Sashe 27
Matar Mutum Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har qofar kitchen din ta qarasa fuska dauke da fara'a suka gaisa daidai nan Audu da gama wankan sa kenan ya shiga yana shiryawa dan yau ze fita aiki ya leqo haqoran nan a washe yana cewa
"Aa, wa nake ji kamar Amarya da sassafen nan?"
"Nice, na zo bikon Ango naji shiru har gari yayi haske baka leqa mu ba" ta fada cikin wani salo da ya saka Bara'atu sakin baki kwan datake soyawa akan wuta ya fara qauri yayi baqi kafin ta ankare ta sauke.
Abdullahi da Babangida suka fito daga daki suka gaida Binta, ta karbi Babannan tana masa wasa ta shige falon Bara'atun suka barta tsaye a kitchen.
A sanyaye ta gama soya kwan ta fara shigar musu da abin karin.
Ta jere komai a tsakiyar daki na Audu daban se nata dana yara daban.
Abdullahi ta fara hadawa shayi shida ze tafi makaranta ta zuba masa wainar kwansa da Biredi ya dauka ya tafi dakinsu Babangida ya bishi dan haka ta zuba nasa ta bisu dashi ta bar Audu da Binta dake zuba hirar da bama fuskanta take ba dan rabi turanci sukeyi.
Tana dawowa ta tarar sun baje suna karyawa tare.
Wani abu ya soketa amma ta daure
"Kin ganni da kwadayi ko?" Binta ta fada tana mata murmushi seta girgiza kai tana murmushin yaqe itama.
Nata abin karin ta dauka ta shigar daki ta dawo ta dauki Babannan dake musu didifniya yana shirin zubar da shayi suka shige ciki.
Binta na zaune har Audu ya shiga ya qarasa shirinsa kafin ta rakashi har qofar gida ya fita, ta rasa ma me zataji, haushi ko mamaki ko me?
Daga rakiyar Audu binta bata dawo ba bangarenta ta wuce.
A sanyaye Bara'atu ta ringa ayyukanta saboda abinda ya faru daga jiya zuwa yau din.
Da Asuba duk sun makara tashi shiyasa ma Audu be fita masallace ba.
Daga gaisuwa wata magana bata hadasu ba ta fita hada abin kari shi kuma ya shiga wanka, tana Allah Allah ta gama idan sun zauna karyawar tayi masa magana Bintan tazo ta kasa ta tsare har seda ya bar gidan kudin cefane ma seda ta fito falo ta gansu a inda ya tashi ta daiji sanda yake ce mata gasu nan kafin ta fito kuma har sun bar falon to abinda take so ta fahimta shin abinda Bintana tayi da gayya ne ko kuwa dai tayine bada wata manufa ba?
Kasancewar Audu baya dawowa cin Abincin rana yasa se gurin uku ta tashi dora girki.
Haka siddan Babannan ya tasa mata rigima, Babangida ya tafi makarantar Allo wadda akeyi nan cikin layinsu gida uku ne tsakaninsu qiriniyarsa tasa Audu kaishi dukda be cika shekaru uku bama sannan amma da yake yana da barage kuma bakinsa ya bude shiyasa seka dauka ya wuce shekarunsa.
Ta rasa yanda zatayi da Babannan din ta goyashi yaqi ta aje masa kayan wasa duk a banza ga aiki ta dakko dan Funkaso take so tayi da miyar Tantakwashi se Zobo da Balaraba tace mata duk in tayi girki ta ringa hada masa Lemo ta kuma koyi kala kala su Jinja harda wani farau farau me dadi idan yayi sanyi.
Gaba daya kukan yaron ya hanata sakat gata ita bata iya aiki idan yaro yana mata rigima ba.
Hijabinta ta zura ta dauki Babannan din da kayan wasansa ta doshi bangaren Bintan, qofar a bude dan haka ta shiga da sallama tana kallon wurin tana qara sha'awarsa, kullum tayi sallah se tayi addu'a Allah ya qarowa Audu budi itama ya maida mata da gurinta irin haka komai a ciki.
Tayi sallama shiru ba'a amsa ba daga inda take tana jiyo tashin kidan turawa qila Tv ce qila radio ta kunna kusan sallamarta uku dan haka ta tura qofar falon da itama ba'a rufeta ruf ba ta shiga da sallama.
