Sashe 24
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tsakar gida ta tadda maman zaune saman tabarma sai fitilar qwai dake kunne a gefanta kasancewar babu wutar nepa,ba kowa tsakar gidan sai ita kadai
"A'ah,sumayya da kece haka da daren nan?" Mama ta fada tana sake bude tabarmar da take kai,gefanta ta qaraso ta zauna bakinta yaqi rufuwa
"Wallahi mama nice,ke kadai ce?"
"Eh duka sun tafi makarantar dare,amma gab suke da dawowa"
"Malam fa?"
"Sun tafi dubiya asibitin murtala shi da abubkar,maqwafcin mu malam sule ba lafiya"
"Ayyah baba sule,Allah ya sawwaqe......bari na yiwa yaya mukhtar din magana to ya shigo ku gaisa"
"Au tare ashe kuke......maza shigo da shi" inji mama tana janyo hijabinta dake gefanta ta zura.
Cikin girmama juna suja gaisa sannan ya fada mata motarsa ya kawo su sa mata albarka,tayi kuwa addu'a sosai don babu damar ta leqa malam din baya nan,nan ya fice qofar gida ya barsu.
Bai jima da fitar ba mama ta matsa mata ta shi su tafi tunda zasu gidan yahanasu,ta miqe suka yi sallama da maman ta fito.
Sai ta tadda mukhtar din da su zainab da halima ya bude musu motar suna ciki,malam kuma yana gefe da alama isowarsa shi kenan don gaisawa ma suke,ta qarasa cikin girmamawa itama tabi sahun mukhtar ta duqa ta gaidashi sannan ta gaida ya abbakar,ya shiga tsokanarta ta hanyar cewa tayi qiba ta zama lukuta me mukhtar ke dura mata ita kadai,ta kasa tanka masa sai dariya da takeyi kanta a qasa saboda kunyar malam da takeyi.
"Ai sai ku wuce ko kada dare ya muku" cewar malam yana shigewa gidan bayan sunyi sallama,mukhtar ya fidda dubu biyu ya bawa su halima yace su sayi kayan kwalliya,qin karba sukayi sai da sumayyan ta sanya baki sannan suka amsa auna godiya suka shige gidan.
Shiru ya biyo baya cikin motar,mukhtar ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Tarbiyyan gidanku na birgeni sumayya,naso a ce ina da wani dan uwa namiji da babu shakka sai na aura masa halima ko zainab" murmushi kawai sumayyan tayi sabida tasan koda yana da dan uwan babu ta yadfa su yaya yahanasu su yadda su sake hada zuri'a da 'yan gidansu.
Mintina qalilan suka isa gidan,ya kashe motar ya fice ta bishi a baya bakinta cike da addu'a.
Dukansu suna tsakar gida zaune kan tabarma suma saboda zafin dake dan busawa a 'yan kwanakin,ga matsalar rashin isashshiyar wutar lantarki da muke fama da ita ta kowanne bangare na qasar nan.
Da fara'ar ta ta amsa sallamar amma jin muryar sumayya yasa ta gintse 'yar fara'ar data yo tsaraba,jamila dake gefen tabarmar ta matsa ma mukhtar,yayin da sayyada taqi motsawa ko su samawa sumayya wani abun zaman,hakanne ya sanya mukhtar din dubanta fuska a hade
"Ke,tashi ki bata guri" tuni ta miqe saboda tana shakkarsa kuma tasan halinsa sarai,daki suka shige ita da jamilan baki daya.
A girmame yake gaisheta ta amsa sannan sumayya ta gaidata,sama sama ta amsa mata suka shiga hira da mukhtar din.
Jamila ta fito da ruwan pure water mai sanyi guda biyu ta cup ta ajjiye gaban mukhtar din sai ya turasu duja gaban sumayyan yana cewa
"Bude kisha,kince min kina jin qishirwa dazu" zuciyar yaya yahansu ta tunzura,ta dinga jifansu da harara tana qwafe da su,ya maida dubansa gun yaya yahanasun
"Mota na kawo miki ki gani yaya,ta iso dazun da safe" sai ta harareshi
"Au shine sai yanzu kaga damar kawo min na gani kenan sai da ka gama nunawa duniya"
"Ba haka bane,data iso din ma a gareji na wuni ana mata service,ina dawowa gida kuma nayi wanka naci abinci muka taho kawo miki"
"Sai kace makaho da baka iya tahowa kai kadai,kai Allah ya kyauta,ya warware mana wannan masifar" ta fadi cike da haushi da tsana,don ya kauda zamcan don kada yayi nisa sai ya miqe yana fadin suzo su ga motar,haka suka miqe suka fice suna hayaniyar murna,tana zaune gun burinta kawai yace ta taso su tafi,Allah ya taimaketa sayyada ta leqo tace ta fito su tafi.
Tana zaune gaban motar shima haka amma sai zuba zance yayan taje wanda ya hana musu tafiya
"To Allah ya tsare ya rabaka da sharrin masu sharri,Allah ya qara budi ya kawo masu yi maka addu'a ya rabaka da wannan matsiyacin zaman kadaicin" bai amsa ba ya ciro dubu uku ya miqa mata yana fadin
" ga wannan ku qara"hannu tasa ta karba zata sake barkewa da wani surutun ya samu yaja motar suka wuce.
