Sashe 87
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Randa yaje da maganar gida da yammaci ne,altine kasa bacci tayi sai data dangana da bokanta,kafin wayewar gari ya yiwa sule kurciya,kurciyar data kawo rabuwarsa da muntarinsa,rabuwar da har yau fuskokinsu basu qara ganawa ba,duk da yadda muntarin keta nemansa ko ina loko da saqo na garinsu saidai babu labarinsa,tun da quruciya yake nemansa har girmansa,har yau yana kewar dan uwansa kuma amini shaqiqinsa sule saidai har yanzu Allah baisa an dace ba.
Muntari yayi kuka yayi kuka har wasu ma suka tayashi kokawa,da qyar aka samo kansa,amma shima daina kiwon yayi ya haqura ya kama karatunsa gadan gadan,bayan rasuwar khadijatu mahaifiyar malam mamman kaka ga mukhtari baabaa prof,garin ya daina musu dadi baki dayansj,sai ya tattara ya koma cikin ainihin garin gombe inda dama kasuwancinsa ya riga yayi qarfi qwarai a can,ya saida dabbobin muntari saidai muntarin yaqi a saida wanda ya baiwa sule,ya samu fili daya na babansa ya zubasu ya maidashi kamar dan qaramin gidan gona yaci gaba da kiwata masa su,yayi alqawarin duk randa Allah ya sake hada fuskokinsu matuqar yana raye saiya cika wannan alqawari.
A kasuwa mahammadu ya zuba kudin muntarin,suka ci gaba da juyawa tare,gefe guda kuma ga karatunsa bai fasa ba,kafin wani lokaci muntarin ya zama dan birni sosai,ya goge,ilimi ya ratsashi,ya zama saurayi wamda har ya kammala secondry dinsa ya soma jami'a.
Kyau tsantsa irin na usilin fulani Allah ya baiwa mukhtar shi,tsantsar farin jini kamun kai kamala da kwarjini wanda shi ya janyo masa tarin masoya maza da mata,yana faran faran da son jama'a,'yammata kuwa ba'a cewa komai,duk da 'yamata ne irin na da,masu tsananin kunya da kamun kai,da wuya kaji tace tana sonka,saidai ka gani a ayyukanta,a hakan ma ana ganin kansu ya bude suna jami'a,a jami'ar ma babu yawan matan,sabida har lokacin jama'a basu karbi karatun boko ba sam sai daidaiku.
Zuwa lokaci dukiyarsu ta sake ninkuwa,irin dukiyar da a lokacin tsoro ma kake asan kana da ita saboda yawanta da rashin hanyoyin boyeta da sarrafata kamar a wannan zamanin,tuni malam muhammadu ya tashi daga malam ya koma alhaji,ya tamfatsa gida irin na masu kudin da,irin gidan da a da saidai gida na sarauta,mai sarautar ma wanda ya isa,kamar sarki ko waziri,gwamna ko shugaban qasa,tun mota da babur da handset sai wane da wane mukhtar yake hawa yake riqewa,arziqi ya zauna musu na ban mamaki,gefe guda bai fasa kiwata dabbobin sule ba,wadanda sukayi albarka suka zama hamshaqin gidan gona,wanda ke fidda kaji,madarar shanu,qwai,a kuma sarrafa yoghourt wanda yayi sunan ba gombe kawai ba har a arewa a wannan lokacin,duk abinda aka saida yana tara kudin a gu na daban yana ajjiyewa sule,har lokacin bai fasa nemansa ba,bai fidda ran kuma ganinsa ba,yakan ce IDAN DA RAI DA RABO.
Kaf qauyensu babu wanda baici arziqinsu ba,mutanen da suka kai maka Allah yayi yawa sa sh,tun a lokacin mai zuwa maka a jirgi sai wane da wane,hatta da mahaifin sule wanda altine ta yashe ta gudu ta barshi cikin tsananin talauci da yunwa,mkhtar ya fidda kudi cikin kudin sule ya biya masa hajji,kafin ya dawo aka buge gidan sa aka sake masa gini da ya dace da irin wancan zamanin,kuka ya dinga yi yana shiwa muntari albarka yana roqon Allah ya bayyana masa dansa,don hashimun ma ta gudu da shi baisan inda yake ba,sosai baban sulen yaci arziqinsa kafin Allah yayi masa rasuwa.
