Sashe 179
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wajensu hamza ya koma,ya taddasu har sun gama ciye ciyensu,wanda duka sumayyan ce ta sa aka kai musu,ba qaramin faranta masa hakan yayi ba,a da aikin ummee ne,ga hidimar baqinta ga na abokanshi,wannan karon kam kafin ummeen ma ta farga har tasa an gama musu komai,musaddqi ke cewa
"Munci mun qoshi,saura a turo mana amarya mu gaisa" wani shegen kallo ya watsa masa,suka tuntsire da dariya baki daua,hamza kam murmushi kawai ya saki yana qarewa almustapha kallo,kusan yafi kowa cikinsu farinciki da samu sauyawar rayuwar abokin nasu,ko makaho ne kai kana kallonshi kasan cewa akwai sauye sauye masu girma tattare da shi.
Sai yamma sannan malam yayi shirin komawa kasancewar a jirgi yazo a nan kuma zai koma,ba yadda baba baiyi da shi ya bari sai gobe ba amma yawi,yace zasu zo zuwa na musamman,lokacin sumayya na raka abida da nafisa wadanda suma zasu koma
"Amma malam da zaku bar mana shi ya kwana biyu wajenmu?" Murmushi malam ya saki yace
"Gaku nan gashi" ai kuwa yana jin abinda aka fada ya noqe kafada yana narke fuska,dariya malam ya saki shida baba
"Shifa kamar wanda aka haifa tare da gidansu,baison matsawa nan da can,ki baya ga haka ma abdur rahman na tabbata sai ya biyo sahu idan ba'a koma da shi ba,don yana dari dari ya bafa shi gani yake kaman bazai dawo ba" sumayyan tana ji tana gani cike da kewa abdallah ya tafi,taso qwarai ya zauna wajeta yayi wasu kwanaki,tana tsaye tana duban motar data daukesu zata kaisu airphort harda baba,sai da suka fice sannan ta saki ajiyar zuciya,ta baya taji an rungumota,ta dan firgita kadan,sam ta mance hana tsaye gefanta,tun daga sanda yarom ya tafi yaga sauyin yanayin fuskarta,habarshi a saman kafadarta ya rada mata
"Ba ke ba,nima ina buqatan yara,zakiyi himma ki bamu namu da wuri my wife?"tilas murmushi ya kubce mata,kunya ta kuma kamata,ta soma yunqurin raba jikinsu saboda idanun mutane,duk da wajen ba gun wucewar jama'a bane sosai,amma tana iya hango eesha na tahowa da alama hanya ce ta biyo da ita ta wajen,shima sarai ya ganta,ya kuma gane abinda yasa sumayya keson qwacewa,sai ya ma sake hade fuska ya kuma janyota cikin jikin nasa sosai
"baki amsa min ba my life"
"Am ready" da sauri ya juyo da ita suna fuskantar juna
"Really?"kai ta gyada a kunyace,sai ya soma juyi da ita wajen,cikin kunnenta ya rada mata
"ki zama cikin shiri yau"sai ta sinne kanta,ya soma manna mata kisses wanda hakan yaso tsaida bugun zuciyar eesha,qara sauri tayi ta bar wajen zuciyarta na bugawa,tsaki ya ja sanda ta gama wucewan
"stupid....ki kula da yarinyar can,banson wata hulda tsakaninku" inda ta wuce din sumayya tabi da kallo sai ta maida kallonta wajensa,gira ya daga mata kafin ya raba jikinsu,cikinsa ya soma shafawa da hannunshi yana yamutse fuska
"Yunwa" ya furta a hankali,sanoda tun safe rabinshi da abinci,idanu ta zari waje,shaf ta manta
"Am really sorry don Allah,Allah na yi maka abinci tun dazun na zaci kaci na bikin ne" ta fada cikin kwabe fuska,yana son salon maganar nan tata,sai ya sake mata murmushi ba tare da ya shirya ba
"Ban haqura ba" ya fada yan akwaikwayon salon maganar tata,dariya ya bata har sai da farareb haqoranta suka fito,idanu ya zuba nata yana kallon yanayin dariyar tata cikin ban sha'awa da burgewa,sai data gama tsaf sannan yace
"Zan turo a dauka min abincin" ya furta yana takawa kan qafafunshi ya matso dab da ita
"Wuce ciki tukunna" juyawa tayi sai da yaga ta wuce ciki sannan shima ya wuce
Qarfe biyar da rabi na yammaci aka soma shirin zuwa dauko amare,dai dai lokacin ya shigo cikin gidan,kwance ya sameta saman gadonshi,idanunta baki daya sun tasa sunyi jajur da su,kanshi ya dauke daga bangarenta,su'ad ta cancanci dukkan wani hukunci daga wajenshi,abubuwan bacin ran data yi masa ba zasu qirgu ba,bai mata yadda baba ya bata lokaci yana musu nasiha ba,da kuma yadda shima yayanka mata warning amma hakan duka bai hanata tsallakewa tayi tafiyarta ba,bugu da qari kuma saboda ta raina mishi iyaye ta dawo cikin gidansu amma babu wanda ya isa ta nemeshi?.ta lura idan batayi da gaske ba wankin hula zai kaiya dare,don wasu takaddu ya diba ya juya yana da nufin sake ficewa,da gudun tsiya ta cimmasa,ta rungumoshi ta baya tana sakin kuka,cikin turanci tace
