Sashe 215
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sai da ya hadata da babban asibitin dake qasar wanda anan yake musu aiki lokaci lokaci,ya basu lambarta lambar gidan da adress,sannan itama ya bata number dinsu,sannan ya karba mata nurse guda daya wanda suka tanada saboda jinyar marasa lafiya wadda zata dinga zuwa tana kwana da ita,sam bai fadawa ummi ba don ya tabbatar cewa zatayi ya turota nigeria,shikuwa baison ko daya abinda zai rabashi da ita dai dai da minti daya
Tattaki ta masa har zuwa cikin falonta,kasancewar ranar girkinta ne,ya jawota kusa da shi ya riqe dukkanin hannayenta cikin nashi yana duban qwayar idanunta
"Kimin alqawari zaki kulamin da kanki har na dawo,ba tunani ba damuwa,kinyi alqawari?" Murmushi ta sakar masa mai kwantar da zuciya ta gyada kai
"Nayi maka noor,Allah ya tsaremin kai ya dawo min da kai lafiya"
"Amiiin baby na" ya furta yana lumshe idanunsa sannan ya matso da ita gab da shi yayi kissing goshinta zuwa wuyanta.
Tare da su'ad suka rakoshi har bakin mota,sai da driver ya ja suka fice sannan kowacce ta juya zuwa ciki,wani kallon banza take jifar sumayyan da shi gami da jan dogon tsaki,bata kulata ba don idan da sabo ta saba,tayi wucewarta ciki abinta.
******* **** ********
Bayan kwanaki biyar da tafiyarshi ne inda suke saka ran dawowarshi jibi,tun safe take jin ciwon mara kadan kadan,saidai bata gayawa ko nurse dinta ba saboda tunda cikinta ya shiga wata na goma take fama da irin hakan kadan kadan lokaci zuwa lokaci,yanzun ma fitsari ne ya tasheta,sai data dauki a qalla minti biyar ta iya yunqurawa ta miqe,mararta ta amsa sai data ce wash sannan ta iya miqewa a daddafe ta qarasa bandakin mararta na ciwo sosai,koda taje fitsarin kadan tayi sai ciwon da ya dadu,dawowa tayi cikin dakin ta soma kai kawo a tsakar dakin,a jikinta take ji tabbas naquda take,bata da maraba da abinda take ji lokacin haihuwar abdallah.
Tsahon awa daya tana gumurzu babu sassauci,hakan ya sanya ta fito falo a daddafe,ta dauki waya ta kira lambar nurse din,cikin sakanni kadan ta iso ta dubata ta tabbatar haihuwa ce,saidai akwai saura,asibitin ta sanarwa,babu jimawa saiga mota sun aiko da ita suka daukesu suka wuce,su'ad taji motsinsu,ta dauka wasu ne ta leqo da taga sune ta koma tayi kwanciyarta abinta.
Daki ne na musamman suka bata,dauke da na'urori kala daban daban bayan ta sauya riga zuwa ta asibiti,tun tana daure ciwon har abun ya soma wuce tunaninta,naquda take haiqan saidai haihuwa tawi zuwa,tun biyu na dare har gari ya waye haihuwa bata zo ba,daga gefan almustaphan ya kira wayarta yafi a qirga saidai ba amsa,saboda sun baro wayar a gida,ya kira su'ad tace bata sani ba,bata gama bashi cikakkiyar amsa ba ma ta kashe wayarta,yayita kira switchoff,take hankalinsa ya tashi,sai sannan yayi dana sanin me yasa ko baba uwani baisa an kawo ba?,kai tsaye ya kira asibitin nan suka shaida masa tana nan tun daren jiya,ranshi ya baci hankalinsa ya tashi,fada ya hauyi kan me yasa basu shaida masa ba?,sannan ya za'ayi su barta tun jiya har yanzu wayewar gari tana naquda har ta kusa cinye awanni da aqa'idar likitoci ba'a so ta gama su bata haihu ba,haquri suka shiga bashi,bai sauraresu ba ya katse layin ya soma tattara ya nasa ya nasa ba tare da ya kammala abinda ya kaishi ba,hankalinsa gaba daya yayo dubai,jinsa yake kaman yayi tsuntsuwa ya ganshi a can.