Muntari baabaa prof sun hadu da matarshi ta farkoZUWAIRIYYA wadda ake kira KILISHIa makaranta,a lokacin yana karatun degreed dinsa na biyu a jami'ar bayero dake kano,diya ce sarkin rano,yarinya ce mai kamun kai,miskilanci da haquri,akwai dan jin kai tattare da ita dan kadan wanda jinin sarauta dake yawo jikinta ya haddasa hakan,saidai akwai fada da tsiwa idan ka tabota,kusan abinda ya zama silar qulluwar alaqarta da mukhtar kenan,haduwarsu wajen cin abinci dake makaranta,sukayi fada daga qarshe ya nemota ya nemi soyayyarta,ta dan garashi sannan daga bisani ta amince ta yarda da aurensa,ba wani lokaci aka dauka ba kasancewar akwai sanayya tsakanin alhj muhammadu da mahaifin kilishi,saboda shahararsa a kasuwanci,zaka samu wani lokaci akwai alaqa ko abota tsakanin masu sarauta da 'yan kasuwa.
Babu bata lokaci akayi komai aka gama,alhj mahammadu ya danqarawa tilon dansa gida cikin kano da kudinsa da kansa a daura da jami'ar bayero,wanda a sannan ba unguwa bace face irin unguwannin nan marasa gidaje sabbin unguwanni,a nan suka tare cikin qauna da aminci da kula da juna,shi yana nashi karatun itama tana nata hankali kwance,da ya gama ya juya masters ita kuma data hada degree ta tsaya hakanan ta maida hankalinta kan kula da gidanta,macace data iya zaman aure,tsantsar kula da miji,iya tarairaya da nuna qauna,shekara uku da aurensu suka samu qaruwar d'a namiji,ba bata lokaci mukhtar baabaa prof ya sanya ma yaron sunan kakansa wato adam,shekara na zagayowa kilishi ta sake sambalo d'a namiji wanda C.S aka yi mata.
Abinda basu taba gani ba wato alhj muhammadu yazo gidansu,da kansa wannan karon yazo ganin jariri bayan sallamarsu daga asibiti zuwa gida,tun a daren kilishi da adam ke kira ummee ta dinga dariya tana fadin lallai wannan yaro yayi goshi,sanda aljh ya daukeshi kallonshi ya dinga yi yana murmushi,yayi wata magana data sanyaya jikinsu ta kuma basu dariya
"Inama rai zai bani aron lokaci da rayuwa naga girman wannan yaro,ba shakka na tabbatar akwai wani lamari tattare da shi,shi na daban ne cikin yaran da nake gani,tun a daren da aka ciroshi jikina ya bani haka" kilishi da ta maida abun wasa dariya tayi
"Alhj ya akai ka sani" da yake shi wasa yake musu tamkar jikokinsa,dariyar shima yayi
"Zaku ce na gaya muku,lokaci zai nuna,ba shakka shi MUSDAFA ne,zababbe ne"
"Shikenan baaba,ka sanya masa suna,dama sunanka nakeso na saka wannan karon,MUHAMMAD MUSTAPHA" yaji dadi qwarai a zuciyarsa,har ya gaza boyewa,ya daga mustapha yadinga masa addu'o'i,wasu cikin kunne wasu cikin baki wasu cikin ido,addu'o'i ne wadanda ko diyan cikinsa mukhtar bai masa su ba,yana son yaron,yana jinsa har cikin zuciyarsa,sosai ya roqa masa albarkar rayuwa duniya da lahira.
