Sashe 39
Tantiriya A Gidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ce ta shugo dakin duk fadan da suka yi amma ta iya zuwa tace yaro Kuma gobe Kawu zai Kai ni wajen Mamata,bazan dawo da wuri ba,sai na yini,Annoor ya kalleta sanye take cikin English gown peach doguwa amma an wani tsaga gefe da gefe,yace banji me kika ce zo ki fada min,Haidar yace kinji kunya Iman yanzu kika gama kuka da masifa kika ce babu ke ba shi amma har kin manta,Iman fari tayi tace ai zuwa nayi na fada Masa yaji haushi,Annoor murmushi yayi yace a dawo lfy,ya mike yace Office zan koma fa,zan cirowa wata Baby a cikinta Ina da operation,Iman tace baza ka cire ba kazami ka tabo jini ka dawo mana gida wlh karka sake taba ni tunda Jinin haihuwa kake tabawa,ba wacce za a cirewa Danta, a sa wani ya cire mana sai Kai,Kuma shike nan sai ka Kalli cikin wata,kofar ta tare wai bazai fita ba,Haidar yana dariya yace hmm muna kallo a gidan nan matsa min na wuce ko wlh na dauke ki nayi waje dake,Matsawa tayi ya wuce ta sake rufe kofar ta babbake,Annoor yana zuwa daukanta yayi cak ya sabata a kafada suka fito tana dariya tace Kawu zai gani,Bai ajiyeta ba sai da ya kaita wajen Kawu ya ajiyeta ya wuce Bai ko tsayawa baiyi ba. Abba ya Kalli Jauro yace za a iya girgizar kasa a gidan nan,wlh kayi ka daura auren nan kar a sake na biyu,Jauro yace yau zanje na sanarwa mahaifiyarsa tukun sai mu tsaida rana,yace ya fiye Maka dai,ya mike yace Yar Inna ta kirani Ya daga wayar yace hello 'yar jajir ya Kalli Habiba wai ita yake wa ba'a,Jauro yace zo nan Yar bakas....Habiba tace kwayi Kwa gama ko a jikina wlh baza kusa ni shiga kanti ba,Jauro yace da an fara kula wasu Kuma kuji haushin mutum,sabo da kullum Kuna tare da shedan ko Baku duba wayar mutum ba akwai kyautar da shedan yake Baku ta sirrin miji sai ku dinga ganewa idan ya kula wata,an rasa ta Ina kuke sani idan ba shedan ba wa zai dinga nuna muku. Abba waya yake da Yar Inna harda tambayarsa me za a dafa Masa,Abba yace karki sa nayi kuka Yar Inna, wai duk da kin iya wannan kulawar kika barni ina ta kallon mata a runfa,na dinga arahar kayan Miya a banza,na tafi wajen Batoola na koya mata girki ta karu Dani a banza ta yaudare ni, Kuma sai yanzu kika nutsu,Kubra dariya tayi a hankali tace Badan yara na kusa ba da na fada Maka wata magana,Abba yace yo shiga daki mana naji,tace a'a a barshi,yace ke banza ki tsaya kallon ruwa kwado ya miki kafa, ana koya miki yanda ake mallaka sadaka bakya daukan haske. Kubra tace to tun yaushe na mallakeka Kuma,yace inji wa? to zance ma na tafi yanzu,dariya tayi tace da rana haka? Jauro Yana Jin komai a wayar tasu, Bazawara tana da wani lokaci ne ita da take neman agajin gaggawa cewar Jauro Yana daga zaune ya bada amsa,ya sake cewa ai Bazawara Emergency ce me zaman kanta,Kubra dariya tayi tace naji Inda kaje ai. Abba ya harari Jauro yace ka tona min asiri Ina niyyar in bata kuka yau,na dade banga kukan Kubra ba ka wani tsoma baki,Jauro yace Kai Nan har kukanta kake son Gani? Abba yace na dare kawai take yi na soyayya ,Habiba