta tana surutu,tace wanne I love you kike so yace Kuma ai zaki ga I love you a aikace ba a baki ba,ke wani namijin fa baya irin surutun nan a aikace kawai zaki Gani,kar kice Dan kinji Spark Yana fada Nabeel sai ya fada kowa da halinsa,wani ma da baya fada yafi me fadan sonki,wani fa duk a baki ne,ba shiri fa aka daura Baku fara soyayya ba to ki bari in kinje kinji bai ce ba sai kiji haushi. Shaheed ne ya shugo da ticket dinsu yace kuzo mu tafi,lokacin Spark Bai dawo daga Office ba suka tafi Naila ce ta kaisu airport sun samu kudi da kayan tsaraba sosai,suna sauka Nabeel yazo daukansu,da kyar ya iya gane Hidaya ce,tayi kiba tayi kyau tayi wani fresh sai walwali take yi. Ganin dan saurayi Shaheed gefen matarsa sai da kishi ya kama shi,ya danne kawai,Shaheed ya mika Masa hannu suka gaisa yace to shike nan Hidaya ku gaida gida a Nan zan jira flight na koma,Nabeel farin ciki yayi Jin Shaheed bazai je ma gidan su Hidaya ba,harda yi Masa godiya mun gode ya ja mota ya Kara gaba. Shaheed a cikin airport ya jira jirgi sannan ya koma Abuja,Yana komawa gidan Naila ta shirya Masa girki hadadde a dining ya zauna yaci abinsa suna Hira itama tana dining din,Spark ya dawo ya shugo da sallama,tace sannu da zuwa,Shaheed yace sannu da zuwa,Spark yace yaran Nan suna ta hankali Yan banza tuwo ya koya muku hankali,Shaheed yace uhm ya kamata Aunty Naila muje gidanmu Kiga yanda Mima zata sauke ki,dariya suka yi tace sai gobe zanzo ai,yace ki mana abin dadi ki taho da shi,tashi tayi ta nufi wajen Spark ta rungume shi ya dauke ta suka yi sama,Shaheed ko ta tasu baya yi abincinsa yake ci. Spark Yana Kai Naila ciki tace ya na ganka haka ne? yace Ina fa lafiya wani film na kalla American film a Office ana ta badala a ciki shi yasa na dawo ba shiri gida a bani nawa Nima,Naila ya dora Saman bed,tace nifa kwayayen nan naki sun fara kaini bango in baza su karbi cikin nan ba to kamar basa raye,dariya Naila tayi tace ai ni na hakura na daina ta tasu ma na barwa Allah komai,Spark yace kinga uwar bari kenan,ana fada miki bakya ji'' yanzu gashi kin hakura da kanki ciki Allah ne yake bada shi ga Wanda yaso a lokacin da yaga dama,Naila tace nifa na gaji da wa'azin nan naka sai kace kaima tuwo kake ci kullum,Yana lallashe ta kamar maye yace Indomie da Salat nake ci,dariya Naila ta dinga yi da ta tuna girkinta,tace dan Allah ka daina tuna min,yace kin Dade kina abin kunya Baby. Iman dai ta cika sati caf a gidan mijinta ba abinda ya faru kullum Annoor sai ya kawo,asibiti ma yaje an Masa duk wani gwaje gwaje normal yake,ya Sha magani shuru ba sauki,ya tafi Islamic chemist wani me kyau suka bashi nasu Ina shuru yanda yake haka yake,Iman ce ta same shi a bedroom Yana zaune Yana tunanin abinda ya kamata,tace tunanin ne dai har yanzu? Yace ba dole ba kullum Ina kallon Abu amma ba dama,dariya tayi tace haba Ango mene na tashin hankalinka Kuma? Kallonta yayi kawai yace ki shirya gobe muje asibitin Mamanki,Iman tace to Allah ya kaimu, ta zauna a gefensa tace abincin