← Book details Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 170 OF 226

Sashe 170

Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Karo na biyu ta sake shigowa garin abuja a matsayinta na matar almustapha suruka ga baba prof,sai ta tsinci kanta cikin tsantsar kunya da nauyin ahalin gidan,sanda suka isa alamu na nuna gidan ya soma karbar baki kamar yadda hakan ya zama al'adar gidan duk yayin da wani sha'ani ya tashi,kai tsaye bangaren ummee ta nufacu zuwa,saidai ya sanya hannunshi ya riqe nata hannun ya sauya akalarta zuwa nasu bangaren
"me kika yimin sa zaki nufi wani gun,idan na kammala duka abinda zanyi kina iya zuwa but not now" shiru ta masa tana jin yadda idanuwa sukayi yawa akansu,akwai 'yammata zaune harabar gidan suna sheqar iskar almuru wanda ke busowa kasancewar an kusa sallar magariba,hakanan garin yana dan hade da hadari mai bada iska,sai yanayin ya dinga haifar da wani yanayi cikin zuciyarta,sai ta samu kanta da lafewa a jikinsa har suka shige bangarensu,sai da suka bacewa idanuwansu sannan suka dauke kansh daga wajen,daya daga cikin 'yammatan ta doka hannunta saman tebur
"Kan bala'i,wai ya akayi haka ne ta faru?,wacce iriyar rashin sa'a garemu da aka gaza samun ko daya daga cikinmu ta shiga rayuwar man din can?"
"Rashin sa'a babba ma kuwa,sai nake ganin fuskar yarinyar ma kamar na santa fa"dariya dayar ta saki
"haba sakina,bakiga yanayinta ba,ba lallai bafa ma a qasar nan ta tashi ba itama,kinsan man din nan yake da bala'in aji da daukar kai,dukanmu munsan ra'ayinshi da aqidarsa irin macen da yake buri,da alama kuma ya samu,don wallahi wannan sai taci uban su'ad a komai da komai"da sauri wadda da alama duka abun yafi tsumata tace
"Yes,gaskiyanki shuhuda,u know what?,ina ganin ma fa soyayyar da yake mata akwai banbanci,i never ever seeing him rungume da su'ad,but ku dubu wannan fa,tana jikinsa,dan gararin idanunshi a wanke,na tabbata ya ganmu but ko a jikinsa,kai i love this man wallahi naso ace ni na samu wannan sa'ar,dole eesha ta shiga wani hali" ta fada abun na tsumata,ci gaba sukayi da tattaunawa kowa na fadin albarkacin bakinsa,'yammata ne dabkowacce ke jin ta burunqasa,kowacce tana burin zamantowa suruka cikin gidan,wadda dukkansu sun kwana da sanin cewa a gurinsu babbar sa'a ce ka zama wani ahali na jini cikin gidan,ko yaya sha'ani yake na gidan basa wasa da shi,mutane ne masu son budawa da kuma babbar harka,idan kuwa suka iso gidan suna samun dukkanin yadda suke so,duk da kowaccensu mahaifinta ba baya bane shima,saidai hausawa sunce baba ma da babansa,kafi wani wani ya fika,haka Allah ya qaddari rayuwarmu,yadda da hakan kadai shi zai sama maka rayuwa mai cike da wadatar zucci,da kuma cikakkiyar godiya ga Allah bisa dukkan wani bigire da ya azaka,Allah kasa mu dace,ka bamu wadatar zuci wadda itace babbar wadata itace babban arziqin duniya.