Bintan na kwance kan kujera Idonta akan qofar ga Tv na aiki a ciki ake waqar da take jiyowa.
Ta sake maimaita sallama tana fadada fara'arta, ba yabo ba fallasa bintan ta yunqura ta zauna tana kallonta ba tareda ta amsa sallamar tata ba.
Kujrar dake dabda ita ta nufa da niyyar zama yanda Binta ta zaburo mata tana cewa
"Karki zauna mun a kujera" ya saka ta dage da sauri har tana shirin yarda Babannan tayi saurin dafeshi tana kallon Binta data miqe tsaye fuska a hade tamkar wadda aka aikowa da saqon mutuwa.
Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*FREE PAGE 12*
"Karki zauna mun a kujera" ya saka ta dage da sauri har tana shirin yarda Babannan tayi saurin dafeshi tana kallon Binta data miqe tsaye fuska a hade tamkar wadda aka aikowa da saqon mutuwa.
Kallon kujerar tayi dan ta gani ko wani abun cutarwa ne akai da ya sakata hanata zama amma bataga komai ba seta sake kallon Bintan dake jifanta da wani kallo data kasa fassarawa.
Cikin kaushin murya tace
"Meya shigo dake dakina?"
Mamaki da Al'ajabi suka cika Bara'atu, ita Binta take tambaya me ya shigo da ita dakinta?
Matar da idan tazo kawo musu abinci take nacin ta zauna suyi hira itace take ganin rashin dacewar zaman musu ta tafi amma yau take mata magana haka cikin zafi da gatsali, tsawar data sake buga mata ta maidata hayyacinta, Babannan ya fasa kuka dan shi baya son Hayaniya tamkar Yakubu ne ya haifeshi.
Qofa ta nuna mata tana cewa
"Fita, kuma wannan ya zama karo na qarshe da zaki tako qazaman qafafunki ki shigo mun daki, wato kinzo ki shafamun tsiya da talauci har da zaman mun a kan kujera?
Wlh karki kuma idan ba haka ba sena banbance miki tsakanin aya da tsakuwa fita" ta qarasa cikin sigar bada umarni.
Kamar kazar da qwai ya fashewa a Ciki Bara'atu ta fita daga dakin tama rasa tunanin da zatayi, to me hakan yake nufi?
Haka ta goye Babannan yana kuka da komai ta shiga aikin Jiki babu kuzari ga rigimarsa ga mamakin Binta Allah ya taimaketa yayi bacci taje ta shimfideshi dukda yamma tayi taci gaba da aikin girkin.
Bata samu ta gama ba seda aka kira sallar Magriba, su Abdullahi sun dawo dan haka shi ta hadawa wanke wanke yayi mata ita kuma ta kama Babangida da Babannan tayi musu wanka itama tayi, seda ta idar da sallah kafin ta shiga kwalliya.
Tana zaune da yara suna cin abinci ita kuma ta zuraww Tv ido tana tunanin abinda ya faru tajiyo sallama daga tsakar gida, mamaki ya sake tiqe ta to me tazo yi mata kuma?
Ko kuwa Tijarar da ta mata dazu ce bata isheta ba ta sake biyota nan?
Tsoro da fargaba ya kamata, ta san idan dukane tsaf Bintan seta babballata ta zubar ita bama zata iya takalar fitinarta ba kamar yanda tace karta sake shigar mata daki in Allah ya yarda anyi na farko anyi na qarshe to akan me kuma ita zata biyota.
Bata gama tunanin ba Binta ta daga labule ta shiga Falon, tayi kwalliya ta kece raini da Leshi ga qamshi tana bulbulawa fuskarta washe da fara'a ta sakeyin sallama.
Kasa amsa mata tayi se kallonta da takeyi a dan tsorace harta zauna akan kujera Abdullahi ya gaisheta sannan ta kalli Bara'atun tace mata
"Ina wuni Maman Baba?
Ya yaran yau duk basu shigar mun ba"
Tsabar mamaki Bara'atu seta hangame baki ta kasa ce mata komai, Binta na shirin sake magana suka jiyo sallamar Audu a tsakar gida, Yaran suka fita da gudu tararsa Binta ta sake qyara zama Bara'atu kuwa tama rasa ya take har ya shigo dakin.