fa Ango ko man Amarya ya isheka?Annoor ya kalleta kawai,yace yau satinki guda Iman a gidan Nan da kalau nake da yanzu kin Saba da Sweetener ya karasa da tausayi,Iman tace harda yin kalar tausayi? yace ai ke yarinya ce shi yasa baza ki gane illar hakan ba. Washe gari Iman da safe da wuri suka ci wanka shadda suka sa fara kalar kayansu iri daya,suka fito kowa ya kalle su sai ya Kara,gidan ya kulle ko Ina sai me gadi suka wuce a tsaleliyar motarsa suna zuwa aka musu iso har Inda masu sauki suke,Iman ta hango ta a zaune yauma tayi tagumi ta zauna a gefe tayi shuru ga tarin tarkacen robobin ruwa Dana lemo a gabanta. Annoor ya Kalli Iman yace Kuna masifar kama kuwa da juna,Iman tace haka ma Kawu yace,sun Dade a wajen sannan suka je layin Maza,suna zuwa layin Maza Annoor ya hango wani mahaukaci ya cire wandonsa Yana fitsari Sweetener a mike gata katuwa ga tsayi,Annoor yace ji mahaukaci da kayan aiki,gamu Nan muna neman ta tafi wajen mahaukacin da bazai amfane ta ba,Iman baya ta juya tana ta dariya kamar ba gobe,Annoor yace muje ke kar na dinga ganin takaici a nan,har suka shiga mota Iman dariya take kamar ba gobe. Suna mota tana dariya yace kin dame ni fa da dariya wlh duk ranar da na warke sai kin gane shayi ruwa ne,Iman tace baka dai da bakin magana,gidan Kawu Taga ya nufa tace gida Kuma sati daya tal,yace ae mana shine dai dai ai,Bai fada mata wani Abu ba sai da suka shiga gidan,Haidar suka samu a compound a zaune ya tasa Laptop a gaba,ya gansu da mamaki yace har an fara fita lallai zaku Sha fada,Iman tace Ina Kwawna Yaya Haidar? Yace ban San Inda kwana yake ba wlh,dariya suka yi Annoor yace share shi muje suka wuce abinsu,Haidar yace an samu yarinya ana ta mata wayo ko sau nawa ake yi oho,Annoor Yana jinsa yace sau uwarka nake yi. Suna shiga ciki suka samu Kawu a Palonsa da Abba sun baje fruits suna Sha suna zuba zance,Abba yace 'yar Inna fushi take dani taki hakura daga na gaji da zaman lafiya na Dan jawo fada shike nan,ta juya min baya gaba daya babu mutunci,Jauro yace har yau fa banje gidan Amarya ba,Abba baki ya bude yace mene dalilin aurenta to in hakane? Jauro yace kunyarta nake ji,Abba yace Kai dai kawai soko,Annoor ne ya shugo bayan sun gaida Umma Habiba sun Sha fada dan me zai dakkota yanzu su fara fita. Suna shugowa Jauro yace me ya kawo ki Iman yanzu? Annoor yace ni nace tazo muje,Kawu gwara na fada Maka gaskiya,durkusawa suka yi Iman tana cewa Dan Allah karka fada,bayan sun gaisa Annoor yace Kawu ni dai tunda aka yi auren nan bani da lafiya,Abba yace toooooo....Iman taji kunya tace bari naje wajen Umma,Abba yace ke zauna sai anji gaskiya kece da laifi ko shine,Iman ta zauna badan ta so ba,Annoor yace Kawu tun kafin ayi auren gaf da an kusa biki ko Iman rungume ni tayi sai na kawo,Abba ya zaro ido Yana karkade kunne ae? Me kace? Jauro yace to fa muna jinka,yace idan Ina Jin sha'awa ko zazzafan hannu na ta rike sai na kawo,Kawu yace babu rabin zance,Annoor yaci gaba da cewa to nayi zaton ba matsala bace da aka