← Book details Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 87

Sashe 72

Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

hanasu ficika suka baku bada yawu na ba,kuci iya nawa da zan sa a kawo in baza kuci ba kuyi bara ma ku kuka sani,ke da Yan uwanki duk babu na kirki Kun bi ku gallabi kowa,gidan Yayanki ban hanaku kuci abincinsu ba ke kika haife su amma abinda zan iya ni shi zanyi,kin ganni karki ce ban fada miki ba Aure zan Kara a Nan na samu mata,Yana gamawa ya kashe wayarsa. Mima tana rike da waya galala a hannunta Arham ya shugo tace na mutu na lalace Arham,Arham yace haka gawa take tana magana wlh da ranki kice wani kin mutu kina nan daram Kuma a zaune kina numfashinki hannunki na motsi har kuka kike fa gawa tana kuka ne sai kice kin mutu Kuma,lalacewa Kuma kina gidan mijinki kinci da wake kin koshi da kibarki ai baki lalace ba,sannan gaki a dakin mijinki babu kwakwaran kwarto Ina kuwa kika lalace Mima ki daina fadar haka, lesbian din Nan da ya addabi al'umma ba yi kike ba ai kuwa baki lalace ba wlh. Arham ya jawota jikinsa Yana durkushe a gabanta yace ga wakilin Papa yi shuru uwata tafi ta kowa, Spark ya boye dariyarsa kawai yace kiyi hakuri Mima ki dawo gidana ki huta,Arham yace in ta tafi waye zai mana tuwon wannan yaran me suka iya. Mima tace ko mutuwa zaku yi sai na tafi na huta a gidan Dana,Arham yace to bari na shirya Jakata Nima,Spark yace to yanzu mene amfanin barin gidan nan kawai daga Jin haka,Mima tace indai bina zakuyi na fasa,Arham yace yawwa Dan Allah karki tafi shi kanshi idan Papa yaji kin tafi zai sake zamansa ne amma in yaga duk wahala kin jure zai dawo,Yar rashin Hallare ce ki jure zan saka Ido sosai akan ki barin irinku suna yawo a gari miji baya kusa hatsari ne,dundu Mima ta durma masa,sai da ya gantsare Yana Kara,ka maidani sa'arka wai Dan ubanka,to kiyi hakuri amma ki jure mu zauna Mima tace kana da gaskiya Arham indai zai dawo komai ma zan jure,Arham yace yawwa sai ayi ta hakuri Hallare tayi yaji,Spark yayi dariya Kuma tana sonta Ina tausaya mata,Mima tace mene Hallare Kuma? Suka ce ba komai,Arham yace wannan kukan ma duk ita ake wa na sani,Mima tace wlh duk yanda akayi ba abin arziki bane Hallare ko me ku tashi Kai Arham Kai ma so kake ka lalace,yace Misam ne danki ya lalatani sanda naje gidansa suna ta iskanci a gabana,tun daga ranar shike nan na kwace. Yau anci shinkafa da wake babu gidan Wanda suka je. Washe gari kuwa ragowar shinkafar Mima ta dafa fara ta yo cefane ta musu shinkafa da Miya nan ma harda cabbage ranar kafin dare sun cinye shinkafar tasss.....da dare Kuma ta basu kudi suka siyo Indomie kowa ya dafa. Washe gari sai tuwon Masara miyar Kubewa basashiya,kowa Yana tsaki haka suka cinye abinsu kwana uku Spark da su Misam basu ga kowa a gidan su ba. Hanan anyi gyara an Kara kyau kawarta Lubna tazo suka tafi har gida wajen wannan guy din,Hanan tace wai ya sunansa ne? Lubna tace Jibson ake ce masa,suna zuwa gidan na rufin asiri ne a waje suka tsaya suka tura yaro ayi musu sallama da Jibson,ba a Dade ba ya fito sanye cikin farar