"Kayi haquri ka yafemin,nasan na bata maka na maka abubuwa marasa dadi,amma duka kai ka janyo da aka hada baki da kai aka dauko mana wata cikin rayuwarmu" dan janyeta yayi daga jikinsa ya waiwayo yana dubanta cikin bacin rai
"Har yau baki hankali ba,duk sanda kika fahimci kinyi kuskure mayi maganar da zamuyi" ya sake juyawa da nufin ficewa,maqalqaleshi tayi bakj daya wanda hakan ya tilasta masa tsayawa,cikin kisaa ta dinga fidda kuka tana bashi haquri,bata da wata mafita data zarve hakan,tasan bazai taba iya shallakewa kukanta ba,kasancewarsa mai yawan tausayi da rashin son kuka,a hankali ya janyeta zuwa gadon suka zube baki daya,hannunshi ya sanya ya goge mata hawayen,har yanzu tana maqalqale a jikinsa,sai da gama goge matan kafin ya dora
"Tun ba yau ba na baki damarki tafi a qirga kan ki gyara,idan baki gyara ba duk abinda ya biyo baya kada kiyi kuka da ni,duk da hakan kika sanya qafa kika shure maganata,mutum nawa kika tadda a nan gidan?,su me ya cisu da suka zauna tare?,me ya gutsiresu gayamin?" Ya fadabyana zuba mata idanu,wani abu ya takoreta,haushin su ummee ya sake kamata,ta tabbatar yana mata kwatance ne da su,tilas ta bude baki a cunkushe tace
"Ba komai"
"So ki iya bakinki ki kyautata kalamanki,kada ki manta wandanda suka sanya baki kan auren su su waye a wajena,iyaye na ne wadanda ba wani abu da matsayinsa yayi dai dai da su ko mene ne shi a duniya" shiru tayi haushi na cikata,tsanar mutanen na sake cikata,itakam wlh bata ga abinda zai sanya ta fasa yi musu abinda tayi niyya ba,amma sai ta kawai ta gyada kai a sanyaye
"Amma almustapha baka daina sona ba har yanzu?,sannan kayi missing dina" murmushi ya subuce masa na gefan baki,kai ya gyada
"Duk yadda kika fada haka ne" qanqameshi tayi tana jin quncin dake ranta na raguwa
"I love u,i love u so much my dear",nan ta narke ta dinga dauka masa alqawuran sauya duk wani abu da baiso,daga qarshe ta masa alqawarin ta bar karatun zata zauna da shi,zata yi dukkan abinda yake so,daya daga cikin abinda ya sake sauko da shi kenan
Ta jima tana kwatanta yadda zata kirashi ta sanar masa tafiyan nasu,bata son sake shiga dakin balle ta gansu irin na dazu,ba mafita dole ta soma kiran lambar da take kyautata zaton tashi ce,wayar na kusa da shi sai ya miqa hannu ya dauka,capital S ya sanyawa sunan tun wancan lokacin,sai ya daga ya kara kunnenshi ba tare da yace komai ba,sallama tayi ya amsa mata kafin shiru ya biyo baya
" amm,dama.....dama ni da amira ne zamu je gidan amaren ana tafiya"shiru ya danyi kafin ya amsa
"Kice ta wuce ta tafi,ke kuma kizo ina nemanki" ya kashe wayar daga haka,cikin mintuna sumayya ta turo qofan hade da sallama,tayi kyau cikin wani yadin material mint blue mai haske wanda aka yiwa adon baqi,dinkin doguwar riga ne wadda ke da shape na umbrella,ba qaramin kyau shigar tayi mata,ta baro mayafinta a daki bata yafa ba,hakan ya bayyana asirin jelar kitsonta da kuma baqaqen fashion data saka wadanda suka qara haska farar fatarta,duk yadda yaso ya kaucewa kallonta ya kasa har su'ad ta lura da hakan,a nutse ta qaraso tana dauke idanunta daga kansu,wani abu data tabbatar zuwa yanzu kishi ne ya riqe mata wuya,saboda su'ad na jikinsa kamar zata shige cikinsa,kanta na kafadarshi,abinda ya hanata zama kenan tana daga tsayen tace
"Gani"
"Na ganki,u look so beautiful,da da wannan shigan zaki tafi wani gidan amare?,ba inda zaki" duk da hakan bai mata dadi ba amma kishin dake cinta yafi mata zafi kan furucinsa,sai kawai ta juya tana cewa
"Ba damuwa" mamaki ya kama su'ad,taso ace ta masa musu sun fara sa'insa ya bata mata rai kamar yadda nata ran yake a bace,amma sai taga akasin hakan,kishi ya sake maqureta sanda taji su'ad na ambatar wash na gaji yake cewa ta kwanta ra huta,bai son ta qara kuka.