Qarfe hudu na yamma ya iso dubai,kai tsaye ya yiwa drivan umarni ya wuce da shi asibitin,kai tsaye ya wuce dakin da take,kwance take saman gadon,kallo daya zaka mata kasan cewa ta jigata qwarai,duk sanyin dake dakin bai hanata gumi ba,muryarshi kawai taji ta daga kanta taba dubanshi,tuni ya ajjiye jakar dake hannunsa ya qarasa inda take,nurses din dake dakin suka fice daya bayan daya,tafin hannunta ya laluba ya sanya nashi hannun ciki,hannunsa saman kanta yana shafawa a hankali,baki daya zuciyarsa ta karye
"Baby......sannu baby" ya fada idanunsa cikin nata,ga mamakinsa murmushi ta sakar masa a wahalce
"Ka dawo?"
"Eh...." Maganar tasa ta katse sanda ta furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil!" Cikin madaukakin sauti ta soma murqususu cikin matsanancin ciwon da ya taso gadan gadan,tamkar dama jiran zuwan almustaphan yake,yanayin yadda yaga tanayi ya sanyashi sake dubata da kanshi,nan ya tabbatar haihuwar ce,nurses din da suka fita ya kirawo don su taimaka masa,din bashi da qwarin gwiwar da zai iya karbar haihuwar shi kadai,yana riqe da ita yana gaya mata addu'o'i tana maimaitawa cikin wahala,a qalla mintuna goma kafin jaririyar ta samu isowa duniya,kukanta ya karade ilahirin dakin baki daya har zuwa waje,basu gama tantance komai ba ta sake wani yunqurin,wani sabon kukan ya sake karade dakin suka hadu suka cika ilahirin dakin zuwa harabar dakunan da kukansu,nurses din ne suka dauke yaran yayin da baki daya hankalinsa ya raja'a a kanta,gumin da ya mata sharkaf ya soma goge mata yana jero mata sannu babu qaqqautawa,dubanshi take yadda ya rude baki daya,kukan yaran na yawo cikin kwanyarta,tasbihi take wa ubangijin talikai,yau gata a karo na biyu ta sake samun diyoyi,diyoyin da suka fito daga tsatsonta,kasa dauke idanunata tayi daga shiyyar da yaran suke sankda nurses suka gama rabasu,kukansu suke sosai suna wutsil wutsil da qafafu da hannyensu,sakayau a yanzu take jinta kamar sun fita da duk wani ciwo dake damunta.
Cikin mintuna qalilan nurses din suka soma gyara yaran,shi kuma ya gyara ta da kanshi a wani daki daban,komai ya kammala,aka maidata zuwa wani dakin ita da yaran baki daya.
Zaune take saman gadon sosai tana jingine da bango,murmushi ne sosai kan fuskarta wanda har sai da ya sanya haqoranta bayyana,idanunta taf da qwalla sanda almustapha yake nufota dauke da daya daga cikin jariran wadda ke nannade cikin wasu irin kayan sanyi masu azabar kyau set da abun daukansu,gabanta ya qaraso shima idanunsa cike da qwalla yana dubanta tare da duban babyn,miqa mata ita yayi sai ta dauke idanunta qwallar data cika mata idanu tana gangaro mata saidai har yau murmushin dake kan fuskarta bai bace ba,da hanzari ua sake matsarta ya kama hannunta yana matsawa cikin rauni da rawar muryar da bata taba ji daga gareshi ba yace
"Kada kice zaki ji kunya babe....karbi diyarki ki gani in dauko miki dayar....duniyarmu ce baby duniyarmu....daga ni sai ke sai su karbi ki gani", ya qarashe maganar yana dora mata yarinyar saman cinyarta,tuni ta sanya hannu ta karbeta,cikin sakanni qalilan qaunar data ke musu taji ta soma ninkuwa cikin zuciyarta,sak jinin gidan baba prof,kana dubanta ko makaho ya shafa yasan jikar mutanen gwambe ce,photocopy na almustapha,sake komawa yayi ya dauko dayar ya dawo saman gadon ya zauna sosai kusa da ita yana bude mata fuskarta