jallabiya fes da shi wankan tarwada,kansa yasha askin kwal kwal sai kyalli yake,Hanan tace sai kace zan Kalli fuskata a kanka sabo da tsabar aski,Ina yini,ya amsa yace ya akayi idan Maula kuka zo Dan Allah ku tafi nidai kudina suna accnt Tarawa nake bani da kudin yin sadaka yanzu Nima nema nake,Hanan tace a'a dama na ganka rannan ne naji ka kwanta min a rai Ina sonka Dan Allah ka aureni,Jibson tsaiwa ya gyara yace duk Wanda kaji yazo yace ayi musayan kaya to ya tabbatar nasa baida kyau,Allah yasa naki da kanjamau ai dole sai anyi test ba a aure da ka yanzu sabo da haka ka so me sonka nima Ina sonki Kuma wannan itace babbar sadaka da zan baki wato kaina,idan ban aureki ba ai nayi asara,na auri wata banza ma Yar talla bare ke,Hanan tace Alhmdllh na gode ni bazawara ce Ina da yarinya Daya,Jibson yace ko yara talatin ne da ke zan aureki,ai mu ba a taba yi mana tayin aure mun fasa ba baza mu ba sunna kunya ba,sabo da irin wannan tallafi fa nake tara kudi Ina ajiyewa ba ci ba sha na aure ne kawai kadan nake kashewa,karki damu za a aureki cikin daraja,Hanan tana ta murna a ranta a fili tace to nan da yaushe zamuyi test din lafiyar yace jibi ki shirya bani address din gidanku da number dinki tace to,ya shiga ciki ya dakko mata littafi karami ta rubuta Masa ya karba suka tafi,Hanan tace gaskiya Dolo ne Wawa wannan da wuri zai sake ni,Lubna tace kina cewa ya sakeki zai sakeki haka yake ai shi. Abba ne yau ya fita tun sassafe yaki dawowa gida ya bar unguwar yace yau sai ya sa Kubra kuka sai sunyi fada shi Kam ya gaji da wannan zaman lafiya haka abin yayi yawa kullum sai a dinga zama lafiya Dan cacar bakin ma'auta sai dai naji a makwafta gashi Nan ko wanne gida ana wayyo wayyo da lamarin aure,amma ni kullum na shugo sai dai a tarbeni ayi min abinda nake so,Nima kullum Ina yiwa Kubra dai dai, Dan canja hali bana yi wlh yau bazan koma gidan ba sai tsakar dare. Wata unguwar ya tafi kawai ya samu majalisa Dattijai ba Wanda ya sanshi shima bai San kowa ba ya zauna,Suna ta hirarsu,wani dattijo yace ai yau Balki ta fara fada ban Bada kudin manja ba na fice,ai duk masifar mace kawai ka fice ka bata waje,kullum kawo kawo mata ba tausayi ba Imani,Abba yace me yasa ka aureta kasan baza ka iya ba,magana ta Gaskiya ka hanata kudin manja sabo da tsiya ka fito Kuma ka bar gidan wannan zalunci ne ,to jira kake ta Nemo kudi ta siya tayi Maka girki kaje ka ci,Kai wannan bai kamata Balki tayi maka biyayya ba wlh,Kaci ka koshi sannan ka koma Balki ta sauke ma sha'awa indai haka ne ka fadawa Balki tayi asara a rayuwarta. In banda asara ma me ta gani ta aureka,Baku da aiki sai ku zauna Kuna gulmar matayenku da munafuncin mutanen unguwa,Dattijai suna jinsa mamaki ya kamasu Bako yazo yana shigar musu zance. Wani a cikin dattijan Yace Malam Rabiu kaji matar Liman Yusha'u ciki ne da ita? Jiya baka majalisa ta wuce muka Gani da idonmu,ai ta Nan ta wuce tana ta ja har ya fara tsufa ma,Abba yace Allah ya sakawa Liman da matarsa kallon matarsa da kuka yi da Kuma gulmarsa da kuke yi Allah ya saka Masa,ana zaune sai ga liman