← Book details Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 87

Sashe 57

Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

dai an taru ga Yan bariki abokan Yahuza,Yahuza yace wai Ina Liman ne yace gani na karaso,idan baza ka daura ba sai ka fada mana,ai kasan ni ba iya khudubar Nan nayi ba da nasan yanga zaka mana da tuni ni na daura da kaina haba sabo da kana da addini da ilimi sai kayi mana yanga, Anji to kana Jan Sallar masallacin juma'a ana biyanka albashi ai ba kyauta kake Jan Sallar ba,gomnati biyanku take,Kuma duk kudin da ake biyanku harda na al'umma idan an kiraku radin suna ko daurin aure gomnati ta biya ku. Liman yasan hali ya share Yahuza ya samu waje ya zauna mutane da yawa a tsaye suke,dangin Papa na kauye da su aka zo sai Baban Misam Wanda shima Yana ja gaba,Abokan Papa duk sun wakilci Papa gasu Nan da yawan gaske,taro yayi taro,haka na Misam ma an Sha mutane,Yahuza sai wulakanta Ikhram suke suna nunawa bata da gata,haka bangaren mata kowa yazo wajen sai ya gane Ikhram bata da gata,dangin Ikhram da suka zo mutum biyu ne rak suma ba wani dangi na kusa bane,Ikhram tana ganin wulakanci tunda bikinta ya matso,matan Uncle suyi mata shima haka,Rafeeq ya bawa Spark labarin Ikhram tun a gidan kafin biki, tausayi ta bashi,ance a yanke sadakinta Yahuza yace ai ba tsada zata yi ba ku Bada dubu Hamsim ai tunda aka zo tsaida rana na fada muku, kamar ma a make yake baya hayyacinsa bakin cikinsa sadaki bazai ci sisi ba shi yasa ya Fadi kudi kadan. Rafeeq yace ni na Kara Sadakin matata dubu Dari biyar zan bayar,Rafeeq ya tara kudi sosai sabo da Iyaye mata me dubu Dari biyu,me dubu Dari me dubu Dari da hamsim etc Mima dubu Dari uku ta bashi tace ko baida kudin sadaki lallai ayi bajinta,Yahuza ya rude yace to kawo sai a boye mata ko wani abin sai a siya mata,Rafeeq ya zaro waya Nan take yayiwa Ikhram transfer a accnt dinta ya nunawa shedu kowa ya sheda yace an bawa Amarya abinta,Yahuza ya fara zare Ido Yana Jin haushi yace wato ni ba'a yarda dani ba to ta fito ta daurawa kanta auren na fasa a tashi a watse a bar min gida,Spark yace Kai Malam saurara karka mana kwaya a nan mun fika hauka Liman daura mana aure Ina dangin Ikhram? wasu Dattijai suka ce gamu Allah sarki yarinya, Spark yace ku mana walicci ai Kuma danginta ne ya halatta Liman daura muje,Yahuza ya mike Yana masifa wallahi ba a kofar gidana ba,Spark yace gidan haya ba har gidane da Kai,idan ban bugaka da kasa ba shege nake wa zaka mayar Yan iska,Yahuza yace Allah? Arham yace Dan anga bamu sako kakin sojoji bane,Khalid hularsa ta manyan sojoji ya dakko ya buga,sai Yahuza yayi mukus ya koma gefe yace bazan sheda ba to wlh,Yana gefe Dattijai aka daura aure sharrr, ana daurawa yaga motocin sojoji suna ta dira a gidan Wanda basu zo da wuri ba,bataliya bataliya,harda escorts din Khalid Dana Spark,Nemar Uncle aka yi aka rasa ya fece,ana ta cin abinci ana shagali,Rafeeq sai washe baki akeyi yana amsa Ameen Ameen,makadan karuwai sake dawowa suka yi suka saki Dan asharalle yau kuma, Rafeeq yau dai yayi rawa shi daya aka rufe shi da liki,kawai Dan yaji