Sannu a hankali suke takowa zuwa bangaren ummi,jifa jifa suna wuce mutane da suka yo sammakon zuwa bikin tun farkon satin,sanye take da abaya baqa mai zubin dinkin buba,ta yane kanta da mayafin rigar,yayin da yake sanye da qananun kaya shirt da trouser baki daya shima baqaqe,zo kaga wani kyau da sukayi,musamman da yake riqe da hannunta saboda yadda ya lura akwai yawaitar 'yan sanya idanu,takanji wani nauyi duk sanda ta tuna yadda ya ritsata awa daya da suka shude a toilet daure da towel tana shirin yin wanka,yana jaddada mata wajibcin yin wankansu tare fuska daure,saidai baki daya yanayin da ya ganta ya sakar masa da jiki,ya zuba masa kasala da wani irin feeling a jikinsa,yayin data yayibi wani towel din ta rufe kanta hakan ya tunzurashi ya dinga takowa inda take har ya qureta a bango
"Yau zaki san kinyi kuskure,me kike boyemin" ya ambata yana dauke towel din dake kanta,gashinta ya bazu zuwa kafadarta,abinda ke sake burgeshi da tafiya da shi kenan,baya ta sake ja taha qoqarin boyewa cikin jacuzzi,cikin sa'a ya samu nasarar danqo ta,idanunta suka fito ganin yana niyyar sanyata cikin bathtube,tsoron dama yake son gani cikin idanunta,wani abu daban take koma masa mai kyau,bai bari ba kuwa sai daya sanyata sannan ya soma rage kayan jikinsa
"Saiki jira na gama nawa wakan sannan kiyi naki tunda baki son muyi tare sannan kuma cikin toilet dina kike ba naki ba"
"Amma ka bari na fita idan ka gama na dawo"
"Is too late" ya fada ko a jikinsa yana tubewa abinsa,idanuwanta ta runtse sanda yake qoqarin cire bixer din da shi kadai ya rage,sai qyarma take,bata taba ganin jiki mai lullube da siffar qarfi haka muraran a gabanta ba,gargasar jikinsa kawai abar kallo ce,karon farko data soma ganinsa a hakan,ko a jikinsa ya kammala wankansa tas sannan ya nade jikinsa da towel ya fice.

Dawowa tayi daga duniyar data tafi sanda taji yana matsa hannunta,tuni sun iso qofar falon ummeen ita yake jira ta cire takalmanta,a nutse ta zaresu sannan suka sanya kai ciki,shi yayi sallama yayin da suka jiyo muryar ummee tana amsawa,kunya da nauyi suka cika sumayyan,kamar ta koma bayanshi ta boye haka ta dinga ji,tana qoqarin zame hannunta dake cikin nashi amma yaqi bata dama,saima rada daya soma yi mata
"I want to show them i care with amanar da suka bani,nasan haka ne so ya kamata suma su gani,sai suyi alqalancin waye ya kasa kula da tashi amanar ko?" Sunne kai tayi ganin idanun ummee na kansu,fuskarta dauke da murmushi da kuma mamaki,don ta taji yara na fadin zuwan nashi bata yarda ba,don an riga da an saba,yawanci sai ana ya gobe daurin aure yake zuwa,wani lokaci ma sai ran daurin auren,awa daya kafin a daura ko minti talatin,musamman idan na yaran 'yan uwa ne,suma sai na kusa saboda tsabar busy,amma yau sai gashi kwanaki shida saura a daura auren,wannan wane irin gagarumin canji ne haka ke tunkarar rayuwar yaron nata,bata gushe ba tana musu barka da isowa fuskarta tamkar gonar auduga,yayin da eesha dake gefe bata daga kai ba tana danne dannen waya har sai da taji muryarshi,karaf idanunta suka fada kansu,zumbur ta miqe tsaye tana rarraba idanu,kada dai ace ta fara samun matsalar idanuwa,wannan yarinyar ya aura?,ko daga bacci ta tashi duk sauyawar da taji da samun cikakkem hutu dake kwance a jikinta ba zata manta ta ba,haka kawai yarinyar ta tsaye mata a rai
"Mutanen UAE" haka ummin ke fada wanda wannan kawai ya isheta amsa,sai ta hau girgiza kai ta shige dakin da ta sauka da gudu,sai sannan hankalin ummen ya kai kai,takun gudunta yaja hankalin almustapha da ya kai sumayya har gaban ummee,kunyarta ta sake burgeshi karo na biyu musamman sanda ta zame daga samn kujera zuwa qasa gaban ummeen,abinda bai taba gani kenan ba wajen su'ad,yana zama kujerar dake daura da ummin yace
"Waccar fa?,sunzi zasu fara haukar nasu kenan ko?"
"Kai kuma kazo zaka fara kenan ba"
"A'a ummi ni ban da case da kowa,just su kiyaye rules din da na sawa zuwansu gidan nan"
"Allah fa ya kawo mu,amiran umman khalipha ya fama da wannan" ta fada tana duban sumayya,alamun qarfi taba ga mai qiba,daga yanayin fuskar almustapha kawai ya isa ya sanar mata akwai gagarumin sauyi daya fara nasar rayuwarsa,yanayinsa baki daya akwai sauyi koda shi din bai san ko ya lura da hakan ba,kunya ta sake kamata tayi qas da kai tana gaidata,ta amsa cike da kulawa da farinciki,shima tashi gaisuwar ya dora ta amsa cikin jin dadi tana tambayarsu ya suka baro dubai
"Sai kuma gaku tun yau?" Ta tambaya cikin mamaki,satar kallonta yayi wanda ummin ta kula da haka
"Eh ummi,akwai wani aiki da nakeson yi,shi ya taso ni dole,tunda naga yayi daidai da date din daurin auren" ta fahimci salon magana ce kawai ta qwatar kai,tunda da aiki ne da tuni ya shaidawa baba,amma ko baban baisan da zuwanshi ba.