" kalli usaina baby.....ba wadda ta miki kara?"ya fafa yana sakin dariya wadda ke qunshe da zallar farinciki,jinsa yake yau kaf duniya babu dan adam din da ya kaishi farinciki,ba wanda kuma ya kaishi sa'ar zuwa duniya,itakam murmushi kawai take bakinta ya gaza furta komai,Allah kenan,buwayi gagara misali,cikin rayuwarta kaf bata taba kawowa kanta haihuwa bama bare kuma aje ga haihuwar 'yan biyu,dai gashi a yau,Allah yayi mata kyautar da bata taba hasashenta ba,haqiqa Allah mai tsananin karamci ne,sosai almustaphan ya dinga sumbatu wanda tasan na tsantsar farinciki ne tana dubanshi tana dariya,ita din ma jinta take saman wata duniya ta farinciki tana yawo,ta kasa dauke idanunta daga yaram,ba don yaranta bane,amma zata iya cewa bata taba ganin jarirai masu ban sha'awa irinsu ba,sam ya mance da ya wanu kira gida ya fada sai data tuna mishi,a sannan ne ya dauko wayarshi,ummi ce mutum ta farko da ya soma kira,danda yake gaya mata tsaye ta miqe tana kabbara,bata qarasa jin zancan ba ta rankaya falon baba,saidai kash kafin ta isa tuni anty maamaa ta rigata kai labarin,wanda ta jishi je sanda take shigowa wajen ummi,a take baban ya mata kyautar kudi masu tsoka,ta dinga ma ummi dariya tana cewa saidai a tara a gaba,itama dariyan ta dinga tace rabonki ne,duk yadda baban yaso sakaya farincikinsa abun yaci tura,haka shima ya dauki waya ya dinga kiran abokai da 'yan uwa yana sanar musu,cikin lokaci qanqani labarin haihuwar ya karade kowanne sakaye,tsakanin baba da malam sai aka rasa wanda za'a yiwa murna,amira kuwa da anty dije kukan farinciki suka sanya,ta dinga kiran almustaphan tana roqonshi zata taho yace sam,sai ta saka kuka,tana so ace cikin dangi itace mutum ta farko data fara daukan yaran,abu daya ne ya saka mata haquri hoton yaran da ya dauka ya tura mata ta email adress dinta,don shi baya watsapp.
Da kanshi ua sallami matarshi bayan ya tabbatar da cewa komai lafiya suka kama hanya zuwa gida,yana bayan motar shi da ita,baki daya yaran na hannunshi ya hana mata ko daya,ji yake idan ya rufe idanu zaiga kamar mafarki kamar almara,ashe duk arziqinka duk dukiyarka,duk farincikin da kake taqama kana ciki bai gama kammaluwa ba matuqar baka samu diyoyin da zaka alaqanta da jininka ba,ashe zallar farincikin da zata fadeshi sai randa ka ganka dauke da zuriya taka ta kanka.
Tattaki ta masa har zuwa cikin falonta,kasancewar ranar girkinta ne,ya jawota kusa da shi ya riqe dukkanin hannayenta cikin nashi yana duban qwayar idanunta
"Kimin alqawari zaki kulamin da kanki har na dawo,ba tunani ba damuwa,kinyi alqawari?" Murmushi ta sakar masa mai kwantar da zuciya ta gyada kai
"Nayi maka noor,Allah ya tsaremin kai ya dawo min da kai lafiya"
"Amiiin baby na" ya furta yana lumshe idanunsa sannan ya matso da ita gab da shi yayi kissing goshinta zuwa wuyanta.
Tare da su'ad suka rakoshi har bakin mota,sai da driver ya ja suka fice sannan kowacce ta juya zuwa ciki,wani kallon banza take jifar sumayyan da shi gami da jan dogon tsaki,bata kulata ba don idan da sabo ta saba,tayi wucewarta ciki abinta.
******* **** ********
Bayan kwanaki biyar da tafiyarshi ne inda suke saka ran dawowarshi jibi,tun safe take jin ciwon mara kadan kadan,saidai bata gayawa ko nurse dinta ba saboda tunda cikinta ya shiga wata na goma take fama da irin hakan kadan kadan lokaci zuwa lokaci,yanzun ma fitsari ne ya tasheta,sai data dauki a qalla minti biyar ta iya yunqurawa ta miqe,mararta ta amsa sai data ce wash sannan ta iya miqewa a daddafe ta qarasa bandakin mararta na ciwo sosai,koda taje fitsarin kadan tayi sai ciwon da ya dadu,dawowa tayi cikin dakin ta soma kai kawo a tsakar dakin,a jikinta take ji tabbas naquda take,bata da maraba da abinda take ji lokacin haihuwar abdallah.
