Sashe 29
Matar Mutum Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da safe ma haka ya fita yana faman daure dauren fuska, qarfe biyar na yamma Babangida ya shigo da Biskit yace mata Babansa ne ya bashi ta tambayeshi yana ina yace yana dakin Amarya, be leqasu ba seda ya dawo daga sallar isha shima daga bakin qofa yayi mata seda safe ya juya daman ko qyallin idon Binta bata gani ranar ba.
Haka al'amura suka cigaba da gudana, a watanni biyu da auran Binta Bara'atun ta fita hayyacinta seka dauka jinyar shekara tayi saboda rama da baqin da tayi.
Wani irin zama sukeyi mara kan gado, Audun gaba daya kamar wanda aka sakawa hannu ya fita a sabgarta tsakaninta dashi idan yana dakinta gaisuwa ce se ranar dayayi sha'awar kulata a shimfida yayi bayaga wannan idan kaji yayi doguwar magana da ita to qorafinta Binta ta kai masa yazo yanayi mata fada wanda bata iya ce masa komai illah ta bashi haquri, to ba se ta aikata abinda ake ce masa tayin ba sannan ne har zata kare kanta.
Wata irin annamimiyar matace Bintan, rashin mutunchi da Tijara se kalar wanda ta manta ne batayi mata a gidan da zarar Audun ya fita yamma nayi ta daidaici lokacin dawowarsa idan yana dakin Bara'atun kenan kuna zata sheqo wanka tazo ta kame mata a falo harya dawo sannan ta hillace shi su tafi se sanda ta ganshi a hakan kuma ze zo ya rufeta da fadan Binta tace tayi mata kaza ko tace mata kaza babu bin ba'asi babu tambayar ya akayi yanda kasan wanda Bintan ta wanke gabanta ta bashi yasha haka yake shakkarta yake jin maganarta.
Ita kuwa Binta daman a shirye ta shigo gidan Audu, bata tsarawa kanta zama da kishiya ba dan haka ta shirya ta kuma tsara komai yanda zata ringayiwa Bara'atun gashin quma har se ita da kanta ta fita ta bar mata gida.
Sanda tazo taga yar yarinyar a matsayin matar Audun ma abin dariya ya bata tasan ba zata sha wahalar kada taba, tayi amfani da nakasun Audun tayi galaba akansa.
Ta karanci shidin mutum ne me son a riritashi, kalar soyayyarsa da wayewarsa har mamaki abin yake bata tamkar wanda ya tashi cikin Turawa ko wasu gogaggun mutane shiyasa take qure basirarta ta tabbatar da ta tashi kansa da nata salon wayo da dabarar.
Da baki kadai idan ta zauna ta ringa tsara masa zance baya sanin sanda yake aikata duk abinda ta sakashi ta kuma fahimci Bara'atun wawiyace babu abinda ta sani se Biyayya wa Audun kamar zata kwanta masa irin abubuwan da Bintan take masa yasa gaba daya ya raina Bara'atun dan qoqarinta da yake gani a baya duk ya disashe, a yanzu kuma da damuwa tayi mata yawa tasa abinda take iya tabukawar ada ma ta dena Shiyasa ya fita a sabgarta.
A ganinsa baqin kishi ta saka a ranta shiya hanata walwa ta takura kanta shi kuwa bashi da lokacin da ze zauna yana lallashinta ko tambayarta me take so tu da dai be tauyeta da komai ba yanzu da budi ya qarar masa ma jin dadi da abubuwan mora rayuwa sedai suyi Kyautarsu amma dukda haka a maimakon ta saki ranta taci arziqi Aa se rama take tana qara qarmashewa tana ja masa zagi dan duk wanda ya ganta se ya zargi wani mugun abun sukeyi mata da ya saka ta fita hayyacinta.
Bara'atu bata sake shiga uku ba seda Binta ta fara laulayi, duk wata hidimar Bintan kanta ta koma bisa umarnin Audu, haka zata kwanta kamar ruwa idan yana gida tayita malele kuwa ita a dole ciwo take daidai da dan kamfai idan ta cire Bara'atun ce zata wanke mata girki kuwa se tayi kala uku a rana kuma taqi ci idan ya dawo tace masa ai ta fada mata abinda take so taci taqiyi haka ze hau kanta da fada da bala'i baiwar Allah sedai tayita kuka tana kuma kaiwa Allah kokenta gashi ya hanata zuwa Bechi a fadarsa idan ta tafi waze kula da Binta tunda shi yanzu sabgogi sun masa yawa dan har tafiye tafiye ya fara.