tashi tayi tace kunfi karfi na nikam,Jauro yace kashe wayar kaji,Abba yace Jaa" Kubra ta amsa na'am yace ki dafa abinda kike so Ina so nima,tace to karka ci komai ka dawo da wuri Kuma,yace yanzu kuwa sannan ya kashe wayar . Jauro yace nima bakina kaikayi yake,Abba ya furta to Sosa abinka mana,yace mutuniyar Habiba ka ganta shuru shuru ko heeey kiyaye ta,idan kana neman Original Harija to Habiba ce,har fada mata nake nace Habiba a dinga raga min na tsufa yanzu,Abba yace Kai bakaken mata akwai quality shi yasa wasu basa son farare,ni kuwa gwara fara ta Ina kallonta ma nishadi nake,Jauro yace af Nima fa ka zugani dagewa zanyi na auro uwar Annoor zizar mata,Abba yace Nidai ba ruwana Ina bayan Habiba kar tace na ci mata fuska,Jauro yace karka fada mata fa nasan halinka,Abba yace wlh bazan iya ba ban dauki alkawari ba a ko yaushe zan iya fada ba ruwana. Sai da Habiba ta fito zata wuce Abba yace Habibalo aje a fara gyaran jiki mun fara neman aure kar wata tazo ta kasa ki a wajen Jauro,wlh ki daina gidadancin nan Habiba ki shugo zamani tam idan baki ji bari ba ai Kya ji hoho nidai na fada miki,Jauro yace ki rabu da shi wannan Kam yanzu ba hayar gida ya kama a Zaria ba,gidan ya siya sosai ya tare a Zaria,Habiba tace ai Kai Jauro ba a rabaka da aure,duk namijin da ya Saba da mata biyu baya iya hakura a zaune take ko ya saki sai ya auri wata,wlh ka auro abarka ni ban hana ba indai zaka samu nutsuwa ai yafi ka nemi na banza,Jauro yace Allah ya kawo ta gari,Dan shi da Abba basu muna muna. Yau ma Habiba ba yanda bata yi ba akan Abba ya tsaya yaci abinci yace shi Kubra tana jiransa bazai ci ba yaje yayi mata laifi, Jauro Nabeel ya sa ya kaishi gida a mota,Nabeel tunda ya dauki Abba a mota suke hira Abba Yana ta bashi dariya sosai,Sun kusa karasawa gida Abba ya hango Hidaya sanye cikin uniform tana ta sauri zata koma gida,rage gudu a wajen yarinyar can 'yata ce Abba ya furta, Nabeel yayi slow Yana tafiya a hankali a saitin Hidaya,Abba yace yi mata horn,Nabeel ya dinga dannawa Hidaya horn,ta zaci samari ne ta ja tsaki tana dauke Kai. Abba dariya yayi yace ta bature yace Goot (Good) yarinya ta tayi hankali ta dauki fada ashe,dariya Nabeel yayi tare da sake danna horn,ta juyo a fusace zata yi masifa ta ga Abba ya sauke glass,baki ta washe tace Abba,yace daina murna ba motata bace hanya aka rage min,Hidaya tayi dariya ta mikowa Abba hannu ya miko nasa ya rike hannunta ya saki sabo da motar tana tafiya kadan kadan,Abba ya furta sai kin karaso,babban yatsa ta dagawa Abba tana daga Masa Kai tana murmushi,Nabeel suka birge yace Ina ma na San nawa iyayen,amma ba komai ai Ina da Kawu yafi ma wasu iyayen,Abba yayiwa magana yace a dakko ta? Abba yace kyaleta bata ji Hidaya Yar rigima ce,da Naila ce da gudu zance a dakko min ita,amma gwara ta Sha wahalar rayuwa tafi yin hankali,Nabeel glass ya dage yayi gaba,Abba ya kalle shi yace Kuna adon suma yaran nan,wannan uwar suma haka kamar ka dakko kaya, badan kana da haske ba ai da bazan ka ganu ba,gaka Nan dan Fulani da Kai mashaallah. Nabeel