← Book details Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 87

Sashe 2

Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

1-5 https://hausanovels001.com.ng Official AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE UMMU LATEEFA Yana zuwa ya fito sanye yake cikin kana nan kaya masu kyau da tsada ba karamin kyau yayi ba,cikin station ya shiga,Yan sanda suka bashi waje ya zauna ganinsa da arzikinsa,idonsa sanye cikin farin glass,file dinsu suka dakko suna rubutu kafin daga bisani DPO ya fito da kansa,ya Kalli Annoor yace Annoor ko? Annoor ya harde kafa yace oho Kuma sanda aka ce ku kamani ba a fada muku sunana ba? DPO yace Kai ka shiga hankalinka nan gaban hukuma kake duk matsayinka baza ka zare mana Ido ba. Annoor jajayen lips dinsa ya tsotsa sannan yace,Ashe kasan Sunan nawa amma kake sake tambaya ta har sai na Kuma fada Maka sunana Annoor,DPO tsaki ya ja yace kasan akan me aka Kamoka? Silly question Annoor ya furta,Kaine ka yiwa wata yarinya Maryam ciki,Maryam budurwarka ai kasanta ko? Annoor yace ci me? ciki Kuma? Ni din? A mafarki naje nayi mata cikin ban sani ba? Ni Lollipop dina ace wata mace ta ganta,dpo Lion gareni fa,leader guda bani da budurwa wa zata yi leading bisa bed,wait wait wacce Maryam din? Maryam Sahabi secretariat dinka,Annoor murmushi yayi yace oh my God cewa tayi tana so na naji haushi na mareta shine ta min sharri,Ina da cctv a dakko a duba,Dpo yace yanzu zata zo ai,Annoor yace dama akan ciki aka wani Tara min jama'a,akan wani cikin shege, sa ace ma da gaske Nina mata cikin Kawu zai karba mene a ciki,but ba cikina bane akan me zan karba.....suna haka sai ga Maryam ta shugo wata katuwa ce sosai tana da kiba zata Kai 30yrs,tana shugowa ta fashe da kuka tace gashi Nan wlh shine yayi min ciki,Annoor ya Kalli Maryam yace yaushe? a Ina package dina yaje Hole dinki? Idanuwansa masu kyau da kwarjini ya zuba mata sai ta fara Ina..Ina.... Annoor yace a tura mu kotu wallahi sai kinyi bayani,Maryam jikinta ya hau bari da kanta tace Dan Allah ka yafe min karya nake so nake a saka ka aure ni,wata Yar sanda ta kwashe Maryam da Mari,suka turata cail aka kulleta,Annoor yace a kulleta kotu zai kaita shi sai ya karbi hakkinsa,yace haka kawai zata jawo naki auruwa a hanani aure, dama mu gidan namu gashi ga irinsa,Maryam kin shiga uku ba ni ba Kawu Jauro ma ya ishe ki tunda kika yiwa dansa sharri,Sallamarsa Yan sanda suka yi suna bashi hakuri ya fice ya wuce gida direct. Katafaren gidansu Dake G.R.A ya nufa,gate masu gadi suka wangale Masa gate,Wata Yar budurwa kamar Yar sadaka yalla da baza ta wuce 18yrs ba ta leko ta sama da sauri,tana ganin Motar Annoor ce ta fito da gudu sanye take cikin doguwar riga Yar kanti silver color da robar Ice cream a hannunta tana Sha kanta ba dankwali,gashinta ya sha gyara,da sauri ta bude Masa motar ya fito yana murmushi,rungume shi tayi tana murna tace Yaya sannu da zuwa,ya furta yawwa Iman Sanabe,Yaya Ina Ice cream dina? Kinyi Assignment yau ya tambaya? ta daga kai tana Shan ice cream,yace bude bayan motar ki dakko akwai chocolate dinki amma fa ki bawa su Nabeela nasu na sanki da rowa,dakkowa tayi tana