Wannan bala'i yasa ta qara figewa tayi zuru zuru.
Ana haka ya tada zancen gyaran gida saboda ya samu isassun kudin da zasu gina masa abinda yake so.
Sunyi shawara da Binta akan Bangaren Bara'atu za'a rushe tunda shine gefen hanya zefi kyau ya zama fuskar gida dan haka ya samu Bara'atu da zancen murna kamar ta fasa ihu sanda yace mata zata tafi Bechi ta zauna na wani lokaci kafin a gama gyaran gidan, a cikin sati daya suka tattara ita da Yaran suka tafi Bechi, cikin bangaren Yakubu na da suka zauna wanda Audun ya saka aka gyare shi daman idan sunje can suke sauka nan fa gulma ta ringa yawo a gari kan cewar auren ta ne ya mutu.
Ramar da tayi ta qara bawa mutane abin fadi aka ringa yawo da zance kala kala kowa da irin abinda yake fadi.
Hankalin Bilki ya tashi da ganin Bara'atun, ita kadai ta iya budewa cikinta ta fada mata halin da take ciki a gidan dan uwanta dan hatta da Innarta duk yanda tayi da tasan me yake damunta qin fada mata tayi kawai tace mata rashin lafiya tayi amma ta samu sauqi.
Ran Bilki ya baci da labarin da Bara'atu ta bata, ta ringa fada qarshe ta dora mata laifin cewar koma menene ita ta jawa kanta da tun farko ta basu damar yi mata rashin mutunchi.
"Akan me zaki zauna kinemi ki kashe kanki da damuwa? shi Yaya Audun mala'ika ne da bazaki iya kallinsa ki gaya masa abinda yake ranki ba.
Kin zauna kin bari zuciyarki ta cika da tsoro mara dalili kina cutar da kanki to wlh idan kika cigaba da wannan salibancin kina ji kina gani seta rabaki da gidan kamar yanda ta fada" Bilkin ta fada cikin qunar rai.
Zamanta a Bechi se yafi mata kwanciyar hankali da nutsuwa, a qasa da wata daya ta fara maida jikinta ta murmure to bata da matsalar komai, ga kayan abinci nan jibgi ya ajiye musu haka kudin kashewa ya bata isassu tayi bacci cikin nutsuwa ta farka tayi abinda zatayi ta fita gurin Goggo Fadi suyi hira da Amaryar da Aminu yayi ya ajiyeta nan suke zaune tareda Goggo Fadin saboda qafa data sakata a gaba, idan kuma taji marmarin fita ta tafi gidansu ta wuni can dare yayi ta koma gida a haka suka ci wata daya sannan Audu ya je musu kwanansa biyu ya juya haka kuma yaci gaba dayi duk qarshen wata zeje yayi musu kwana biyu har suka shafe watanni hudu a Bechi.
A bangaren Audu da Binta kuwa filin gida suka samu suna zuba sharafin soyayya babu kama hannun yaro.
Ginin daya tayar kuma yayi nisa, ginin Bene ne akeyi na zamani taswira me kyau da qawatarwa qasan na Mandiya Binta ne se Benen da aka dora da zata zama turakar me gidan bangaren da Bintan take ciki yanzu kuma ya barshi akan Bara'atu seta koma can dukda Binta a ranta ta quduri cewar Bara'atun ta tafi kenan ba zata dawo mata cikin gida ba.
Kwana biyu da yake zuwa yi musu qarshen wata seda yayi da gaske Binta ta barshi, Allah ya sani bawai baya son Bara'atu bane Aa mugayen halaye data tsiro dasu ne suke bashi a ganinsa Kishi ne yake damunta ya hanata walwala.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*FREE PAGE 13*
Gini ya kammalu har Binta ta tattara ta koma sabon bangarenta.