Fara'arsa ta sake fadada ganinsu duka a gurin, ya zauna a kan two sitter kusada Bara'atun yana cewa
"Aa kace Uwargida da Amaryar duk suna nan me kuke tattaunawa haka?"
"Sirri muke nida Yayata" Binta ta fada tana fari da ido, Bara'atu kuwa a salube ta zame qasa tana masa sannu da zuwa tare da gaishe shi ya amsa cikin walwala.
A fakaice Binta ta galla mata harara, ta gani amma idon Audun be kai ba yana qoqarin ciro alawa daga Aljihunsa ze bawa Babannan.
Cikin yauqi Binta tace
"Barka da dawowa Ango, akwai idon yara da nayi maka maraba ta musamman"
Wani abu ya sako qirjin Bara'atu, shi kuwa kamar wani gaula haka ya bita da kallo yana cewa
"Allah ko, to ki ajiye mun bashi".
Hawaye taji sun zubo mata tayi saurin sharewa tareda miqewa ta fice daga falon dan kawo masa ruwa.
Wannan ai cin fuska ne, a dakinta a kuma ranar kwananta zasu ringa irin wannan maganganun daman haka akeyi ko kuwa nata Mijin da kishiyar ne suka raina mata wayo?
Ta hado Ruwa da Zobo a Try daidai zata shiga dakin taji Bintan na ce masa
"Ai nan na wuni, can din yayi mun shiru da yawa shiyasa na taho muka sha hirar mu ina tayata ayyuka se dazu babu jinawa na koma nayi wanka"
"Kai amma naji dadi, Allah yaci gaba da hada kanku" Audun ya fada daidai nan ta kai ajiye Ruwan a gabansa mamakin Binta na neman ya sumar da ita.
Tana ajiyewa tsulum Binta ta sakko tana cewa
"Bari na tayaki" ta zuba masa Ruwan a kofi daya ta zuba zobon a wani kafin ta dauka duka biyu tana kallonsa da murmushi tace
"Wanne zaka fara sha?"
"Bani ruwan" ya fada ta kai masa Bakinsa babu shiri Bara'atu ta miqe daga durquson da tayi tunda ta ajiye kayan tabi bayan yaran da Abdullahi ya hada kansu suka fita, yaron nada hankali da tsinkaye.
Baya taba zama ya tisa su gaba sedai idan ita ta kirashi ko Audun.
"Aa, wa nake ji kamar Amarya da sassafen nan?"
"Nice, na zo bikon Ango naji shiru har gari yayi haske baka leqa mu ba" ta fada cikin wani salo da ya saka Bara'atu sakin baki kwan datake soyawa akan wuta ya fara qauri yayi baqi kafin ta ankare ta sauke.
Abdullahi da Babangida suka fito daga daki suka gaida Binta, ta karbi Babannan tana masa wasa ta shige falon Bara'atun suka barta tsaye a kitchen.
A sanyaye ta gama soya kwan ta fara shigar musu da abin karin.
Ta jere komai a tsakiyar daki na Audu daban se nata dana yara daban.
Abdullahi ta fara hadawa shayi shida ze tafi makaranta ta zuba masa wainar kwansa da Biredi ya dauka ya tafi dakinsu Babangida ya bishi dan haka ta zuba nasa ta bisu dashi ta bar Audu da Binta dake zuba hirar da bama fuskanta take ba dan rabi turanci sukeyi.
Tana dawowa ta tarar sun baje suna karyawa tare.
Wani abu ya soketa amma ta daure
"Kin ganni da kwadayi ko?" Binta ta fada tana mata murmushi seta girgiza kai tana murmushin yaqe itama.
Nata abin karin ta dauka ta shigar daki ta dawo ta dauki Babannan dake musu didifniya yana shirin zubar da shayi suka shige ciki.
Binta na zaune har Audu ya shiga ya qarasa shirinsa kafin ta rakashi har qofar gida ya fita, ta rasa ma me zataji, haushi ko mamaki ko me?
Daga rakiyar Audu binta bata dawo ba bangarenta ta wuce.
A sanyaye Bara'atu ta ringa ayyukanta saboda abinda ya faru daga jiya zuwa yau din.
Da Asuba duk sun makara tashi shiyasa ma Audu be fita masallace ba.