murmushi yayi yace ai kudi ake kashe mata Abba,Abba Yana ji yace Uhmm Yan mata ne suke so shi yasa kuka dage da adon suma,da Yan mata zasu hada baki duk me suma da gemu baza su soshi ba da gudu zaku sauke gashin Nabeel yace ai Abba yanzu yawa ne ace baka da Dan gemu da suma,da yanzu ne kwantai zaka yi wlh,Abba yace karya kake ni nayi kwantai, kasan waye ni kuwa a wajen Yan mata sanda Ina saurayi? Aji ne dani sai gajiya aka yi aka min aure da Yar a bokin Babana sabo da in tsaya ma Ina kula wata yawa ne nafi karfin su,Yan mata Allah Allah suke Hasheem ya kulasu ni kuwa Ina,Abba harda gyara sunansa Hasheem,yace har abada yaro baza ka auri kamar Yar Inna ba a kyau,duk na muku Zarra,ai matan yanzu duk Yan cuwa cuwa ne,komai sai sunyi cuwa cuwa,samun irin Yar Inna sai dai ka tafi saudiyya,Kuma kace zaka je saudiyya wlh zaneka Larabawa zasuyi kace zaka auri matan da suke garin Manzo,gwara ka fara kamun kafa na baka Jinin Yar Inna ko kayi dace. Nabeel ya dinga dariya kamar me,haka Jauro ma yake musu kuri iri iri,musamman sanda ya auri Na'ima Matashiya,ya dinga ce musu ko ku Albarka baza ku samu irin Na'ima ba matar manya. Har kofar gida Nabeel ya sauke Abba ya mikawa Abba kudi yace Abba gashi a bawa yara,Abba yace ka bawa dai uban yaran,bazan basu ba sai dai na San musu kudin makaranta da kudin cin goruba,Dan yanzu ma Allah yasa na biyawa Mohsin Makkah ne shi yasa zan iya bawa Yar Inna Kudin nan nace taje ta Sha shagalinta amma da lokacin da ban biya Masa bane kwandala baza suci ba ko zasu mutu,nima sai dai su ciyar dani,Kai tabara nake yi a da,dariya Nabeel ya dinga yi yace to na fasa a bani kudina,yace ai ba kyau ayi kyauta a karbe ko baka sani ba ne Malam bai koya Maka ba,dan Allah tafi gida,Kubra ce ta leko tana kira Zara data fita da gudu tana cewa indai kika dawo sai na zaneki,Abba yace me leke dan wuta,dama leke kike yi idan bana nan,Kubra ciki ta koma ta barshi,sallama suka yi da Nabeel ya koma gida. Iman sai dare tayi wanka taci kwalliya cikin Arabian dress riga da Skirt, tayi kyau mayafi ta Dan yafa yanda Larabawa suke yi tazo ta zauna a Palonsu tana kallon film dake bata Sallah yau,Nabeel ne ya fito shima ya zauna sanye cikin 3qtr da riga hooddie kasancewar ana dan Sanyi,Iman ya kalla yayi dariya yace Iman har an fara kwalliyar amarcin ne? Angon bai dawo ba ai,Iman tace Yaya wanne Ango Kuma nayi abata Dan na birge kaina ace min sabo da Annoor nayi ba dama nayi motsi a gidan nan sai ace shi na yiwa,Yace irin wannan kwalliya haka kamar a Kuwait, murmushi tayi kawai tace karfe nawa ne? ya duba wayarsa yace 8pm,tace uhmm lokaci yayi nisa,Bai dawo ba ko? Ni Yaya Allah ka daina min haka,yace to na daina amma idan ba Kya son Annoor ni Ina so zan rufa miki asiri a haka,Iman tace tab wallahi bai Isa ba,babu Wanda zai rufa masa asiri abinda ya shuka sai ya girbe kayansa tas,Nabeel yayi dariya yace ki daina pretending Iman shi kike so,tace Allah ya kiyaye na so me fyade dan fyade,haka kawai ai na Kalli video din sai da na nutsu na kalla hmmm yayi min fya....mukus tayi