← Book details Matar Mutum Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 91

Sashe 68

Matar Mutum Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kika kara da Zubaida ma kika koreta balle Bara'atu karan kada miya?

Dan Allah karki bada ni mana, a gaban Audun kikayi wannan haukar ai kuwa kin kashe kanki kin ruguza duk wani shirinki na baya da wanda ya kamata muyi a gaba wlh murus kin kashe kanko a gurinsa".

A hankali ta fara rage kukan da take tana kallon Turai alamar sonjin qarin bayani, ta yaya ta kashe kanta a gurin Audu ta ruguza shirinta ma baya dana yanzu?"
"Wai ma tukunna, ta ya akayi har ya maida ta baki sani ba?" Turai ta jefa mata tambayar, taja Dankwalinta da aka tsinto mata a Soro ta face majina kafin ta shiga bawa Turai Labarin yanda sukayi kan zancen maido da yara sa dalilinta nayin hakan har zuwa kan zuwansu Bilki da maganar da sukayi dashi dazun.

"Tirqasa, au yanzu suna cikin gidan nan kikayi wannan abin kunyar gaskiya Binta baki haduba kwakwata kin bada ni wlh sauqinta daya be ga wannan qaramin haukan naki ba dan wlh da ace yana nan kikayi shikenan kin gama yawo babu wata fankama da zaki sake yi masa ya yarda" Turan ta sake fada kafin ta muskuta tayi qasa da murya taci gaba da magana.

Se bayan sallar Isha'i su Turai suka bar gidan bayan sun tattauna batutuwa da yawa da Bintan tareda matar da suka zo tare, jan kunne tayi mata sosai akan abinda suka tattauna ta fito ta rakosu zuwa sannan zuciyarta ta danyi sanyi kadan.

Ta kalli dakin Bara'atun ta ciji yatsa, ta ci Alwashin seta gwammace mutuwarta da dawowa gidan Audu, zaman da sukayi a baya sharar fage ne yanzu ne zata nuna mata Asalin ita din wacece ta shayar da ita ruwan azabar da ko kallon inda Audu yake aka ce ta yi ba zata yarda ba.

Tana tsaye tsajar gidan bayan ta rakosu Turai Bilki ta fito sukayi wa juna kallon tara saura ta wuce Abinta bakin famfo ta bar Binta da jan qwafa.

Kaf setaci uwarsu wlh a sannu zatayi maganinsu.

Se yanzu kam taga baiken kanta data kasa riqe kanta tayi shirmen dazu ai su Bilkin zasu qara rainata su tafi da ita a baki amma ta gode Allah da batayi a idon Audun ba.

Tana hawa Barander yayi sallama, ji take kamar ta qunduma ashar a maimakon amsa masa amma ta dake iya dakiya ta amsa sedai bata iya ta tsaya ba balle ta juyi ta masa sannu da zuwa ta shige daki tana jiyo shi suna magana da Bilki kusan minti biyar kafin yabi bayanta.

"Uwargida ran gida ko Amarya zance?" Ya tsokaneta yana zama akan kujera tace
"Uhm" kawai tana cirewa Naziru Nafkin.

"Yau sarautar ta motsa kenan?" Ya sake sako mata wasa ta daure ba tareda ta kalleshi ba tace
"To kai ya ka gani?"
"Ras" ya fada kafin ya laluba Aljihunsa ya zaro wata Farar Embelop me dan girma ya miqa mata se sannan ta kalle shi ta saka hannu ta karba tana budewa, Awarwaro ne guda hudu a ciki na zinari, ta hadiye yawu Aljanunta na son abin duniya suka motsa.

"Tukuici ne, ko ince sadakin fadar kishiya ne" Audun ya fada.

Maganar Turai ta dazu ta fado mata da tace
"Ki kwantar da hankali kiyi masa laka laka irin yanda kikayi sanda kika shigo gidan, kina kallon dai wahalar da kikasha lokacin daya Auro Zubaida ta isheki ishara kisan tashin hankali ko masifa ba zata biyar da Audu ba sedai lallashi da kwantar da kai ta hakane zaki moreshi sannan ki samu biyan buqatarki to tabbas ta fara ganin gaskiyar hakan.

Dake taga abin duniya se gashi harda yi masa murmushi tace ta gode.

Ta goye Naziru suka wuce dakinsa tare, ya shiga ciki ya watsa ruwa kafin ya fito ta shirya masa abinci a ranta tana lissafin abubuwan da zata nemi yayi mata yanzu da yake neman shiri da ita.

Yana cin abinci yana mata zancen ai jibi Bara'atun zata tare kuma su Bilki zasu zauna nan harse tazo kafin su koma Bechi haka ta ringa daurewa tana yaqe duk a qoqarin ta na amfani da hudubar Turai na karta bari ta canza masa tunani akan wanda yake mata game da Bara'atu ta hakan ne zata sake korata a ruwan sanyi ba tareda ya zargeta ba.