yi auren ma haka,Kawu yace Amma kaima tun lokacin ai sai ka fada,yace nayi na asibiti da wasu na Islamic chemist shuru ban warke ba,Abba yace Allah ya rufa asiri ma ba a Dade ba yazo ya fada da sai dai aga matar ta Raina shi ba a San dalili ba,da yawa aure Yana mutuwa a irin haka amma mutane basa ganewa wasu su zagi matar ace daga aure har an sakota basu San dalilin ba,wasu Kuma su zagi mijin daga aure har ya saki matar. Jauro yace muje wajen Affa mana Baban matarka Kubra ai ya kware a wannan fannin,Abba yace kwarai idan kaga ba a dace ba to sai dai ayi na sihiri Kuma,Annoor da sauri yace a Ina ne zanje yanzu? Abba yace hanyar Jos ne daga fada sai ka tafi Kuma sai gobe Inshaallah,to Allah ya kaimu,yace Ameen,Iman kunya ta isheta,fitowa suka yi Iman sabo da kunya ta nace sai sun tafi gida. Hanan sati daya suka kwashe tayi aure aure ya Jibson ya turo da manya aka kawo kudi da komai ko lefe kudin ta karba kawai,sabo da aure da komai ba duk kudin ta karba,kayanta tsotsafi ba uwar data canja shi ta Kai,Jibson yace bai San zance,kafin ta tare da yamma ya shiga bangarensa yaga kayan yace baza ta sabu ba,bazan hau tsohon gado ba,tsohon gadon da wani ya hau ya gama iskancinsa a Kai bazan hau ba,ya kira Hanan Amarya yace wannan tarkacen fa? bazan hau tsohon gado ba fa gwara ma ku canja,karki sake a kawoki yau,Hanan takaici ya isheta tace sai kace wani mijinta kirki,ko an fada Masa sonsa nake yi,da yasan haduwar mijina na farko ai da baiyi magana ba ma,aikin banza Yan kudina Ina Adamawa zan hada na canja saitin kaya idan zan koma gidan Mohsin yasa zanyi asara. A ranar ta kukkulla da kudin da babanta ya bata ta hada ta siyo kaya masu arahar gaske ta siyar da waccen ta cika kudi aka bata,washe gari aka kwashe tsofaffin kaya aka saka sababbi da kyar,Jibson yaje ya Gani ya taba gadon yace ayyyaaaa a yau zan balla shi in ta tare,ya sake kallon kayan yace to duk da dai basu da Quality ai sabo sabo ne ko sabon Kashi ne sai anga banbanci. Baban Hanan ya gaji da ita dama ta ishe shi ya matsu ta sake aure,yau kuwa kawaye da wasu Dattijai yan uwan Ummanta da yamma suka kawota dakin miji tayi sababbin dinkunanta kala biyar da jakankunana da takalma kala uku uku harda mayafi da kayan kwalliya,bangarenta daban bangaren mahaifiyar Jibson daban. Bangaren mahaifiyar su Lubna suka Kai Amarya wacce ta Sha kyau tana kamshi,Mahaifiyar Jibson ta karbe su hannu bibiyu tare da danginta mata su biyar,har abinci da kaza ga ruwa ga lemo aka bawa Yan kawo Amarya Wanda mota Daya aka tura ta dakko su. Amarya aka Kai bangarenta ba laifi yayi kyau sabo da gidan mashaallah da kyansa ba Wanda zai raina ko Ina ya sha tiles. Sai dare aka Maida Yan Kai Amarya,Jibson ya shugo wajen Amarya 9pm na dare da kajinsa da kayan Sha,sai da ya fara kaiwa uwarsa nata sannan ya kawowa Hanan nata,ya sameta a zaune ta rufe fuska yace haka nake so naji gida ko Ina Yana kamshi,ko bude fuskar baiyi ba,ya bude Kasarsa yace karki ce ban miki Bismillah ba in zaki ci gata in na cinye