Sashe 158
Noor Al Hayat Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari da safe karfe bakwai khadijah ta ji fitan Aliyu da mota, mikewa tayi ta fito tana mamakin inda xa shi da sassafe, ta bude kofar dakinsa ta ga Shureim kwance yana bacci, rufe kofar tayi ta koma dakinta, sai bayan da tayi wanka ta sa wata doguwar riga mara nauyi sannan ta sauka downstairs don tsaftace gidan, kafin karfe takwas da rabi ta gama komai, tana kokarin sa turaren wuta aka bude kofar parlorn, da sauri ta juya ganin sa ta dauke kai, ya karaso ya ajiye jakar hannunsa da Breakfast din su yana kallonta ta ki juyowa, bai ce mata komai ba ya wuce sama, sai a sannan ta mike ta isa gun jakar ta bude ta ga kayan shureim ne a ciki, ta rufe a hankali ta koma daki ta dau wayarta, ta fi two minutes tana kallon wayar kafin ta turo baki tayi dialing number Umma, Umma na dagawa tace "Fatan kun tashi lafiya Daughter" a hankali Khadijah tace "Umma shine baki kira ba koh?" Umma tayi murmushi tace "Toh ke ba gashi kin kira ba yanxu, ya grandson dina?" Khadijah tace "Yana lafiya" Umma tayi kasa da murya tace "Kiyi hakuri da abinda kika gani kin ji khadijah hakan kadai ne rufin asirin ki, and I am sorry for hiding that from you ban san yanda xaki dau hakan ba shi yasa..." Khadijah ta ji hawaye ya kawo idonta ta rasa abinda xata ce, Umma tace "Soon xa ki fahimce gata mu ka maki, nasan ki da taurin kai khadijah don Allah ki ajiye makaman yakin ki ki rungumi mijin ki ki manta komai, a role dina na matsayin mahaifiya a gare ki nake baki shawarar ki daina riko ba shi da amfani khadijah, wllh na tabbata son da Aliyu yake maki baxai misaltu ba da dadewa na gane haka, ke kam ba lallai ki gani ba tunda kin sa ma kanki k'in sa saboda kaddarar da ya faru tsakanin ku, Wai ma in tambaye ki... Tunda kike kin taba ganin wanda yayi ma mace fyade ya damu kamar yanda Aliyu ya damu? Ko akwai it's very rare in today's world khadijah, sure from the beginning Barrister Sudais ya xame maki wani Haske a rayuwar ki, ya haskaka maki rayuwar ki, abinda kuma baki sani ba shine, bar ma Aliyu auren ki da Barrister yayi duk cikin haskaka maki rayuwa ne coz Aliyu is the best husband for you duba da irin duniyar da muke ciki a yau, shi kadai xa ki aura ki samu kwanciyar hankali da nutsuwa ku xauna lafiya tare da d'an ku, shi yasa ya hakura ya bar masa ba don baya so ba, Kuma ya tabbata Aliyu xai daura daga inda ya tsaya, Barrister abun girmamawa da mutuntawa ne a gun ki khadijah, kinga Babu abinda bai maki ba don tabbatar da Haske a rayuwar ki, and Dr Ayman nasan shi ma har abada baxa ki mance shi ba don ya maki abinda mahaifin ki bai maki ba yana da rai, duk da nima na so kwatanta hakan amma babu dama, ban kuma san ta inda xan fara ba, don haka mutanen nan biyu babu da abinda xa ki iya biyansu sai dai kullum ki masu addu'ar gamawa da duniya lafiya, Allah ya ba ku xaman lafiya my daughter...." a sanyaye khadijah tace "Amin Ummata nagode" Umma tace "Maa sha Allah, my regards to both father and son" d'an murmushin karfin hali khadijah tayi daga haka ta katse wayar dai dai shigowar Aliyu dakin, kin kallon direction dinsa tayi, yana kallonta yace "We are going out anytime soon, ki shirya, and am hoping kin ga breakfast downstairs..." sai a sannan ta kallesa ta daure fuska tace "Xuwa ina?" Yace "Idan mun fita xa ki gani" daga haka ya juya ya fita, komawa tayi ta kwanta kan gado duk jikinta a sanyaye daga maganganun da Umma tayi mata, ta kusa minti talatin kwance Shureim ya shigo dakin da sallama, tana kallonsa har ya karaso kusa da gadon yana ta xuba kamshi, yana murmushi yace "Anty ina kwana" tace "How was ur night" yace "Alhmdllh" tace "wa ya maka wanka?" Yace "Uncle, Anty we are going out yace in kin shirya ki fito, muna jiran ki" ta hade rai tace "Kayi breakfast ne?" Yace "Eh mun yi da uncle" ta mike xaune tace "Toh ni ce baxan yi breakfast din ba xa ka wani ce kuna jirana" Tsayawa yyi yana kallonta, Aliyu ya bude kofar dakin, sanye yake da shadda milk color, lkci daya kamshinsa ya cika ko ina na dakin, yana kallonta yace "Iman, ke nake jira" Ta kallesa tace "Ku kunyi breakfast ni kuma sai in fita haka?" Ya daga kafada yace "Nobody stopped you from Breakfasting...." Tashi tayi tsaye ta nufi kofa kamar xata tashi ta bi gefensa ta fice dakin ya bi ta da kallon gefen ido kafin yayi murmushi, Shureim yace "Uncle da mun kawo mata nata daki koh?" Karasowa yayi yana murmushi ya xauna gefen gadon ya dafa kafadan yaron yace "Ko mun