Kwanaki ukun da su Bilki sukayi a cikin gidan sun zamar mata kwanaki mafiya baqi da muni a rayuwarta.

Idan ta tuna wai Bara'atu ce zata dawo mata gida se taji kamar ta shaqe kanta ta mutu kawai ta huta da takaici, ranar da zata tare din kuwa tun farar safiya yana fita itama ta fice gidan Turai dan bata da sama da ita a Kano wuni guda suna qulle qullen sharri na yanda za'ayi bata komo gida ba se bayan sallar Magriba lokacin ta tabbatar da su Bilki sun tafi idan ma Bara'atun tazo da yan rakiya duk suma sun koma inda suka fito.
*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*
*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*
*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*
*Muna da magunguna iri iri*
*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*
*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*
*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*
*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,
*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*
*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*
*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*
*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*
*Kutuntube mu ta wannan number
08129249549*
07011401314*
BARA'ATU
Gaba daya komai daya faru ya ringa mata tamkar fim, sanda ta samu labarin an mayar da auranta da Audu daga zuwa kai sadaki rasa tantance me zatayi tayi se kawai ta shiga daki ta kulle ta kwanta kan Katifa tayi shiru ta bar Inna Hajara da yan uwanta dake ta murna a tsakar gida.

Ita kadai take hangowa kanta makomar rayuwarta, su murna sukeyi amma ita tasan meta baro a gidan Audu wanda bata fatan ta koma ta tarar.

Sannan abinda yake qara sanyaya mata jiki yanda har kawo lokacin bata saka Audu a ido ba dukda ta samu labarin yazo yana garin ta dauka kafin faruwar komai zeje su zanta yaji ra'ayinta taji nashi amma se kawai ta tsinci anmaida mata aure babu jin ta bakinta babu komai abinda ko sanda tana budurwa ba'ayi mata ba anya kuwa Audu ne yake son komen nan ko kuwa yan uwansa ne suka tursasashi maida ita?

Tayiwa kanta tambayar.

Da yammacin ranar Kawunta ya kai musi kudin sadaki hade danashirue shirye da Audun yace a bata tayi, wannanya qara kassara mata jiki harta kasa daurewa ta fashe da kuka domin ta tabbatar da cewar ba ra'ayinsa bane na mayar da ita dole wani ne ya sakashi idan kuwa hakane ta tabbatar seta gwammace kida da Karatu gashi bakin Alqalami ya bushe ballantana tace a koma baya.

A sanyaye take komai ga sati biyun da aka saka na kwanakin tariyarta suna qaratowa har sannan kuma bata saka Audu a ido ba, da tayi maganar wa Yan uwanta Hadiza ce kadai ta fahimceta dan Inna Hajara fada take mata akan waita fiya saka damuwa a rai ai babu yanda za'ayi ace dole aka wa Audu ya mayar da ita tunda shi ba yaro bane ba rashin zuwan sa kuma bata san uzurinsa ba kuma dai duk tsiya gidansa za'a kaita idan taje can koma menene zasu tantance.

A wannan gabar ita da kanta seda ta ga baiken Innar tata ta kuma fara yarda da abinda ake fadi a gari na cewar kwadayi ne yake Dawainiya da Innar tata.

Idanba kwadayin abin duniya ba kowacce uwa tana qoqarin siyawa yar tamutunci a gurin Miji amma ita wannan be dameta ba fatanta kawai ta koma gidansa duk irin rayuwar da zatayi bata sani ba.

Cikin wannan zullumi da Taraddadi ta shiryi dawowa gidan Audu karo na biyu a matsayin matarsa.

Tsirarun mutane suka rakota ciki harda yan gidansu Audun basu jima ba kuma saboda motar data kawosu yana tsaye ga kuma wadda zata maida su Bilki dan haka suka rankaya suka koma ana ta tsegumin Ina Binta ta tafi basu ganta ba.

Bayan sun tafi gidan ya mata shiru dan ita kadai ta taho yaran ance se ta kwana biyu a kawo su a cewar Hadiza tasha Amarci a tado da tsohuwar zuma tukunna, dariya ma maganar ta bata dan bata hango wannan Amarcin da suke fada muddin Binta na cikin gidan nan.

Ta fita tsakar gidan ta tsaya tana qarewa ko Ina kallo, gidan na nan yanda ta barshi se yan canje canje na kwalliya da fenti da aka sakeyi masa yanda ko ina yake shiru cikin Aminci a ranta tayi fatan ina ma gurin ya dawwama a haka?

Ina ma rayuwarsu ta baya sanda suke zaune a daki ciki daya a Bechi ta dawo?
Chapter 68 · 0% Book details