Daga gaisuwa wata magana bata hadasu ba ta fita hada abin kari shi kuma ya shiga wanka, tana Allah Allah ta gama idan sun zauna karyawar tayi masa magana Bintan tazo ta kasa ta tsare har seda ya bar gidan kudin cefane ma seda ta fito falo ta gansu a inda ya tashi ta daiji sanda yake ce mata gasu nan kafin ta fito kuma har sun bar falon to abinda take so ta fahimta shin abinda Bintana tayi da gayya ne ko kuwa dai tayine bada wata manufa ba?
Kasancewar Audu baya dawowa cin Abincin rana yasa se gurin uku ta tashi dora girki.
Haka siddan Babannan ya tasa mata rigima, Babangida ya tafi makarantar Allo wadda akeyi nan cikin layinsu gida uku ne tsakaninsu qiriniyarsa tasa Audu kaishi dukda be cika shekaru uku bama sannan amma da yake yana da barage kuma bakinsa ya bude shiyasa seka dauka ya wuce shekarunsa.
Ta rasa yanda zatayi da Babannan din ta goyashi yaqi ta aje masa kayan wasa duk a banza ga aiki ta dakko dan Funkaso take so tayi da miyar Tantakwashi se Zobo da Balaraba tace mata duk in tayi girki ta ringa hada masa Lemo ta kuma koyi kala kala su Jinja harda wani farau farau me dadi idan yayi sanyi.
Gaba daya kukan yaron ya hanata sakat gata ita bata iya aiki idan yaro yana mata rigima ba.
Hijabinta ta zura ta dauki Babannan din da kayan wasansa ta doshi bangaren Bintan, qofar a bude dan haka ta shiga da sallama tana kallon wurin tana qara sha'awarsa, kullum tayi sallah se tayi addu'a Allah ya qarowa Audu budi itama ya maida mata da gurinta irin haka komai a ciki.
Tayi sallama shiru ba'a amsa ba daga inda take tana jiyo tashin kidan turawa qila Tv ce qila radio ta kunna kusan sallamarta uku dan haka ta tura qofar falon da itama ba'a rufeta ruf ba ta shiga da sallama.
Bintan na kwance kan kujera Idonta akan qofar ga Tv na aiki a ciki ake waqar da take jiyowa.
Ta sake maimaita sallama tana fadada fara'arta, ba yabo ba fallasa bintan ta yunqura ta zauna tana kallonta ba tareda ta amsa sallamar tata ba.
Kujrar dake dabda ita ta nufa da niyyar zama yanda Binta ta zaburo mata tana cewa
"Karki zauna mun a kujera" ya saka ta dage da sauri har tana shirin yarda Babannan tayi saurin dafeshi tana kallon Binta data miqe tsaye fuska a hade tamkar wadda aka aikowa da saqon mutuwa.
Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*FREE PAGE 12*
"Karki zauna mun a kujera" ya saka ta dage da sauri har tana shirin yarda Babannan tayi saurin dafeshi tana kallon Binta data miqe tsaye fuska a hade tamkar wadda aka aikowa da saqon mutuwa.
Kallon kujerar tayi dan ta gani ko wani abun cutarwa ne akai da ya sakata hanata zama amma bataga komai ba seta sake kallon Bintan dake jifanta da wani kallo data kasa fassarawa.
Cikin kaushin murya tace
"Meya shigo dake dakina?"
Mamaki da Al'ajabi suka cika Bara'atu, ita Binta take tambaya me ya shigo da ita dakinta?
Matar da idan tazo kawo musu abinci take nacin ta zauna suyi hira itace take ganin rashin dacewar zaman musu ta tafi amma yau take mata magana haka cikin zafi da gatsali, tsawar data sake buga mata ta maidata hayyacinta, Babannan ya fasa kuka dan shi baya son Hayaniya tamkar Yakubu ne ya haifeshi.
Qofa ta nuna mata tana cewa
"Fita, kuma wannan ya zama karo na qarshe da zaki tako qazaman qafafunki ki shigo mun daki, wato kinzo ki shafamun tsiya da talauci har da zaman mun a kan kujera?
Wlh karki kuma idan ba haka ba sena banbance miki tsakanin aya da tsakuwa fita" ta qarasa cikin sigar bada umarni.
Kamar kazar da qwai ya fashewa a Ciki Bara'atu ta fita daga dakin tama rasa tunanin da zatayi, to me hakan yake nufi?