Daki ta shiga ta fada kan gado idanunta na mata zafi kamar yadda zuciyarta ke mata,bata tabajin makamancin wannan kishin ba akan duka mazajen data aura har da mukhtar kuwa,sunan Allah ta dinga ambata kadan kadan har ta soma ji zuciyarta na mata sanyi,miqewa tayi ta isa gaban mudubi tana duban kanta,sai ta soma zargin kanta da zafafa kishi?,meye ne a ciki?,su'ad matarsa ce,meye ke bai miki ba kema?ta tambayi kanta,sai ta saki murmushi tana baiwa kanta qwarin gwiwa,ganin lokacin sallar magariba yayi sai ta shiga bayi ta daura akwala,ta dawo ta sake sabunta kwalliyarta ta zura haijabi ta tada sallah,bata bar kan abun sallar ba sai wajen takwas na dare bayan tayi sallar isha'i tare da karatun qur'ani saboda ta sake samun nutsuwar zuciya,ta kuwa sameta,don sakayau take jinta,bata san ya tsarin gidan nasu zai kasance ba,hakan ya sanya batayi gigin dora komai a matsayin abincin dare ba,sai data gama sallar ne ma ta shiga kitchen,cikin qanqanin lokaci ta shirya haddaden salad,ta fere abarba ta markada ta tayi lemon abarba wanda yaji flavour mai dadin qamshi.
"Munci mun qoshi,saura a turo mana amarya mu gaisa" wani shegen kallo ya watsa masa,suka tuntsire da dariya baki daua,hamza kam murmushi kawai ya saki yana qarewa almustapha kallo,kusan yafi kowa cikinsu farinciki da samu sauyawar rayuwar abokin nasu,ko makaho ne kai kana kallonshi kasan cewa akwai sauye sauye masu girma tattare da shi.
Sai yamma sannan malam yayi shirin komawa kasancewar a jirgi yazo a nan kuma zai koma,ba yadda baba baiyi da shi ya bari sai gobe ba amma yawi,yace zasu zo zuwa na musamman,lokacin sumayya na raka abida da nafisa wadanda suma zasu koma
"Amma malam da zaku bar mana shi ya kwana biyu wajenmu?" Murmushi malam ya saki yace
"Gaku nan gashi" ai kuwa yana jin abinda aka fada ya noqe kafada yana narke fuska,dariya malam ya saki shida baba
"Shifa kamar wanda aka haifa tare da gidansu,baison matsawa nan da can,ki baya ga haka ma abdur rahman na tabbata sai ya biyo sahu idan ba'a koma da shi ba,don yana dari dari ya bafa shi gani yake kaman bazai dawo ba" sumayyan tana ji tana gani cike da kewa abdallah ya tafi,taso qwarai ya zauna wajeta yayi wasu kwanaki,tana tsaye tana duban motar data daukesu zata kaisu airphort harda baba,sai da suka fice sannan ta saki ajiyar zuciya,ta baya taji an rungumota,ta dan firgita kadan,sam ta mance hana tsaye gefanta,tun daga sanda yarom ya tafi yaga sauyin yanayin fuskarta,habarshi a saman kafadarta ya rada mata
"Ba ke ba,nima ina buqatan yara,zakiyi himma ki bamu namu da wuri my wife?"tilas murmushi ya kubce mata,kunya ta kuma kamata,ta soma yunqurin raba jikinsu saboda idanun mutane,duk da wajen ba gun wucewar jama'a bane sosai,amma tana iya hango eesha na tahowa da alama hanya ce ta biyo da ita ta wajen,shima sarai ya ganta,ya kuma gane abinda yasa sumayya keson qwacewa,sai ya ma sake hade fuska ya kuma janyota cikin jikin nasa sosai
"baki amsa min ba my life"
"Am ready" da sauri ya juyo da ita suna fuskantar juna
"Really?"kai ta gyada a kunyace,sai ya soma juyi da ita wajen,cikin kunnenta ya rada mata
"ki zama cikin shiri yau"sai ta sinne kanta,ya soma manna mata kisses wanda hakan yaso tsaida bugun zuciyar eesha,qara sauri tayi ta bar wajen zuciyarta na bugawa,tsaki ya ja sanda ta gama wucewan