Mustapha bai cika wata ukuba duniya ba Allah ya yiwa alhj muhammad rasuwa,dan kasuwa mai gaskiya da amana,tausayi da taimako,kowa nashi ne,kowa cin arziqinsa yake,ba iyalansa kadai sukayi rashi ba hatta da kano da gombe baki daya,mukhtar ya dauko mahaifiyarsa ta dawo gidansa dake kano da zama,ya sake yiwa gombe nisa,abinda ya sake sakashi kenan ya rage zuwa gomve,sai yayi wata shida ko shekara baije ba,hakan ne ya sanya har sule yaje ya tafi basu hadu ba,sanda yaje aka gaya masa kamar zaiyu hauka,sai ya koma zuwa akai kai amma har ya gaji ya watsar sulen bai kuma dawowa ba,da alama har yanzu baqin abun da aka yi masa na cikin jikinsa.
Nauyi sai ya sake yiwa mukhtar yawa,ga dukiyarsa ga wanda mahaifinsa ya bari aka raba musu,mahaifiyarsa ta dauki tata ta damqa masa,don bata da wani itama sama da dan nata,haka duka ya hada,ga karatu da ya kasa haquri ya bari saboda yadda yaji dadinsa,ga kasuwanci ya sakoshi gaba,bayan shekara biyar da haihuwar mustapha kilishi ta sake haihuwar 'ya mace wadda taci sunan farida,zuwa lokacin sun fara ganin abinda alhj muhammadu ya fada akan mustaphan,ba shakka shi na daban ne tsakaninsa da dan uwansa,akwai banbance babance sosai,bayan haihuwarta ba dadewa itama innar mukhtar ra rasu tabi mijinta bata cika shekara ba aka haifi mai sunanta naja'atu suna kiranta da huda,haka suka ci gaba da gudanar da rayuwarsu,ko yaushe arziqinsu bunqasa yake albarkacin taimako da suke yiwa bayin Allah da nemanta sa suka ci gaba da yi ta hanyar Allah.
Mukhtar bai bar karatunsa ba sai da ya zama farfesa,a lokacinne suka hadu da ABDUS SAMAD wanda ya zame masa aboki,kusan bai qara amini tun bayan rasa sulensa da yayi sai a kan abdus samad,abdus samad na qaunar baabaa prof qwarai da gaske,a lokacin ya fara taba siyasa,ya shigeta da qafar dama,ko ince ya shigeta da gaskiya da amana,da magana daya tak idan ya fadeta,abinda yawancin 'yan siyasarmu suka rasa,ba wani abu yake nema cikinta ba sabida babu abinda ya nema ya rasa a duniya,arziqin duniya da dukiya Allah riga da ya bashi saidai ya nemi na lahira,wanda yana amfani da dukiyarsa yana nema saidai Allah ya karba masa,ba takara ya tsaya ba,amma yana supporting gwanatin dake nema sabida yadda da yayi da ingancinta da,cikin ikon Allah kuwa ta samu nasara,hakanne ya sanya aka bashi matsayin AMBASSDOR jakadan nijeria a merica,sosai abdus samad yayi farinciki,don shima iyalinsa na can,matarshi daya alokacin hajiya khaulat,abinda ya zaunar da ita can acan abdus samad ya ganta ya aureta sabida mahaifinta pharmacist ne acan a wani asibiti yake aiki,,itakam tace ba zata bishi nijeria ba,tilas ya yadda ya aureta a can suka zauna a can,bai wani damu sosai ba,don shima acan yake nashi aikin irin ma surukinsa,damuwarsa kawai yaran da zai haifa kada su tashi da tarbiyyar can.
Gidan da abdus samad suke zaune me block biyu ne,hakan ya sanya yace muntari ya zauna a nan,amma yace a'ah,saidai abdus samad yazo su zauna qyatacce kuma yalwataccen gidan da gwamnatin tarayya ta bashi ya zauna iya wa'adin aikinsa,hakan suka tattaro suka dawo,duk da khaulat bata so ba,saboda macace mai tsananin izza girman kai da ji da kai,macace dake son taga kowa a qasanta ita ce a sama,hakan ya sanya jininsu yaqi haduwa da kilishi ummee,saboda sam bata da wulaqanci,barta da miskilancinta fada da rashin son raini,sam ta tsanu halayen khaulat,duk da yadda ita khaulat din ke maqale mata,saboda tasan daga babban gida ummeen take,bugu da qari girma ne da cinyewa a wajenta ace tana hulda da mace irin ummeen,mata a wajen ambassador muhammad mukhtar muhammad adam,kuma diyar gidan sarauta.