Tsahon awa daya tana gumurzu babu sassauci,hakan ya sanya ta fito falo a daddafe,ta dauki waya ta kira lambar nurse din,cikin sakanni kadan ta iso ta dubata ta tabbatar haihuwa ce,saidai akwai saura,asibitin ta sanarwa,babu jimawa saiga mota sun aiko da ita suka daukesu suka wuce,su'ad taji motsinsu,ta dauka wasu ne ta leqo da taga sune ta koma tayi kwanciyarta abinta.
Daki ne na musamman suka bata,dauke da na'urori kala daban daban bayan ta sauya riga zuwa ta asibiti,tun tana daure ciwon har abun ya soma wuce tunaninta,naquda take haiqan saidai haihuwa tawi zuwa,tun biyu na dare har gari ya waye haihuwa bata zo ba,daga gefan almustaphan ya kira wayarta yafi a qirga saidai ba amsa,saboda sun baro wayar a gida,ya kira su'ad tace bata sani ba,bata gama bashi cikakkiyar amsa ba ma ta kashe wayarta,yayita kira switchoff,take hankalinsa ya tashi,sai sannan yayi dana sanin me yasa ko baba uwani baisa an kawo ba?,kai tsaye ya kira asibitin nan suka shaida masa tana nan tun daren jiya,ranshi ya baci hankalinsa ya tashi,fada ya hauyi kan me yasa basu shaida masa ba?,sannan ya za'ayi su barta tun jiya har yanzu wayewar gari tana naquda har ta kusa cinye awanni da aqa'idar likitoci ba'a so ta gama su bata haihu ba,haquri suka shiga bashi,bai sauraresu ba ya katse layin ya soma tattara ya nasa ya nasa ba tare da ya kammala abinda ya kaishi ba,hankalinsa gaba daya yayo dubai,jinsa yake kaman yayi tsuntsuwa ya ganshi a can.
Qarfe hudu na yamma ya iso dubai,kai tsaye ya yiwa drivan umarni ya wuce da shi asibitin,kai tsaye ya wuce dakin da take,kwance take saman gadon,kallo daya zaka mata kasan cewa ta jigata qwarai,duk sanyin dake dakin bai hanata gumi ba,muryarshi kawai taji ta daga kanta taba dubanshi,tuni ya ajjiye jakar dake hannunsa ya qarasa inda take,nurses din dake dakin suka fice daya bayan daya,tafin hannunta ya laluba ya sanya nashi hannun ciki,hannunsa saman kanta yana shafawa a hankali,baki daya zuciyarsa ta karye
"Baby......sannu baby" ya fada idanunsa cikin nata,ga mamakinsa murmushi ta sakar masa a wahalce
"Ka dawo?"
"Eh...." Maganar tasa ta katse sanda ta furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil!" Cikin madaukakin sauti ta soma murqususu cikin matsanancin ciwon da ya taso gadan gadan,tamkar dama jiran zuwan almustaphan yake,yanayin yadda yaga tanayi ya sanyashi sake dubata da kanshi,nan ya tabbatar haihuwar ce,nurses din da suka fita ya kirawo don su taimaka masa,din bashi da qwarin gwiwar da zai iya karbar haihuwar shi kadai,yana riqe da ita yana gaya mata addu'o'i tana maimaitawa cikin wahala,a qalla mintuna goma kafin jaririyar ta samu isowa duniya,kukanta ya karade ilahirin dakin baki daya har zuwa waje,basu gama tantance komai ba ta sake wani yunqurin,wani sabon kukan ya sake karade dakin suka hadu suka cika ilahirin dakin zuwa harabar dakunan da kukansu,nurses din ne suka dauke yaran yayin da baki daya hankalinsa ya raja'a a kanta,gumin da ya mata sharkaf ya soma goge mata yana jero mata sannu babu qaqqautawa,dubanshi take yadda ya rude baki daya,kukan yaran na yawo cikin kwanyarta,tasbihi take wa ubangijin talikai,yau gata a karo na biyu ta sake samun diyoyi,diyoyin da suka fito daga tsatsonta,kasa dauke idanunata tayi daga shiyyar da yaran suke sankda nurses suka gama rabasu,kukansu suke sosai suna wutsil wutsil da qafafu da hannyensu,sakayau a yanzu take jinta kamar sun fita da duk wani ciwo dake damunta.
Cikin mintuna qalilan nurses din suka soma gyara yaran,shi kuma ya gyara ta da kanshi a wani daki daban,komai ya kammala,aka maidata zuwa wani dakin ita da yaran baki daya.