Sababbin kayan daki Babanta yayi mata jere na garari irin wanda ba'a samu filin yi a wancan dakin ba se yanzu saboda wannan me yalwa sosai akqa debe su dan har rabin Filin maqocinsu da suke jingine ya siya ya shigo dashi shiyasa ta samu maka makan dakuna biyu ga Falo da kitchen da stor
e, an rushe katangar tsakiyar bangarorin gidan ya hade se ya sake tada daki babba a tsakar gida guda daya aka kumayi Kitchen shima na tsakar gidan se Bandaki.
Tsaf aka fente ko Ina har inda Bintan ta tashi dukda babu abinda gurin yayi amma yaga be kamata Bara'atu ta shiga a haka ba.
Ya sake aiya mata gado daya tunda daya take dashi nan kuma daki biyu ne yasa aka kwaso kayanta ta aka ajiye a store din gidan Alhaji Idi gidan qawarta qwara daya duk unguwar, da ita kadai ta iya sakewa ragowar dai idan sabga ta tashi aka gayyaceta zataje amma bata shiga gidan kowa suma tun suna shigo mata ganin bata sakewa yasa suka bari.
Binta na zuwa suka ringa shishige mata duk suka zama yan korarta dan ta wuce da Ajin ace qawayenta ne, amma da yake yawancinsu gulma ce wasu kuma kwadayi ya sakasu neman qawancen haka suke jure duk izgilancinta suna manne da ita.
Ranar da aka maido kayan Bara'atu Binta bata tare suka fita da Audu ya ajiyeta a Gadon qaya dan ya siyi mota a tsukin.
Gidan wani sabon Abokinsa Mustapha shima harkar Mai yake dan haka yanzu Audun yana mu'amala sosai da su dan qungiya guda garesu.
A Asibiti suka hadu da Matarsa Baturiya gurin awo, hali yazo daya aka qulla qawance.
Se daga baya suka fahimci sudin matan Abokanai ne shikenan zumunchi ya qullu har ta gabatar da ita ga sauran matan Abokanan mazajen nasu dan suma guruf suke dashi kowacce naji da kanta Mijinta hamshaqi.
Data dawo gidan bata ma lura da an zuba kaya ba tunda qofar a kulle take, taci gaba da sabgoginta.
Washe gari Audu yace mata gobe zeje Bechi.
A fili tayi masa fatan zuwa da dawowa lafiya a zuciyarta kuwa tace
"A haka dai Auran ze balbalce badai ta dawo gidan nan ba".
Haka al'amura suka cigaba da gudana, a watanni biyu da auran Binta Bara'atun ta fita hayyacinta seka dauka jinyar shekara tayi saboda rama da baqin da tayi.
Wani irin zama sukeyi mara kan gado, Audun gaba daya kamar wanda aka sakawa hannu ya fita a sabgarta tsakaninta dashi idan yana dakinta gaisuwa ce se ranar dayayi sha'awar kulata a shimfida yayi bayaga wannan idan kaji yayi doguwar magana da ita to qorafinta Binta ta kai masa yazo yanayi mata fada wanda bata iya ce masa komai illah ta bashi haquri, to ba se ta aikata abinda ake ce masa tayin ba sannan ne har zata kare kanta.
Wata irin annamimiyar matace Bintan, rashin mutunchi da Tijara se kalar wanda ta manta ne batayi mata a gidan da zarar Audun ya fita yamma nayi ta daidaici lokacin dawowarsa idan yana dakin Bara'atun kenan kuna zata sheqo wanka tazo ta kame mata a falo harya dawo sannan ta hillace shi su tafi se sanda ta ganshi a hakan kuma ze zo ya rufeta da fadan Binta tace tayi mata kaza ko tace mata kaza babu bin ba'asi babu tambayar ya akayi yanda kasan wanda Bintan ta wanke gabanta ta bashi yasha haka yake shakkarta yake jin maganarta.
Ita kuwa Binta daman a shirye ta shigo gidan Audu, bata tsarawa kanta zama da kishiya ba dan haka ta shirya ta kuma tsara komai yanda zata ringayiwa Bara'atun gashin quma har se ita da kanta ta fita ta bar mata gida.
Sanda tazo taga yar yarinyar a matsayin matar Audun ma abin dariya ya bata tasan ba zata sha wahalar kada taba, tayi amfani da nakasun Audun tayi galaba akansa.