Muntari yayi kuka yayi kuka har wasu ma suka tayashi kokawa,da qyar aka samo kansa,amma shima daina kiwon yayi ya haqura ya kama karatunsa gadan gadan,bayan rasuwar khadijatu mahaifiyar malam mamman kaka ga mukhtari baabaa prof,garin ya daina musu dadi baki dayansj,sai ya tattara ya koma cikin ainihin garin gombe inda dama kasuwancinsa ya riga yayi qarfi qwarai a can,ya saida dabbobin muntari saidai muntarin yaqi a saida wanda ya baiwa sule,ya samu fili daya na babansa ya zubasu ya maidashi kamar dan qaramin gidan gona yaci gaba da kiwata masa su,yayi alqawarin duk randa Allah ya sake hada fuskokinsu matuqar yana raye saiya cika wannan alqawari.
A kasuwa mahammadu ya zuba kudin muntarin,suka ci gaba da juyawa tare,gefe guda kuma ga karatunsa bai fasa ba,kafin wani lokaci muntarin ya zama dan birni sosai,ya goge,ilimi ya ratsashi,ya zama saurayi wamda har ya kammala secondry dinsa ya soma jami'a.
Kyau tsantsa irin na usilin fulani Allah ya baiwa mukhtar shi,tsantsar farin jini kamun kai kamala da kwarjini wanda shi ya janyo masa tarin masoya maza da mata,yana faran faran da son jama'a,'yammata kuwa ba'a cewa komai,duk da 'yamata ne irin na da,masu tsananin kunya da kamun kai,da wuya kaji tace tana sonka,saidai ka gani a ayyukanta,a hakan ma ana ganin kansu ya bude suna jami'a,a jami'ar ma babu yawan matan,sabida har lokacin jama'a basu karbi karatun boko ba sam sai daidaiku.
Zuwa lokaci dukiyarsu ta sake ninkuwa,irin dukiyar da a lokacin tsoro ma kake asan kana da ita saboda yawanta da rashin hanyoyin boyeta da sarrafata kamar a wannan zamanin,tuni malam muhammadu ya tashi daga malam ya koma alhaji,ya tamfatsa gida irin na masu kudin da,irin gidan da a da saidai gida na sarauta,mai sarautar ma wanda ya isa,kamar sarki ko waziri,gwamna ko shugaban qasa,tun mota da babur da handset sai wane da wane mukhtar yake hawa yake riqewa,arziqi ya zauna musu na ban mamaki,gefe guda bai fasa kiwata dabbobin sule ba,wadanda sukayi albarka suka zama hamshaqin gidan gona,wanda ke fidda kaji,madarar shanu,qwai,a kuma sarrafa yoghourt wanda yayi sunan ba gombe kawai ba har a arewa a wannan lokacin,duk abinda aka saida yana tara kudin a gu na daban yana ajjiyewa sule,har lokacin bai fasa nemansa ba,bai fidda ran kuma ganinsa ba,yakan ce IDAN DA RAI DA RABO.
Kaf qauyensu babu wanda baici arziqinsu ba,mutanen da suka kai maka Allah yayi yawa sa sh,tun a lokacin mai zuwa maka a jirgi sai wane da wane,hatta da mahaifin sule wanda altine ta yashe ta gudu ta barshi cikin tsananin talauci da yunwa,mkhtar ya fidda kudi cikin kudin sule ya biya masa hajji,kafin ya dawo aka buge gidan sa aka sake masa gini da ya dace da irin wancan zamanin,kuka ya dinga yi yana shiwa muntari albarka yana roqon Allah ya bayyana masa dansa,don hashimun ma ta gudu da shi baisan inda yake ba,sosai baban sulen yaci arziqinsa kafin Allah yayi masa rasuwa.