Haka ta goye Babannan yana kuka da komai ta shiga aikin Jiki babu kuzari ga rigimarsa ga mamakin Binta Allah ya taimaketa yayi bacci taje ta shimfideshi dukda yamma tayi taci gaba da aikin girkin.
Bata samu ta gama ba seda aka kira sallar Magriba, su Abdullahi sun dawo dan haka shi ta hadawa wanke wanke yayi mata ita kuma ta kama Babangida da Babannan tayi musu wanka itama tayi, seda ta idar da sallah kafin ta shiga kwalliya.
Tana zaune da yara suna cin abinci ita kuma ta zuraww Tv ido tana tunanin abinda ya faru tajiyo sallama daga tsakar gida, mamaki ya sake tiqe ta to me tazo yi mata kuma?
Ko kuwa Tijarar da ta mata dazu ce bata isheta ba ta sake biyota nan?
Tsoro da fargaba ya kamata, ta san idan dukane tsaf Bintan seta babballata ta zubar ita bama zata iya takalar fitinarta ba kamar yanda tace karta sake shigar mata daki in Allah ya yarda anyi na farko anyi na qarshe to akan me kuma ita zata biyota.
Bata gama tunanin ba Binta ta daga labule ta shiga Falon, tayi kwalliya ta kece raini da Leshi ga qamshi tana bulbulawa fuskarta washe da fara'a ta sakeyin sallama.
Kasa amsa mata tayi se kallonta da takeyi a dan tsorace harta zauna akan kujera Abdullahi ya gaisheta sannan ta kalli Bara'atun tace mata
"Ina wuni Maman Baba?
Ya yaran yau duk basu shigar mun ba"
Tsabar mamaki Bara'atu seta hangame baki ta kasa ce mata komai, Binta na shirin sake magana suka jiyo sallamar Audu a tsakar gida, Yaran suka fita da gudu tararsa Binta ta sake qyara zama Bara'atu kuwa tama rasa ya take har ya shigo dakin.
Fara'arsa ta sake fadada ganinsu duka a gurin, ya zauna a kan two sitter kusada Bara'atun yana cewa
"Aa kace Uwargida da Amaryar duk suna nan me kuke tattaunawa haka?"
"Sirri muke nida Yayata" Binta ta fada tana fari da ido, Bara'atu kuwa a salube ta zame qasa tana masa sannu da zuwa tare da gaishe shi ya amsa cikin walwala.
A fakaice Binta ta galla mata harara, ta gani amma idon Audun be kai ba yana qoqarin ciro alawa daga Aljihunsa ze bawa Babannan.
Cikin yauqi Binta tace
"Barka da dawowa Ango, akwai idon yara da nayi maka maraba ta musamman"
Wani abu ya sako qirjin Bara'atu, shi kuwa kamar wani gaula haka ya bita da kallo yana cewa
"Allah ko, to ki ajiye mun bashi".
Hawaye taji sun zubo mata tayi saurin sharewa tareda miqewa ta fice daga falon dan kawo masa ruwa.
Wannan ai cin fuska ne, a dakinta a kuma ranar kwananta zasu ringa irin wannan maganganun daman haka akeyi ko kuwa nata Mijin da kishiyar ne suka raina mata wayo?
Ta hado Ruwa da Zobo a Try daidai zata shiga dakin taji Bintan na ce masa
"Ai nan na wuni, can din yayi mun shiru da yawa shiyasa na taho muka sha hirar mu ina tayata ayyuka se dazu babu jinawa na koma nayi wanka"
"Kai amma naji dadi, Allah yaci gaba da hada kanku" Audun ya fada daidai nan ta kai ajiye Ruwan a gabansa mamakin Binta na neman ya sumar da ita.
Tana ajiyewa tsulum Binta ta sakko tana cewa
"Bari na tayaki" ta zuba masa Ruwan a kofi daya ta zuba zobon a wani kafin ta dauka duka biyu tana kallonsa da murmushi tace
"Wanne zaka fara sha?"
"Bani ruwan" ya fada ta kai masa Bakinsa babu shiri Bara'atu ta miqe daga durquson da tayi tunda ta ajiye kayan tabi bayan yaran da Abdullahi ya hada kansu suka fita, yaron nada hankali da tsinkaye.
Baya taba zama ya tisa su gaba sedai idan ita ta kirashi ko Audun.