Dan Asharalle Yana wake Ikhram Yana kiran sunanta a wakar ya fara rawa dama shi dancer ne,Amarya ta fito da tawagarta ko wacce ta ci wanka aka sake sabon shagali su Stella ana ciki ana takawa,Ikhram harda shiga suyi iri daya da Rafeeq, rada ta Masa a kunne sai tasa hannu ta matse babbar rigarsa ya dinga murga duwawu,Kamal idonsa ya rufe ya juya yace ana abin kunya a wajen nan,Spark yace bazan iya kallo ba kunya zata kashe ni,Naila ta dinga dariya,Misam kuwa cewa yake ana zubar da mutunci a wajen nan yau. Su Mima ana can ana shagali suna ta faman zuzuta Amaryar Rafeeq,Sai gani suka yi videos na tashi a sama,social media ana ta watsawa duk Wanda yaje da kalar nasa,wayar ta kashe wai kar ta ganowa kanta Amaryar Misam bata so ma ta ganta, bangaren Chika kuwa suna kusa tuni anje daukan Amarya da motoci biyar sabo da kawayen sai an gama na Rafeeq zasu taho,11am aka tafi da Amarya Abuja,ana gamawa Yahuza yace da su Asabe lallai yau su dauke Amarya baya son bikin,washe gari aka yi za a kaita amma yace Sam ba a isa ba,Spark yace masu Kai Amarya su shirya ba damuwa,Asabe tace dole muje muga gidan Ikhram ko karyar kudi aka yi mana,suka shirya ita da Amarya yaran suka zubewa Yahuza su suka fito,Amarya Ikhran tace ni ba sai gobe akace ba kayana ma ban hada ba,Kuma yau na gayyaci wasu duk zasu zo min biki,Kun San fa sabo da sana'ata Ina da mutane,Asabe tace to su koma gidan ubansu mu yau zamu kaiki idan Kuma kece da kanki to ki bayani. Ikhram ta zuba uban gayya yau zata yi shagalinta ta kashe kudin komai amma ance dole a kaita yau ta saka kuka,Asabe tace in zaki shirya ma ki shirya,Naila tace ke dalla daina kuka shirya mu tafi can ma fa dinner za ayi ta Misam,Yau ta Misam za ayi,duk wani tarkacen Amarya Naila da Beauty sun hada komai an zuba a mota Daya,kayan Lefenta ma a mota daban ba abinda suka bari nata,ta shiga wanka tana ta kuka ta fito ta shirya a haka, kuka yaki karewa sabo da ita tayi gayya yau Wanda baza su je Abuja ba,ta Bada kudin Abinci da komai na saukar baki,ga abinda ake mata a cikin mutane Yan biki,haka ta shirya Cikin wani material me tsada,ta zuba kyau Yar kwalliyar ma baya baya aka yi sabo da hawayenta. Haka ta fito kawai Asabe tace to lulluba mayafin a Kai,ta lulluba ta rufe fuskarta ta fito Spark yace iya motocin da zasu cinye shi ya basu basu fi ma mota biyu ba zuwa uku mutanen duk kawayene, dattijan Asabe ce kawai da Amarya sai Maman Chinyere,Su Stella da yare motar su daya,sai kawaye,Wanda suka bi motar mazan,iya Yan gidan su Rafeeq ne su a Jirgi zasu koma,Jirgi suka bi su,sabo da son Kai Spark ya dauke Nailansa,ta shiga mota yace ke fito kunyi yawa a motar muje ki shiga waccen,sai da ya bari motocin sun tafi ya tasa keyarta suka tafi a jirgi gata ga shi. Spark suna sauka ya Kira Mima yace Amaryar Rafeeq ma suna hanya a jirgi zasu zo,Mima ta rude tana ayi a gyara gidan nan tana yiwa Yan aiki masifa babbar Amarya ta kusa sauka,karamar Amarya su suna mota ana gwajab gwajab a hanya ayi a gyara min gidan Dan Allah. Ta samu mutanen kauye danginsu dake su ta Raina dan Allah ku tashi haka bakwa gajiya da