Ta karanci shidin mutum ne me son a riritashi, kalar soyayyarsa da wayewarsa har mamaki abin yake bata tamkar wanda ya tashi cikin Turawa ko wasu gogaggun mutane shiyasa take qure basirarta ta tabbatar da ta tashi kansa da nata salon wayo da dabarar.
Da baki kadai idan ta zauna ta ringa tsara masa zance baya sanin sanda yake aikata duk abinda ta sakashi ta kuma fahimci Bara'atun wawiyace babu abinda ta sani se Biyayya wa Audun kamar zata kwanta masa irin abubuwan da Bintan take masa yasa gaba daya ya raina Bara'atun dan qoqarinta da yake gani a baya duk ya disashe, a yanzu kuma da damuwa tayi mata yawa tasa abinda take iya tabukawar ada ma ta dena Shiyasa ya fita a sabgarta.
A ganinsa baqin kishi ta saka a ranta shiya hanata walwa ta takura kanta shi kuwa bashi da lokacin da ze zauna yana lallashinta ko tambayarta me take so tu da dai be tauyeta da komai ba yanzu da budi ya qarar masa ma jin dadi da abubuwan mora rayuwa sedai suyi Kyautarsu amma dukda haka a maimakon ta saki ranta taci arziqi Aa se rama take tana qara qarmashewa tana ja masa zagi dan duk wanda ya ganta se ya zargi wani mugun abun sukeyi mata da ya saka ta fita hayyacinta.
Bara'atu bata sake shiga uku ba seda Binta ta fara laulayi, duk wata hidimar Bintan kanta ta koma bisa umarnin Audu, haka zata kwanta kamar ruwa idan yana gida tayita malele kuwa ita a dole ciwo take daidai da dan kamfai idan ta cire Bara'atun ce zata wanke mata girki kuwa se tayi kala uku a rana kuma taqi ci idan ya dawo tace masa ai ta fada mata abinda take so taci taqiyi haka ze hau kanta da fada da bala'i baiwar Allah sedai tayita kuka tana kuma kaiwa Allah kokenta gashi ya hanata zuwa Bechi a fadarsa idan ta tafi waze kula da Binta tunda shi yanzu sabgogi sun masa yawa dan har tafiye tafiye ya fara.
Wannan bala'i yasa ta qara figewa tayi zuru zuru.
Ana haka ya tada zancen gyaran gida saboda ya samu isassun kudin da zasu gina masa abinda yake so.
Sunyi shawara da Binta akan Bangaren Bara'atu za'a rushe tunda shine gefen hanya zefi kyau ya zama fuskar gida dan haka ya samu Bara'atu da zancen murna kamar ta fasa ihu sanda yace mata zata tafi Bechi ta zauna na wani lokaci kafin a gama gyaran gidan, a cikin sati daya suka tattara ita da Yaran suka tafi Bechi, cikin bangaren Yakubu na da suka zauna wanda Audun ya saka aka gyare shi daman idan sunje can suke sauka nan fa gulma ta ringa yawo a gari kan cewar auren ta ne ya mutu.
Ramar da tayi ta qara bawa mutane abin fadi aka ringa yawo da zance kala kala kowa da irin abinda yake fadi.
Hankalin Bilki ya tashi da ganin Bara'atun, ita kadai ta iya budewa cikinta ta fada mata halin da take ciki a gidan dan uwanta dan hatta da Innarta duk yanda tayi da tasan me yake damunta qin fada mata tayi kawai tace mata rashin lafiya tayi amma ta samu sauqi.
Ran Bilki ya baci da labarin da Bara'atu ta bata, ta ringa fada qarshe ta dora mata laifin cewar koma menene ita ta jawa kanta da tun farko ta basu damar yi mata rashin mutunchi.
"Akan me zaki zauna kinemi ki kashe kanki da damuwa? shi Yaya Audun mala'ika ne da bazaki iya kallinsa ki gaya masa abinda yake ranki ba.
Kin zauna kin bari zuciyarki ta cika da tsoro mara dalili kina cutar da kanki to wlh idan kika cigaba da wannan salibancin kina ji kina gani seta rabaki da gidan kamar yanda ta fada" Bilkin ta fada cikin qunar rai.