kawo mata cewa xata yi who sent us..." Shureim yayi dariya yace "Uncle but why is she even angry, ko bata son gidan nan ne, or she don't want you to leave with us?" Murmushi kawai Aliyu yayi yana shafa sajensa a hankali yace "I don't know also, amma ka tambayeta" ya xaro ido yana yar dariya yace "Xata doke ni ne" rungume sa Aliyu yyi a hankali yace "Not when am around darling" Suna ta xaune dakin har ta dawo, Bata yi xaton xata samesu a ciki ba, Bata rufe kofar ba tace "Can you both excuse me" Ya kalli Shureim yace "Tafi downstairs gani nan xuwa nima" fita yaron yyi a dakin, khadijah ta xaro ido tace "Cewa nayi both..." yana murmushi yace "Ni ba mijin ki bane xan yi excusing din ki?" ta daure fuska tace "Ni dai ka fita xan canxa kaya" Yace "But am not stopping you Iman" ya kalli agogon wrist dinsa yace "Kina ta bata mana lokaci kuma da nisa xa mu je" Tace "Toh ka fita, ko kuma in fasa xuwa" Yana kallonta kamar mai counting word din yace "I.. am.. going.. no where!" Wani kallo ta dinga masa, lkci daya ta nufi can karshen gado tayi kwanciyar ta ta juya masa baya, murmushi yayi ya hau saman gadon tana ganin haka tun kan ya matso kusa da ita xata tashi yyi saurin cafkota, Kamar xata yi kuka tace "Don Allah Aliyu ka bari, bana so, to nace ka fita in sa kaya ka ki fita, ya xanyi?" Sosai xuciyarta ke bugawa tana kallonsa, ya jawota jikinsa a hankali ya kai bakinsa wuyanta murya can kasa yace "Me yasa xan fita, what is it that u are hiding" turasa tayi da karfi tace "Stop it Aliyu.." Ya dago yana kallon idanuwanta yace "Really?" Jin yanda muryarsa ya canxa ta hadiye wani abu da kyar tace "Alryt, since you are not going na ji xa sa kayan haka, sake ni" a hankali ya saketa yana kallonta, sauka tayi daga kan gadon ganin inda ta nufa da gudunta ya mike da sauri ya riga ta isa kofar ya sa makulli yana kallonta, juyawa tayi kamar xata yi kuka tace "Me yasa kake min haka don Allah" ganin irin kallon da yake mata da lumsassun idonsa ta koma gun kayanta ta fiddo wanda xata sa kamar xata yi kuka, bathroom ta nufa ya bi ta, ta tsaya bakin kofar pleadingly tace "Don girman Allah ka bar ni in sa kaya Aliyu, Kai fa kace ina bata maku lokaci... " bathroom din ya shiga ya jawota xata yi ihu ya sa makulli yace "Ki sa a nan tunda kina kunyar sa wa a cikin dakin" Bata fuska tayi tace "Ni wllh bana son abinda kake min..." Ya amshi kayan ya daura kan washing machine yace "Let me help you" Bai jira cewarta ba ya jawota lkci daya ya sauke doguwar rigar jikinta idonsa ya sauka kan tabon Cs dake cikinta, tayi kara a rikice ta durkushe wajen jikinta na rawa, dagota yayi yana kallonta a sanyaye ko kiftawa babu, ta dinga nonnokewa tana cewa "Don girman Allah ka bari Aliyu, wlh kunya nake ji" a hankali ya saketa yace "Toh sa kayan ki" jikinta na bari ta dau skirt din atamfar da sauri ta sa, sanann ta dau rigar ma ta saka, ya jawota jikinsa ya ja mata zip din rigar a hankali, ta kasa kallonsa, dago kanta yayi a hankali, ta rufe idonta da sauri, yayi murmushi yyi mata light French kiss, a rude ta bude idonta ya saketa ya bude kofar ya fita bathroom din, da kyar ta fito daga karshe duk jikinta ya mutu, Kasa shafa komai tayi a fuskarta ta sa turare da hijab kawai ta sakko downstairs, yana xaune parlorn Shureim na kwance jikinsa, ta ki yarda ta dago kanta har ta iso ta tsaya daga bayan kujera, kallonta kawai yake ganin ta kasa dagowa yayi murmushi yace "Ko d'an kwalliya baxa ki yi ba" Ta turo baki tace "Baxan yi ba" ya xaunar da Shureim yace "Toh mu je in fada maki me yasa xa ki yi" da sauri ta dago tana kallonsa tace "A'a ni bana so..." Yace "Toh je ji gyara fuskar ki" juyawa tayi da sauri ta koma sama tana waigen ko ya biyota, tana shiga daki ta sa makulli, eye pencil ta sa ta goga powder a fuskarta ta sa chappete, lokaci daya tayi wani sanyayyen kyau, ta maida hijab dinta ta sauko rike da flat shoe dinta, kallonta kawai Aliyu yake ko kiftawa babu har ta shigo parlorn, ya mike yana kallon Shureim yace "Tafi daki ka dauko min makullin mota" tashi yyi ya wuce sama, Aliyu ya mike ya nufo ta, tana ganin haka tace "Wayyo don Allah ka bari, Kar ka xo kusa da ni ka ga yanxu Shureim xai...." Toshe bakinta yyi ganin ihu xata masa, yana kallon eye balls dinta yace "You... Are beautiful Iman" Tayi saurin sauke idonta gabanta na faduwa, ya xame hannunsa bakinta, Bata ankara ba sai jin kiss tayi, duk sai da ya rabata da chappete din da tasa ta kasa kwakkwaran motsi wajen, ganin faduwa xata yi yayi saurin