Muntari baabaa prof sun hadu da matarshi ta farkoZUWAIRIYYA wadda ake kira KILISHIa makaranta,a lokacin yana karatun degreed dinsa na biyu a jami'ar bayero dake kano,diya ce sarkin rano,yarinya ce mai kamun kai,miskilanci da haquri,akwai dan jin kai tattare da ita dan kadan wanda jinin sarauta dake yawo jikinta ya haddasa hakan,saidai akwai fada da tsiwa idan ka tabota,kusan abinda ya zama silar qulluwar alaqarta da mukhtar kenan,haduwarsu wajen cin abinci dake makaranta,sukayi fada daga qarshe ya nemota ya nemi soyayyarta,ta dan garashi sannan daga bisani ta amince ta yarda da aurensa,ba wani lokaci aka dauka ba kasancewar akwai sanayya tsakanin alhj muhammadu da mahaifin kilishi,saboda shahararsa a kasuwanci,zaka samu wani lokaci akwai alaqa ko abota tsakanin masu sarauta da 'yan kasuwa.
Babu bata lokaci akayi komai aka gama,alhj mahammadu ya danqarawa tilon dansa gida cikin kano da kudinsa da kansa a daura da jami'ar bayero,wanda a sannan ba unguwa bace face irin unguwannin nan marasa gidaje sabbin unguwanni,a nan suka tare cikin qauna da aminci da kula da juna,shi yana nashi karatun itama tana nata hankali kwance,da ya gama ya juya masters ita kuma data hada degree ta tsaya hakanan ta maida hankalinta kan kula da gidanta,macace data iya zaman aure,tsantsar kula da miji,iya tarairaya da nuna qauna,shekara uku da aurensu suka samu qaruwar d'a namiji,ba bata lokaci mukhtar baabaa prof ya sanya ma yaron sunan kakansa wato adam,shekara na zagayowa kilishi ta sake sambalo d'a namiji wanda C.S aka yi mata.
Abinda basu taba gani ba wato alhj muhammadu yazo gidansu,da kansa wannan karon yazo ganin jariri bayan sallamarsu daga asibiti zuwa gida,tun a daren kilishi da adam ke kira ummee ta dinga dariya tana fadin lallai wannan yaro yayi goshi,sanda aljh ya daukeshi kallonshi ya dinga yi yana murmushi,yayi wata magana data sanyaya jikinsu ta kuma basu dariya
"Inama rai zai bani aron lokaci da rayuwa naga girman wannan yaro,ba shakka na tabbatar akwai wani lamari tattare da shi,shi na daban ne cikin yaran da nake gani,tun a daren da aka ciroshi jikina ya bani haka" kilishi da ta maida abun wasa dariya tayi
"Alhj ya akai ka sani" da yake shi wasa yake musu tamkar jikokinsa,dariyar shima yayi
"Zaku ce na gaya muku,lokaci zai nuna,ba shakka shi MUSDAFA ne,zababbe ne"
"Shikenan baaba,ka sanya masa suna,dama sunanka nakeso na saka wannan karon,MUHAMMAD MUSTAPHA" yaji dadi qwarai a zuciyarsa,har ya gaza boyewa,ya daga mustapha yadinga masa addu'o'i,wasu cikin kunne wasu cikin baki wasu cikin ido,addu'o'i ne wadanda ko diyan cikinsa mukhtar bai masa su ba,yana son yaron,yana jinsa har cikin zuciyarsa,sosai ya roqa masa albarkar rayuwa duniya da lahira.
Mustapha bai cika wata ukuba duniya ba Allah ya yiwa alhj muhammad rasuwa,dan kasuwa mai gaskiya da amana,tausayi da taimako,kowa nashi ne,kowa cin arziqinsa yake,ba iyalansa kadai sukayi rashi ba hatta da kano da gombe baki daya,mukhtar ya dauko mahaifiyarsa ta dawo gidansa dake kano da zama,ya sake yiwa gombe nisa,abinda ya sake sakashi kenan ya rage zuwa gomve,sai yayi wata shida ko shekara baije ba,hakan ne ya sanya har sule yaje ya tafi basu hadu ba,sanda yaje aka gaya masa kamar zaiyu hauka,sai ya koma zuwa akai kai amma har ya gaji ya watsar sulen bai kuma dawowa ba,da alama har yanzu baqin abun da aka yi masa na cikin jikinsa.