murna ta bi bayansa suka shiga hamshakin palon nasu. Habiba Uwar gidan Jauro tana murmushi tace ka dawo kenan Dana,Annoor yace Ummi na dawo ya gida? tace lfy lau,Ina yaran gidan fa? su Nabeela suna daki suna karatu na manta ya kuke ce Masa da turanci ma? Annoor yace Assignment? tace ae shi suke yi,mutuniyarka ce dai ita tun yamma ta gama nata sabo da tana jiranka,sannan maganinta ya kare Doctor ka manta ne? Iman Sanabe kunya taji ta rufe Ido tace Allah Innah ki daina tam,Annoor ya Kalli Iman yace Sanabe an gyara min part Dina,Iman Sanabe tace yes mana yaya ai ka San ba fashi,Sama ya haura Iman ta bishi yace karki biyo ni,Baki ta turo tace Yaya na rasa me nayi Maka yanzu baka so na,ko Juyowa baiyi ba ya wuce abinsa,zama tayi a Palo tana fushi. Kawu Jauro ne ya shugo ya sha yard ka rantse ba shine me kudin ba,baya sa kaya me tsada Kuma ka ganshi a motoci na gani na fada Sam a jikinsa ba kama sai motocinsa zaka gane Yana da kudi,Yana shugowa yaran suka dinga fitowa suna furta sannu da Zuwa Kawu,Jauro Iman ya kalla yace Yar Auta ta waye ya taba min ke? Iman ta kwabe fuska tace Kawu Yaya ne ya tsane ni,Nabeela ce ta Kalli Iman tace ai itace ta fiye takura yanzu idan ta bishi bedroom sai tace zata yi bacci a can,Iman Bata san ta girma ba,Nabeel yace sai shegen iyayi da Sanabe,Jauro yace ku kyale min yarinya fa,zo mu tafi Iman Yar Albarka rabu da su,Iman tace Kawu me ka siyo mana? Kawu yace na manta ma Yana mota Nabeel ya mikawa key yace Je kwaso muku kayan Yana gaban mota,Nabeel ma saurayi ne matashi Wanda har ya girmi Annoor ma da watanni biyar. Kayan makulashe ya kwaso a ledoji kowa da nasa ledar daban dama sun Saba haka yake musu,har matansa biyu kowacce da nata shima Jauro da nasa. Jauro sai da ya bari kowa ya shiga dakinsa ya kwanta ya fito Yana bi daki daki Yana ganin kowa Yana Nan,Yana zuwa dakin Rahma bata Nan wayam,agogon hannunsa ya duba yaga har 12am. A palon ya zauna ya jira yaga yaushe zata shugo,Rahma a lokacin tana can club sabon gari sai 2am sannan gayu suka sauke ta a mota ,Me gadi ta kira a waya ya lallaba ya bude mata a hankali tana shugowa ta bashi dubu biyu cin hanci ta wuce ciki. Riga ce a jikinta gown da kadan ta wuce gwiwa ta dameta,tafiyar sanda take yi a hankali da haka ta shugo palo,Kawu ta gani a zaune Yana jiranta gabanta ne ya Fadi, a Palon ta tsaya,Jauro yace barka da dawowa,Rahma ta tsaya tana Sosa wuya tana wasa da yatsunta,zata yi magana Jauro yace Rahma ke gani kike wani kike wa? kanki kike wa wlh ba ni ba,Jauro ba ruwansa ko wajen Allah na fita kwas ko ba sabulu,Allah yana gani ban rayu da ku da wata manufa ba,nayi iya yina na baku Ilimi na addini Dana boko hasali ma na addinin yafi yawa akan ku mata,kunyi sauka Kun haddace littafan addini da dama Wanda mu azamanin bamu samu Hakan ba,sannan kin gama secondary yanzu na saki a university" dukkanku mata ba wacce bata Jin salary duk watan Allah sai na muku albashi na 30k ya ishe ku kuyi hidinmun rayuwa ba tare da wani namiji ya hure muku kunne ba,duk abinda kuke so na muku,na Baku ci da Sha sutura sai Kun zaba,me kike Nema Rahma a rayuwa? Laila haka ta dinga iskancin nan sai da