← Book details Noor Al Hayat Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 168

Sashe 48

Noor Al Hayat Complete Hausa Novel · about 8 min read

Throughout schl days ko assignment aka ba su Iklima ko average bata ci, daga 2 sai 3, baby ta samu abun dariya kullum cikin mata dariya take, ita dai Khadijah ba ruwanta nata ido, yau Friday tun da suka dawo schl khadijah ke kitchen gun kyauta tana bata labarin makaranta, kyauta tace "Toh ni abinda nake son sani a nan shine, ita ikliman bata gane karatu ne da bata amsa tambaya a aji?" Khadijah ta hade rai tace "Ni Anty mai girki am not gisting you about her ba ruwana kawai ina baki labarin masu kokari ne a aji" Kyauta tace "Ke dai kin fiye tsoro tsiya shi yasa baby ke burgeni, shegen duka take ma mummunar yarinyar" Khadijah tayi yar dariya tace "Ni dai ba ruwana Anty mai girki" Kyauta ta kyabe baki tace "Yo ai ba karya nayi ba, mummunar karshe ce yarinyar da nanikakken hanci kamar an taka amala a kan hanya, ido mitsi mitsi kamar na tana, baki kamar gidan tsutsa, ga gashinta kamar na hammata na" Khadijah ta fashe da dariya har da kyakyatawa, kyauta ta washe baki tace "Atoh, duk uwarta ce ta ja mata ai, da bata gallaza ma 'ya yan wasu da Allah bai hada yar ta da kwakwalwar tantabara ba, da yanxu bata nuna maki tsana kiri kiri ba ai ke xa ki dinga assisting dinta kina koya mata kamar yanda ku ke yi da baby, amma uwar taki xaman lafiya da kowa, meye amfanin haka a rayuwa.... Da ta kwantar da hankalinta ma wataran duk baxa ta gan mu a nan ba sai dai idan Allah yyi xa a sake saduwa" ita dai Khadijah bata ce komai ba, kawai ji suka yi ana cillo da jakunkuna waje, duk suka kalli juna sannan suka fita da sauri, Anty Khadijah ce tsaye parlorn duk ta fiddo Ghana must go da jakar kyauta da komai nata dake cikin daki waje, Tana wani murmushi tace "Dama rana irin ta yau nake jira, har ni kyauta xaki tsaya kitchen kina yi da ni kina yi da 'ya ta, to xaman ki ya xo karshe gidan nan yanxun nan kuma ba sai anjima ba, in dai ba gidan ubanki bane, ba kuma na uwarki bane nan din tattara ina ki ina ki ga su nan ki kama gabanki" kyauta tayi shiru tana kallonta, kofa Anty khadijah ta nufa kamar xata tashi sama ta fita compound cikin tsawa ta dinga kwala ma Usman kira ya biyota da gudu yana amsawa ta shigo parlor tana nuna masa kayan tana huci tace "Maxa kwashe tsummokaran nan ka fita da su can wajen gate" Khadijah ta fashe da kuka tace "Anty don Allah kiyi hakuri kar ki koreta..." Fixgota Anty khadijah tayi ta kai mata wani mugun dundu har sau uku a baya ta gware kanta tace "Tsinanniya ae nan ba da dadewa ba xa ki bi ta kema, mu dai je xuwa" Khadijah bata daddara ba ta durkusa tana kuka sosai tana kallon kyauta dake ta kallon Anty khadijah tace "Anty mai girki kice tayi hakuri don Allah" cikin tsawa Anty khadijah tace ma kyauta "Ki fita nace kar in fitar da ke da kai na munafuka annamimiya" Kyauta tayi murmushi tace "Xan tafi, ke kuma Allah ya hada ki da dai dai ke a rayuwa" Khadijah ta fashe da matsanancin kuka ta rike kyauta cikin rawar murya tace "Don Allah Anty mai girki kar ki tafi ki bata hakuri, kar ki tafi ki bar ni" haurinta Anty khadijah ta yi kamar ta samu ball tana huci tace "Tashi ki kwaso naki kayan ki bi ta kema.... Ba sai kin ce kar ta tafi ba" Tashi da sauri khadijah tayi tana kuka xata je dauko kayan nata Kyauta ta rikota tace "Kar ki damu Khadijah in sha Allah xa mu hadu wataran, ke dai ki kula da kanki ki rike maraicin ki Allah na tare da ke" daga haka kyauta ta saketa ta dau jakarta daya da ya rage parlorn ta nufi kofa ba tare da ta bi ta kan kudin aikinta ba, Baby dake tsaye parlorn ta fashe da kuka tace "Anty me yasa xa ki koreta, she is very kind, and she can cook" Anty khadijah ta ja kunnenta da karfi tace "Nan din gidan ubanta ne da baxan koreta ba, masu halin tsiya... Ga ku so dangi" daga haka ta bi bayan kyauta da sauri domin ta tabbatar ta tafi, bata dawo ciki ba sai da ta tabbatar kyauta ta bar layin gaba daya, mai gadi duk jikinsa yyi sanyi amma bai ce komai ba, ta dawo ciki tana yatsine fuska tace "Gayyar tsiya, ita kuma Anty fatima idan ta dawo nima sai ta koreni in ga" jan iklima dake ta murmushi a parlor tayi xuwa sama, don ita ce ma taje ta kira ta a daki wai kyauta na xaginta. Har mumy ta dawo khadijah na xaune can inda kyauta ta saba ce mata ta xauna farkon xuwanta gidan, tayi kuka har ta gode Allah, kasa cewa komai Mumy tayi bayan baby ta gaya mata abinda Anty Khadijah