Nauyi sai ya sake yiwa mukhtar yawa,ga dukiyarsa ga wanda mahaifinsa ya bari aka raba musu,mahaifiyarsa ta dauki tata ta damqa masa,don bata da wani itama sama da dan nata,haka duka ya hada,ga karatu da ya kasa haquri ya bari saboda yadda yaji dadinsa,ga kasuwanci ya sakoshi gaba,bayan shekara biyar da haihuwar mustapha kilishi ta sake haihuwar 'ya mace wadda taci sunan farida,zuwa lokacin sun fara ganin abinda alhj muhammadu ya fada akan mustaphan,ba shakka shi na daban ne tsakaninsa da dan uwansa,akwai banbance babance sosai,bayan haihuwarta ba dadewa itama innar mukhtar ra rasu tabi mijinta bata cika shekara ba aka haifi mai sunanta naja'atu suna kiranta da huda,haka suka ci gaba da gudanar da rayuwarsu,ko yaushe arziqinsu bunqasa yake albarkacin taimako da suke yiwa bayin Allah da nemanta sa suka ci gaba da yi ta hanyar Allah.
Mukhtar bai bar karatunsa ba sai da ya zama farfesa,a lokacinne suka hadu da ABDUS SAMAD wanda ya zame masa aboki,kusan bai qara amini tun bayan rasa sulensa da yayi sai a kan abdus samad,abdus samad na qaunar baabaa prof qwarai da gaske,a lokacin ya fara taba siyasa,ya shigeta da qafar dama,ko ince ya shigeta da gaskiya da amana,da magana daya tak idan ya fadeta,abinda yawancin 'yan siyasarmu suka rasa,ba wani abu yake nema cikinta ba sabida babu abinda ya nema ya rasa a duniya,arziqin duniya da dukiya Allah riga da ya bashi saidai ya nemi na lahira,wanda yana amfani da dukiyarsa yana nema saidai Allah ya karba masa,ba takara ya tsaya ba,amma yana supporting gwanatin dake nema sabida yadda da yayi da ingancinta da,cikin ikon Allah kuwa ta samu nasara,hakanne ya sanya aka bashi matsayin AMBASSDOR jakadan nijeria a merica,sosai abdus samad yayi farinciki,don shima iyalinsa na can,matarshi daya alokacin hajiya khaulat,abinda ya zaunar da ita can acan abdus samad ya ganta ya aureta sabida mahaifinta pharmacist ne acan a wani asibiti yake aiki,,itakam tace ba zata bishi nijeria ba,tilas ya yadda ya aureta a can suka zauna a can,bai wani damu sosai ba,don shima acan yake nashi aikin irin ma surukinsa,damuwarsa kawai yaran da zai haifa kada su tashi da tarbiyyar can.
Gidan da abdus samad suke zaune me block biyu ne,hakan ya sanya yace muntari ya zauna a nan,amma yace a'ah,saidai abdus samad yazo su zauna qyatacce kuma yalwataccen gidan da gwamnatin tarayya ta bashi ya zauna iya wa'adin aikinsa,hakan suka tattaro suka dawo,duk da khaulat bata so ba,saboda macace mai tsananin izza girman kai da ji da kai,macace dake son taga kowa a qasanta ita ce a sama,hakan ya sanya jininsu yaqi haduwa da kilishi ummee,saboda sam bata da wulaqanci,barta da miskilancinta fada da rashin son raini,sam ta tsanu halayen khaulat,duk da yadda ita khaulat din ke maqale mata,saboda tasan daga babban gida ummeen take,bugu da qari girma ne da cinyewa a wajenta ace tana hulda da mace irin ummeen,mata a wajen ambassador muhammad mukhtar muhammad adam,kuma diyar gidan sarauta.