shinkafa ne ku,ku tashi za a gyara gida,ta sa Yan aiki suka fara aikin gyara ko Ina sai kamshi,yaro bai Isa ya wuce ba zata fara masifa karka bata min gidan nan Amarya zasu sauka yanzu. Su Mima basu San ma tuni an kawo ta Misam ba tana gidan Marikinsa an sauke su da karramawa da mutuntawa abinsu idan anje Dinner an dawo Kuma za wuce da ita gidanta baki Kuma su kwana a gidan Baba da safe a Maida su. Spark tuni sun dawo Naila har ta wuce gidanta ma ta gyara kayanta ta fara hada kayan da zata saka anjima dinner din Misam ta Rafeeq sai gobe,Rafeeq tunda yasan haka tsoro yaji ya kira Spark yace karfa suje gidan Mima suyi musu wulakanci su Asabe su tafi da abin fada,Spark yace ai baza a kaita gidanba,gidan su Islam za a kaisu sai ace sun wuce gidansu na Abuja sai gobe a hadu a dinner,Kai Kuma idan kaje Dinner din Misam kar ku shiga tare da Ikhram,kowa ya shiga daban,Rafeeq yace to Alhmdllh,Spark haka ya kira Mima ya fada mata yace ai suna gidansu na Abuja sai gobe sunce za a hadu a dinner,Mima tace manya kenan,ai komai na manya na daban ne,to ta Misam din baza ta zo ta gaida uwarsa ba? Spark yace yace zai kawota bayan sati daya da biki tunda kunce ku ba bikinsa kuke ba me zai kawota Kuma tayi,Tsaki ta ja tare da kashe wayarta. Da yamma kowacce ta hade an tafi dinner din Misam,Su Mima Allah Allah suke suga wace,Amarya kyau sai ka Santa sosai da ka ganeta sabo da ta Sha kyau iya kyau,Dangi suka fara dira kowa mazan ma an cika sosai an Sha kyau wuri ne me tsada da kyau komai yaji,Mima tana shiga ta dinga kallon Amarya tana ta kallonta kamar mayya,Ikhram ce ta shiga ta samu waje kusa da Beauty ta zauna,Rafeeq ma ya shugo daban ya zauna kusa da Beauty su Mima basu gane ba,Mima kirji ta dafe lokacin da Chika tayi murmushi tace na shiga uku me zan gani? Chika ce fa ta mike ta dinga bin dangi tana cewa Kun ganeta Chika ce Yar aikina,ita ya auro yarinyar da ta ci min mutunci ba irin rashin kunyar da bata min ba,wurin ta tunkara a hasale,Spark ya riketa tana Fisgewa ka sake ni inje Inci Ubanta,wlh sai Misam ya sake ta bazai taba zama da wannan ba idan ba haka ba wlh sai na Masa baki,ni zaku rainawa hankali ku dinga min iskanci,shi yasa aka Hana mu San wace,aka tsaya ana ta kallon Mima,Spark yace Mima wai mene haka Dan Allah Mari ta kwadawa Spark tace sake ni bakin munafuki,ai da kai ake munafuntata shashasha,Spark dafe da gefen kumatunsa Chika ce ta yafito Naila ,taje wajenta tace kice dj ya sakar min kida a kira Amarya da Ango ana bata mana lokaci,Naila taje ta isar da sako Dj ba ruwansa ya saki sauti sannan aka kira Amarya da Ango,Mima tana ta balbali ita kadai ko kunya ,Chika Kuma suna fitowa ta rike hannayen Ango shi Kuma ya rike mata kugu suna takawa a hankali ana ta ruwan liki,sai dangi matan dukkan su suka fara tashi suna zanzarewa kafin kace me duk sun bar wajen har Mima,shagali ya Kara dadi ranar anyi show,Spark sai shafa kumatunsa yake Inda Mima ta mare shi,yace da Naila Baby duba min ko ya kumbura,Naila tace maganinka kenan ai,haka zaki ce kenan? ae mana ta furta tana shafa masa wajen. Ango
Chapter 57 · 0% Book details