tayi ma kyauta, jikinta yyi mugun sanyi ta wuce daki da kyar ta kira Aliyu, ce masa tayi ya dawo gida yanxu, jin yanayin muryar mahaifiyar tasa yasa ko minti biyar bai kara ba a clinic ya taho gida, har ta gama bayyana masa abinda ya daga mata hankali bai iya yace komai ba yana tsaye dakin shi ma jikinsa yyi sanyi, can ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "kiyi hakuri mumy, yanxu kinsan inda xa a samo kyautar?" Cike da damuwa Mumy tace "A ina xan sani Aliyu, matar da ba waya gare ta ba, gashi ko kudin aikinta ba a bata ba, yanxu Khadijah ciwon xuciya take son sa min ne a gidana shine abinda ban sani ba har yanxu, don me yasa bata son in xauna lafiya yanda nake so a gidana, me yasa khadijah take min haka, don nace ta xo mu xauna tare laifi nayi Aliyu da xata dinga cuta ta haka, don wannan wallahi cuta ce" Yyi kasa da murya yace "Don Allah kiyi hakuri mumy, Allah ya ganar da ita.... Xan ma mai gadi magana yanxu idan Allah yasa kyautar ta dawo ya bar ta ta shigo kawai" daga haka ya fita, labe ya ga Anty Khadijah jikin kofa tana eavesdropping duk abinda suke cewa, tana ganinsa tayi masa wani shegen kallo hade da tsaki ta shige dakinta, bai ce komai ba sai tabe baki da yayi ya sauka downstairs. Bayan ya sanar ma mai gadin ya bar kyauta ta shigo ko da xata dawo.... ya koma cikin gida, har lkcn baby na ta kumbure kumburen an kora kyauta a dinning, su siyama kam ko a jikin su, a ransa yace "xa su ci gidansu da aikin gidan nan kuma Yanxu" ya karasa dining yana kallon baby yace "Ina Iman?" Hannu ta buda masa alamar bata sani ba, kitchen ya shiga ya fita waje, xaune ya ganta har lkcn a gun idonta ya kumbura don kuka, ya tsaya yana kallonta can ya karasa wajen ta, tana ganinsa ta kuma rushewa da kuka ta kife kanta da gwiwa, ya durkusa gabanta yace "Kukan me kike?" Ta dago da sauri cikin rawar murya tace "Yayanmu Anty ta kori Anty mai girki" shiru ya d'an yi kafin yace "Ko xa ki bi ta ne?" Ta gyada masa kai da sauri, yyi murmushi yace "Toh kiyi hakuri, xata dawo in sha Allah" a hankali tace "Yaushe?" Yace "Mumy xata nemo ta" shiru khadijah tayi ya mike yace "Tashi ki je ki wanke fuskar ki" Tashi tayi ta tafi gun tap ta wanke fuskarta sannan ta dawo tana kallonsa yace "Kar ki sake kuka fa" tace "Toh" juyawa yyi ya shiga gidan ta bi bayansa, tsaye suka ga Anty Khadijah a kitchen ta hada kwanukan wanke wanke xata yi, Aliyu ya danne dariyarsa bai sake kallon direction dinta ba har ya fita kitchen din, Khadijah xata wuce tace "Zo nan..." Dawowa Khadijah tayi ta nuna mata tsintsiya tace "Maxa ki tafi ki share gaba daya gidan ai aikin ki ne kema, kuma babu uban da xai maki" daukan broom din Khadijah tayi ta fita, dai dai sakkowar mumy tana ganinta tace ta ajiye tsintsiyar su je daki su yi assignment da baby, ajiyewa tayi ta wuce sama dakin baby. Washegari da Asuba Anty khadijah ta shiga kitchen, Aliyu dake xaune parlor tun bayan da ya dawo masallaci sai murmushi yake jin yanda take ta dambe da utensils a kitchen, idan ta dauke wancan sai wannan ya fadi, tayi tsaki ya fi a kirga, karfe bakwai saura ya wuce sama don yin wanka ya tafi aiki, yana gama shiryawa ya fito ya shiga dakin baby kamar yanda ke yi duk safiya don ganin ko sun shirya, tsaye ya ga baby tana duba ma khadijah idonta da yyi ja, ya karasa dakin yace "What happen" baby tace "Yayanmu we where just on our own muna shiryawa fa, kawai sai ga ikliman nan ta shigo wai mun sace mata pen, can you imagine fa, alhalin karya ne she lost her pens gaba daya da mumy ta ba mu, shine ta dauke na Iman wai nata ne ta sace har da buga mata pen din a fuska shine ya taba idonta gashi yana mata ciwo yanxu, Yayanmu a daina siya mana komai iri daya ka gaya ma Mumy plsss, iklima don't like peace, she is always looking for conflict, I really dont like that girl" Aliyu ya duba idon Khadijah yace "Ke kuma kina xaune ta tsone maki pen a ido koh" Baby tace "Noo, Yayanmu the thing in here is that Iman don't like trouble, I just notice that, if not da ace ni ce... I will beat her blue black har sai Anty baxata ganeta ba" juyawa Aliyu yyi ya leka dakin Anty Khadijah ya ga ikliman bata ciki, fita parlor yyi ya ganta a dinning har uwar ta hada mata shayi ga uban soyayyen kwai a gabanta da bread, Saleem ma na xaune dinning din yana breakfast, fita yyi ya xaga ya k'arya branch din flower ya dawo, yana daga tsaye a bakin kofar parlor, yace "Iklima" tun da ta xo gidan sae ranan ya
Chapter 48 · 0% Book details