"stupid....ki kula da yarinyar can,banson wata hulda tsakaninku" inda ta wuce din sumayya tabi da kallo sai ta maida kallonta wajensa,gira ya daga mata kafin ya raba jikinsu,cikinsa ya soma shafawa da hannunshi yana yamutse fuska
"Yunwa" ya furta a hankali,sanoda tun safe rabinshi da abinci,idanu ta zari waje,shaf ta manta
"Am really sorry don Allah,Allah na yi maka abinci tun dazun na zaci kaci na bikin ne" ta fada cikin kwabe fuska,yana son salon maganar nan tata,sai ya sake mata murmushi ba tare da ya shirya ba
"Ban haqura ba" ya fada yan akwaikwayon salon maganar tata,dariya ya bata har sai da farareb haqoranta suka fito,idanu ya zuba nata yana kallon yanayin dariyar tata cikin ban sha'awa da burgewa,sai data gama tsaf sannan yace
"Zan turo a dauka min abincin" ya furta yana takawa kan qafafunshi ya matso dab da ita
"Wuce ciki tukunna" juyawa tayi sai da yaga ta wuce ciki sannan shima ya wuce
Qarfe biyar da rabi na yammaci aka soma shirin zuwa dauko amare,dai dai lokacin ya shigo cikin gidan,kwance ya sameta saman gadonshi,idanunta baki daya sun tasa sunyi jajur da su,kanshi ya dauke daga bangarenta,su'ad ta cancanci dukkan wani hukunci daga wajenshi,abubuwan bacin ran data yi masa ba zasu qirgu ba,bai mata yadda baba ya bata lokaci yana musu nasiha ba,da kuma yadda shima yayanka mata warning amma hakan duka bai hanata tsallakewa tayi tafiyarta ba,bugu da qari kuma saboda ta raina mishi iyaye ta dawo cikin gidansu amma babu wanda ya isa ta nemeshi?.ta lura idan batayi da gaske ba wankin hula zai kaiya dare,don wasu takaddu ya diba ya juya yana da nufin sake ficewa,da gudun tsiya ta cimmasa,ta rungumoshi ta baya tana sakin kuka,cikin turanci tace
"Kayi haquri ka yafemin,nasan na bata maka na maka abubuwa marasa dadi,amma duka kai ka janyo da aka hada baki da kai aka dauko mana wata cikin rayuwarmu" dan janyeta yayi daga jikinsa ya waiwayo yana dubanta cikin bacin rai
"Har yau baki hankali ba,duk sanda kika fahimci kinyi kuskure mayi maganar da zamuyi" ya sake juyawa da nufin ficewa,maqalqaleshi tayi bakj daya wanda hakan ya tilasta masa tsayawa,cikin kisaa ta dinga fidda kuka tana bashi haquri,bata da wata mafita data zarve hakan,tasan bazai taba iya shallakewa kukanta ba,kasancewarsa mai yawan tausayi da rashin son kuka,a hankali ya janyeta zuwa gadon suka zube baki daya,hannunshi ya sanya ya goge mata hawayen,har yanzu tana maqalqale a jikinsa,sai da gama goge matan kafin ya dora
"Tun ba yau ba na baki damarki tafi a qirga kan ki gyara,idan baki gyara ba duk abinda ya biyo baya kada kiyi kuka da ni,duk da hakan kika sanya qafa kika shure maganata,mutum nawa kika tadda a nan gidan?,su me ya cisu da suka zauna tare?,me ya gutsiresu gayamin?" Ya fadabyana zuba mata idanu,wani abu ya takoreta,haushin su ummee ya sake kamata,ta tabbatar yana mata kwatance ne da su,tilas ta bude baki a cunkushe tace
"Ba komai"
"So ki iya bakinki ki kyautata kalamanki,kada ki manta wandanda suka sanya baki kan auren su su waye a wajena,iyaye na ne wadanda ba wani abu da matsayinsa yayi dai dai da su ko mene ne shi a duniya" shiru tayi haushi na cikata,tsanar mutanen na sake cikata,itakam wlh bata ga abinda zai sanya ta fasa yi musu abinda tayi niyya ba,amma sai ta kawai ta gyada kai a sanyaye