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

8⃣7⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

*SANARWA DA BABBAR MURYA*

*BA NUFIN MU CIN ZARAFIN WANI KO BATAWA WANI BA,SABODA GUDUN RUBUTA MUNANAN AYYUKA CIKIN LITTAFIN AYYUKANMU,WANDA SAI MUN TSAYA GABAN UBANGIJI MUNYI BAYANI RANAR GOBE QIYAMA,AMMA TURA TA KAI BANGO,AN FARA SHIGA SHINGENMU ANA MANA BARNA,BAYAN MUN KAME KANMU DAGA DUKKAN WANI ABU DA ZAI ZAMA SHIGA HURUMUN WANI BATANCI KO CIN ZARAFI A GAREMU*

*GAREKU MASU SATAR FASAHA ZANCE KO BARAYIN ZAUNE*

*Ina mai shaidawa duk wani mahaluki da yasan cewa yaci da gumi na,ya dauki wani littafi nawa da na zauna na bata lokacina na rubutashi da hannu na don al'ummar ma'aiki su amfana,MALLAKINA ya kaishi wane waje ya saida yana zuba kudin a aljihunsa cewa NI SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA BAN YAFE BA,BAN YAFE BA,BAN YAFE BA,KUMA INA ROQON ALLAH YAYI MIN SAKAYYA KAYANA DA AKA DAUKA ANA SAIDAWA*

*GAREKA KO GAREKI BARAUNIYA A OKADA,DUK WANDA YA SANSHI KO YA SANTA YA ISAR MASA/TA*

*ABADAN DAYA SATA KOTA SATA,AKA KAISHI OKADA ANA SAIDAWA AKAN KUDI NAIRA DARI BIYU,NACE ALLAH YA ISA BAN YAFE BA,INA ROQON ALLAH KUMA YA FITAR MIN HAQQI NA MATUQAR BANI NA ZALUNCESU BA SU SUKA ZALUNCENI,TUNDA BAN TABA DAUKAR HAQQIN WANI MALLAKIN WANI NA MAIDA SHI MALLAKINA BA,ALLAH YA BIMIN HAQQINA,INA FATAR ZAKU SADAR DA WANNAN SAQO ZUWA GARESU*

*SANNAN WANNAN LITTAFI DA NAKE RUBUTAWA DAMA SAURAN LITTATTAFAINA,MALLAKINA NE,NA YISHI NE KYAUTA BA NA SAIDAWA BA,A DUK SANDA NAKE DA BUQATAR SAIDAWA ZAN SIYAR DIN,AMMA BAN BAIWA KOWA IZINI YA SIYAR MIN BA,WANDA KUMA YAYI HAKAN NA BARSHI DA FITOWAR RANA DA FADUWARTA,NA BARSHI DA MAI SAMA,MUGA ALFANUN DA ZAI SAMU CIKIN KUDIN DA KA SAMU TA HANYAR SAIDA ABUN SATA*

*WALLAHI WALLAHI ALLAH MU GUJI CIN HAQQIN WANI,BILLAHILLAZAI LA ILAHA ILLA HUWA DUK WANDA KA GANSHI RAN QIYAMA YA QETARE TO BABU HAQQIN WANI A KANSHI,WANNAN ALQAWARI NE NA UBANGIJI,SAI YA FITARWA DA DUK WANI BAWA HAQQINSA KAN DAN UWANSA,KODA DABBA CE TA ZALUNCI 'YAR UWARTA DABBA*

*ALLAH KASA MU DACE*
_____________________________________
Chapter 170 · 0% Book details