yayi Sallama a gabansa Kuma sai fara'a ana girmama shi Malam Liman ka karaso ya iyalin? Abba baki bude ya kalle su,yace Kaine Yusha'u Liman? Liman yace nine lafiya? Yace yanzu suka yi gulmarka data matarka sunce ta wuce jiya ta nan sun ganta cikinta ya fara tsufa suka kwashe da dariya. Liman yace ai majalisar Nan munafukai ne kamar ba dattijai ba,Abba tashi yayi yace wlh gwara na koma gidana bazan iya zama a nan ba,ya tashi yayi tafiyarsa Kuma ba gida ya tafi ba har sai da dare yayi a masallaci yake samu yayi sallarsa. Unguwarsu ya dawo ya shiga gidan abokinsa sun Dade har kusan Sha biyu na dare nai dawo ba,Yar Inna taga shuru shuru har Sha biyu,ga wayarsa bata shiga ta kira Mohsin ta sanar Masa. Hankalinsu duk ya tashi Mohsin wurin 12:30am sai ga Abba ya shugo gidan ga yara suna gidan Naila ba kowa sai Yar Inna sai karamar da take goyo tana ganin Hashimu ya dawo sai murna harda rungume shi tace wlh ka sani kuka Ina ka tafi haka? wayar Mohsin ta kira tace ya dawo lafiya Lau sai lokacin hankalinsa ya kwanta shi da Beauty,Abba yace kinyi kuka da gaske Yar Inna? Kubra ta Harare shi tace ban sani ba,Abba yaji dadi shi dama haka yake so suyi fada kawai,tace wanne kuka ne banyi ba sabo da Allah tun safe har dare 12:30 ba dole na zaci ko kidnapping Dinka aka yi ba,gaskiya karka sake min irin wannan wlh wannan ai ba yi bane,Abba shi dadin masifar Yar Inna yake ji,yace ko banza dai munyi fada yau amma kullum sai tarairayata a dinga tarairayata Ina ta yin soyayya, Dan Allah ki kwana a dakinki yau ke kadai Nima na kwana a nawa muyi fada kawai,nidai Allah ya gani hakurin nan ya isheni da zaman lafiya yayi yawa Ina za a Kai shi haka rayuwa ba jarabawa ba dadi ni bazan iya ba. Dariya ce ta kama Yar Inna tace ohh dama duk Dan muyi fada ka tafi? yace ae gaskiya zan fada a gari na dinga yawo har dare yayi na tafi gidan abokina na Kai har kusan Sha biyu na dare sauran lokacin na karasa a masallaci,tsakani da Allah fa Ina zan iya kullum sannu da zuwa ana kaffa kaffa dani dadin yayi min yawa,babu matsalar da zata zo tasa na dinga tuna mutuwa, shi wannan Mohsin da Ina fargaba bashi da kudi yazo ya samu kudi,matarsa ba ta gari ba yazo ya samu ta gari Beauty,Naila tana prison Ina damuwa Allah ya yaye min ta fito ta auri me kudi tana zamanta lafiya Kuma babu rikici ba komai kullum shuru,ke nan kin gyara halayen ki abin naki ya wuce misali naga alama so kike ki tsallake siradi da gudu a lahira,gaskiya mu dinga fada Nima ko Hallare ta huta,Kubra tace Allah ya shiryeka,Allah yasa ka nutsu tunda aka haifeka a haka ai baza ka shiryu ba. Kuma mutumin da rufa Maka asiri nayi na aureka aka tura min Kai dole,wacce wahala ce ban Sha ba ni na dauki nauyin yarana da Kai har suka girma Ashe Kai kudin Makka ka Tarawa Danka Kuma duk Shekara sai kudin aikin hajji ya tashi dole ka Dade kana tari,Abba yace yawwa Maza ki zobe ladanki,tace baza ka godewa Allah ba ya fitar mu daga wahala yanzu yayi mana ni'ima,tunda muka taso muke a wahala da talauci da jarabawar rayuwa, yanzu Allah ya yaye mana"
Chapter 72 · 0% Book details