"Amma almustapha baka daina sona ba har yanzu?,sannan kayi missing dina" murmushi ya subuce masa na gefan baki,kai ya gyada
"Duk yadda kika fada haka ne" qanqameshi tayi tana jin quncin dake ranta na raguwa
"I love u,i love u so much my dear",nan ta narke ta dinga dauka masa alqawuran sauya duk wani abu da baiso,daga qarshe ta masa alqawarin ta bar karatun zata zauna da shi,zata yi dukkan abinda yake so,daya daga cikin abinda ya sake sauko da shi kenan
Ta jima tana kwatanta yadda zata kirashi ta sanar masa tafiyan nasu,bata son sake shiga dakin balle ta gansu irin na dazu,ba mafita dole ta soma kiran lambar da take kyautata zaton tashi ce,wayar na kusa da shi sai ya miqa hannu ya dauka,capital S ya sanyawa sunan tun wancan lokacin,sai ya daga ya kara kunnenshi ba tare da yace komai ba,sallama tayi ya amsa mata kafin shiru ya biyo baya
" amm,dama.....dama ni da amira ne zamu je gidan amaren ana tafiya"shiru ya danyi kafin ya amsa
"Kice ta wuce ta tafi,ke kuma kizo ina nemanki" ya kashe wayar daga haka,cikin mintuna sumayya ta turo qofan hade da sallama,tayi kyau cikin wani yadin material mint blue mai haske wanda aka yiwa adon baqi,dinkin doguwar riga ne wadda ke da shape na umbrella,ba qaramin kyau shigar tayi mata,ta baro mayafinta a daki bata yafa ba,hakan ya bayyana asirin jelar kitsonta da kuma baqaqen fashion data saka wadanda suka qara haska farar fatarta,duk yadda yaso ya kaucewa kallonta ya kasa har su'ad ta lura da hakan,a nutse ta qaraso tana dauke idanunta daga kansu,wani abu data tabbatar zuwa yanzu kishi ne ya riqe mata wuya,saboda su'ad na jikinsa kamar zata shige cikinsa,kanta na kafadarshi,abinda ya hanata zama kenan tana daga tsayen tace
"Gani"
"Na ganki,u look so beautiful,da da wannan shigan zaki tafi wani gidan amare?,ba inda zaki" duk da hakan bai mata dadi ba amma kishin dake cinta yafi mata zafi kan furucinsa,sai kawai ta juya tana cewa
"Ba damuwa" mamaki ya kama su'ad,taso ace ta masa musu sun fara sa'insa ya bata mata rai kamar yadda nata ran yake a bace,amma sai taga akasin hakan,kishi ya sake maqureta sanda taji su'ad na ambatar wash na gaji yake cewa ta kwanta ra huta,bai son ta qara kuka.
Daki ta shiga ta fada kan gado idanunta na mata zafi kamar yadda zuciyarta ke mata,bata tabajin makamancin wannan kishin ba akan duka mazajen data aura har da mukhtar kuwa,sunan Allah ta dinga ambata kadan kadan har ta soma ji zuciyarta na mata sanyi,miqewa tayi ta isa gaban mudubi tana duban kanta,sai ta soma zargin kanta da zafafa kishi?,meye ne a ciki?,su'ad matarsa ce,meye ke bai miki ba kema?ta tambayi kanta,sai ta saki murmushi tana baiwa kanta qwarin gwiwa,ganin lokacin sallar magariba yayi sai ta shiga bayi ta daura akwala,ta dawo ta sake sabunta kwalliyarta ta zura haijabi ta tada sallah,bata bar kan abun sallar ba sai wajen takwas na dare bayan tayi sallar isha'i tare da karatun qur'ani saboda ta sake samun nutsuwar zuciya,ta kuwa sameta,don sakayau take jinta,bata san ya tsarin gidan nasu zai kasance ba,hakan ya sanya batayi gigin dora komai a matsayin abincin dare ba,sai data gama sallar ne ma ta shiga kitchen,cikin qanqanin lokaci ta shirya haddaden salad,ta fere abarba ta markada ta tayi lemon abarba wanda yaji flavour mai dadin qamshi.