Zamanta a Bechi se yafi mata kwanciyar hankali da nutsuwa, a qasa da wata daya ta fara maida jikinta ta murmure to bata da matsalar komai, ga kayan abinci nan jibgi ya ajiye musu haka kudin kashewa ya bata isassu tayi bacci cikin nutsuwa ta farka tayi abinda zatayi ta fita gurin Goggo Fadi suyi hira da Amaryar da Aminu yayi ya ajiyeta nan suke zaune tareda Goggo Fadin saboda qafa data sakata a gaba, idan kuma taji marmarin fita ta tafi gidansu ta wuni can dare yayi ta koma gida a haka suka ci wata daya sannan Audu ya je musu kwanansa biyu ya juya haka kuma yaci gaba dayi duk qarshen wata zeje yayi musu kwana biyu har suka shafe watanni hudu a Bechi.
A bangaren Audu da Binta kuwa filin gida suka samu suna zuba sharafin soyayya babu kama hannun yaro.
Ginin daya tayar kuma yayi nisa, ginin Bene ne akeyi na zamani taswira me kyau da qawatarwa qasan na Mandiya Binta ne se Benen da aka dora da zata zama turakar me gidan bangaren da Bintan take ciki yanzu kuma ya barshi akan Bara'atu seta koma can dukda Binta a ranta ta quduri cewar Bara'atun ta tafi kenan ba zata dawo mata cikin gida ba.
Kwana biyu da yake zuwa yi musu qarshen wata seda yayi da gaske Binta ta barshi, Allah ya sani bawai baya son Bara'atu bane Aa mugayen halaye data tsiro dasu ne suke bashi a ganinsa Kishi ne yake damunta ya hanata walwala.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*FREE PAGE 13*
Gini ya kammalu har Binta ta tattara ta koma sabon bangarenta.
Sababbin kayan daki Babanta yayi mata jere na garari irin wanda ba'a samu filin yi a wancan dakin ba se yanzu saboda wannan me yalwa sosai akqa debe su dan har rabin Filin maqocinsu da suke jingine ya siya ya shigo dashi shiyasa ta samu maka makan dakuna biyu ga Falo da kitchen da stor
e, an rushe katangar tsakiyar bangarorin gidan ya hade se ya sake tada daki babba a tsakar gida guda daya aka kumayi Kitchen shima na tsakar gidan se Bandaki.
Tsaf aka fente ko Ina har inda Bintan ta tashi dukda babu abinda gurin yayi amma yaga be kamata Bara'atu ta shiga a haka ba.
Ya sake aiya mata gado daya tunda daya take dashi nan kuma daki biyu ne yasa aka kwaso kayanta ta aka ajiye a store din gidan Alhaji Idi gidan qawarta qwara daya duk unguwar, da ita kadai ta iya sakewa ragowar dai idan sabga ta tashi aka gayyaceta zataje amma bata shiga gidan kowa suma tun suna shigo mata ganin bata sakewa yasa suka bari.
Binta na zuwa suka ringa shishige mata duk suka zama yan korarta dan ta wuce da Ajin ace qawayenta ne, amma da yake yawancinsu gulma ce wasu kuma kwadayi ya sakasu neman qawancen haka suke jure duk izgilancinta suna manne da ita.
Ranar da aka maido kayan Bara'atu Binta bata tare suka fita da Audu ya ajiyeta a Gadon qaya dan ya siyi mota a tsukin.
Gidan wani sabon Abokinsa Mustapha shima harkar Mai yake dan haka yanzu Audun yana mu'amala sosai da su dan qungiya guda garesu.
A Asibiti suka hadu da Matarsa Baturiya gurin awo, hali yazo daya aka qulla qawance.
Se daga baya suka fahimci sudin matan Abokanai ne shikenan zumunchi ya qullu har ta gabatar da ita ga sauran matan Abokanan mazajen nasu dan suma guruf suke dashi kowacce naji da kanta Mijinta hamshaqi.
Data dawo gidan bata ma lura da an zuba kaya ba tunda qofar a kulle take, taci gaba da sabgoginta.
Washe gari Audu yace mata gobe zeje Bechi.
A fili tayi masa fatan zuwa da dawowa lafiya a zuciyarta kuwa tace
"A haka dai Auran ze balbalce badai ta dawo gidan nan ba".