Zaune take saman gadon sosai tana jingine da bango,murmushi ne sosai kan fuskarta wanda har sai da ya sanya haqoranta bayyana,idanunta taf da qwalla sanda almustapha yake nufota dauke da daya daga cikin jariran wadda ke nannade cikin wasu irin kayan sanyi masu azabar kyau set da abun daukansu,gabanta ya qaraso shima idanunsa cike da qwalla yana dubanta tare da duban babyn,miqa mata ita yayi sai ta dauke idanunta qwallar data cika mata idanu tana gangaro mata saidai har yau murmushin dake kan fuskarta bai bace ba,da hanzari ua sake matsarta ya kama hannunta yana matsawa cikin rauni da rawar muryar da bata taba ji daga gareshi ba yace
"Kada kice zaki ji kunya babe....karbi diyarki ki gani in dauko miki dayar....duniyarmu ce baby duniyarmu....daga ni sai ke sai su karbi ki gani", ya qarashe maganar yana dora mata yarinyar saman cinyarta,tuni ta sanya hannu ta karbeta,cikin sakanni qalilan qaunar data ke musu taji ta soma ninkuwa cikin zuciyarta,sak jinin gidan baba prof,kana dubanta ko makaho ya shafa yasan jikar mutanen gwambe ce,photocopy na almustapha,sake komawa yayi ya dauko dayar ya dawo saman gadon ya zauna sosai kusa da ita yana bude mata fuskarta
" kalli usaina baby.....ba wadda ta miki kara?"ya fafa yana sakin dariya wadda ke qunshe da zallar farinciki,jinsa yake yau kaf duniya babu dan adam din da ya kaishi farinciki,ba wanda kuma ya kaishi sa'ar zuwa duniya,itakam murmushi kawai take bakinta ya gaza furta komai,Allah kenan,buwayi gagara misali,cikin rayuwarta kaf bata taba kawowa kanta haihuwa bama bare kuma aje ga haihuwar 'yan biyu,dai gashi a yau,Allah yayi mata kyautar da bata taba hasashenta ba,haqiqa Allah mai tsananin karamci ne,sosai almustaphan ya dinga sumbatu wanda tasan na tsantsar farinciki ne tana dubanshi tana dariya,ita din ma jinta take saman wata duniya ta farinciki tana yawo,ta kasa dauke idanunta daga yaram,ba don yaranta bane,amma zata iya cewa bata taba ganin jarirai masu ban sha'awa irinsu ba,sam ya mance da ya wanu kira gida ya fada sai data tuna mishi,a sannan ne ya dauko wayarshi,ummi ce mutum ta farko da ya soma kira,danda yake gaya mata tsaye ta miqe tana kabbara,bata qarasa jin zancan ba ta rankaya falon baba,saidai kash kafin ta isa tuni anty maamaa ta rigata kai labarin,wanda ta jishi je sanda take shigowa wajen ummi,a take baban ya mata kyautar kudi masu tsoka,ta dinga ma ummi dariya tana cewa saidai a tara a gaba,itama dariyan ta dinga tace rabonki ne,duk yadda baban yaso sakaya farincikinsa abun yaci tura,haka shima ya dauki waya ya dinga kiran abokai da 'yan uwa yana sanar musu,cikin lokaci qanqani labarin haihuwar ya karade kowanne sakaye,tsakanin baba da malam sai aka rasa wanda za'a yiwa murna,amira kuwa da anty dije kukan farinciki suka sanya,ta dinga kiran almustaphan tana roqonshi zata taho yace sam,sai ta saka kuka,tana so ace cikin dangi itace mutum ta farko data fara daukan yaran,abu daya ne ya saka mata haquri hoton yaran da ya dauka ya tura mata ta email adress dinta,don shi baya watsapp.
Da kanshi ua sallami matarshi bayan ya tabbatar da cewa komai lafiya suka kama hanya zuwa gida,yana bayan motar shi da ita,baki daya yaran na hannunshi ya hana mata ko daya,ji yake idan ya rufe idanu zaiga kamar mafarki kamar almara,ashe duk arziqinka duk dukiyarka,duk farincikin da kake taqama kana ciki bai gama kammaluwa ba matuqar baka samu diyoyin da zaka alaqanta da jininka ba,ashe zallar farincikin da zata fadeshi sai randa ka ganka dauke da zuriya taka ta kanka.