na aurar da ita sannan na samu salama,ki daina biyewa Haidar kina tunanin Haidar idan yayi ma ai shi namiji ne ke kuwa mace ce,Rahma shuru tayi tana turo baki tana kunkuni ita an matsa mata,Kawu kawai wai Kai babu Wanda zai dan shakata shike nan sai a hanashi rawar gaban jantsi,Jauro yace kiyi rawar gaban rana ma ba ta gaban hantsi ba,watarana zakiyi nadama da dana sani tunda baki da hankali,ya mike ya fice Yana cewa kiji tsoron Allah shawara na baki. Rahma dakinta ta wuce tayi wanka ta kwanta tace daga na dan je club me nayi ni ba sex nayi ba fa", Dan kiss ne sai Dan kayan kirjina da suka isheni tumbul tumbul yo Dan an dan musu Excersise shike nan,so ake na zauna da su sunyi Dan Kam ba wani motsi,wlh bazan iya ba dole a motsa su,Ni Nabeel ma badan Dan uwana nane ba na jini ai ni shi nake so shi nake sha'awa tunda wancen masifaffen bama shiri,Annoor ai marina zaiyi gwara Nabeel, Haidar Kuma na Masa rashin kunya,kwanciya tayi abinta ta shige bargo . Haidar a mota abokai suka ajiye shi a kofar gida,dama idan har ya fita iskancinsa to baya fita da mota Yana dawowa katanga yake haurawa har da Ladder dinsa ta baya Jauro bai sani ba,ba a sanin sanda yake dawowa. Iman bata yi bacci ba tana palon su na mata tana kallon film kasancewar ba school,Haidar ne ya shugo Yana sanda zai wuce part dinsa,Yaga Iman harararta yayi yace ke daina kallo zan tattaka ki munafuka,dariya tayi tace Kai ka sani Yaya Haidar ai wlh sai na fadawa Kawu gobe,Annoor ne ya fito tunda ya shiga bedroom dinsa bai fito ba sai yanzu zai je ya dakko abincinsa ya samu Iman da Haidar suna Hira Yana dariya tana cewa sai ta fadawa Kawu yau ma sai dare. Fuska ya daure ya karaso cikin kayan baccinsa ya wuce su ba tare da ya kula su ba,Haidar bangarensa ya wuce Yana cewa ga masifaffe ne ya fito wai shi na gari,idan ba sai naci Uban Annoor kwana nan zan hada masa tsiya,Iman tace sai na fada Masa Allah,Wucewa yayi abinsa Yana dariya Dake Haidar Yana da fara'a sai dai akwai zuciya. Annoor ne ya dakko abincinsa ya hauro sama,Yana karasowa ya Kalli Iman yace wai uban me kike kallo ne? Iman tace American Film ne Yaya yana da kyau akwai fadakarwa da wa'azantarwa,a American film din ne akwai wa'azantarwa ke fa shashasha ce,tashi kije ki kwanta,Yaya a dakinka? Wani kallo yayi mata Wanda ba shiri ta mike tare da kashe kallon tace, Yaya maganin nawa,sai gobe ni yanzu bani da shi,waccen Dana baki me yasa kika batar da shi dalla wuce ki bani waje,bedroom dinta ta wuce,yace ki sa key bana so naji kofarki a bude tace to sannan ta rufe shi ya zauna Yana cin abinci. Yana gamawa ya mike yayi knocking dakin Nabeela tana ji tasan shine tace Yaya Ina nan ka sani,yace Good ayi addua, bedroom din Rahma yaje yasan itace Bata Jin magana yana knocking tace na dawo Kawu ma ya ganni,yace Okay ayi Addua ya juya wuce dakinsa ya kwanta. Jauro kuwa yau Kwanan Na'ima ne tana dakinsa suna kwance,yace Amarya,Na'ima tayi murmushi tace na'am Darling,Jauro yace idan bake Na',ima bazan Kwan gida ba, rayuwa sai da Na'ima,Na'ima kece dai, akan na rasa ki Na'ima gwara ace min Dan jaki,Na'ima sai dadi take ji tace Dan ma
Chapter 2 · 0% Book details