Duk yadda taso boye damuwarta amma sai da ya fuskanta,kan dole yake zuwa da ita gidan saboda yaya yahanasun dolensa ce,amma banda haka da tuni ta bar zuwan gidan,da tuni ya yanke alaqar dake tsakaninsu,kan hanya ya tsaya ya siya musu yoghourt manyan roba biyu masu sanyi da tsire mutumin sumayyan don duk ya faranta mata,a hankali ya dinga janta da hira da labarukan ban dariya,sosai ta sake sake masa jiki tana qyaqyata dariya wanda hakan shima ya masa dadi.
*~TSUGUNNE BATA QARE BA~*
Shi da ita duka suna zaune cikin falon nata da ya sake gyara mata shi,sanye suke da kayan barci saidai sai banbanta gun zama da ayyukan yi,shi yana zaune kan qaramar kujera ta zaman mutum daya dauke da computer yana aiki,yayin da ita ke kwance saman doguwar kujera tana kallo a tashar mbc inda suke hasko film din ashqui,kusan bata taba zama ta kalli film din complete ba sai yau.
Dakin ya dauki shiru kasancewar kowa ya bada muhimmanci kan abinda yakeyi,wayar mukhtar dake saman jakar laptop dinsa ta dauki tsuwwa,ya dubi wayar sai yaga baquwar lamba ce,kusan ya jima da daina daukar ire iren lambobin,to amma sunyi da wani costumer dinsa zaya kirashi kan wasu kaya da zai siya a shagonsa,sai yayi zaton shine saboda haka ya daga
"Assalamu alaikum" mukhtar din ya fada,kana yayi jim kusan daqiqa talatin sannan ya sake cewa
"Wacce zainab?,daga ina?" Ya sake yin shiru na sakan biyar sannan ya ja tsaki ya kife wayar yaci gaba da binda yakeyi.
Ba'a cika minti biyar ba wani kiran ya kuma shigowa,ya dubi wayar ba tare da yayi niyyar dagawa ba,lambar dazun ce dai sai ya sake dauke kansa yaci gaba da abinda yakeyi din ransa na quna.
Kiran da aketa maimaitawa a kai akai shi ya dami sumayya har ya ja hankalinta,tana daga kwancen ta dubeshi
"Don Allah yaya mukhtar ka daga,wallahi ta dameni" ta fada a shagwabe,bai dubeta ba yace
"Bazan daga ba,barta kawai" sai ta maida kallonta din batason ko gu daya ya wuceta.
Bai haqura ba mai kiran yaci gaba da nacin kiran har sai da sumayyan ta sake tankawa ya bata amsa irin ta dazun,sai ta tashi zaune tana gyara wuyan rigar barcinta da ya salube tare da fadin
"Shikenan,bari ni na daga maka ko a bar kunnuwanmu su huta"
"Kema ba zaki daga ba" ya fada bayan ya dago idonsa wannan karon ya dubeta,dariya ta saka tana tunanin wasa yake mata,dai dai lokacin da kiran ya sake shigowa ta sanya hannunta da sauri ta suri wayar ta daga ta kara a kunnenta tana masa gwalon taci nasara ta daga ba tare da wafce ba kamar yadda yayi niyyar yi da farko.
A hankali ta cire wayar daga kunnenta qirjinta na bugawa jin muryar macace tana gaya mata mukhtar take nema,miqa masa wayar tayi jiki a sanyaye.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣2⃣
_______________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*ma yaftahillahu lin nasi min rahmatin fala mumsika laha,wama yumsik fala mursilalahu bin ba'a dihi*
_Allah ka sanya mu daga cikin wadanda zaka yita saukar da rahamarka garesu,alfarmar sayyadina rasulullahi S A W_
_______________________________
Hannu ya sanya ya amsa,sai ya latse wayar ya kasheta baki daya ya ajjiyeta gefansa yaci gaba da aikinsa,wanda yana duba yanayin ginin gidansa wanda a yanzun ake daf da kammalashi
"Sai da na gaya miki kada ki daga" ya fadi idanunsa na kan computer din,cikin wata iriyar mutuwar jiki da kasala ta lallaba ta koma kan kujerar data tashi taci gaba da kallonta,saidai sam ta daina fuskantar komai,wani abu mai kama da zazzafan kishi ne ya shiga taso maga,ta dinga ambaton sunan Allah har zuwa sanda suka qare film din ta koma dakin gadonta.
Sam bacci yaqi zuwa mata face nazari da take tayi ita kadai har mukhtar din ga gama abinda zaya yi ya cimmata akan gadon,jikinsa ya janyota sannan cikin taushin murya yace
"Meke faruwa ne sumy uhmmm?"
"Babu komai" ta furta can qasan maqoshinta
"Ban santa ba nina sumayya,abinda kawai na sani customer dina ce,tazo shago na siyayya ita da 'yan uwanta,ta buqaci number dita saboda koda zasu tashi zuwa wani lokaci,tun daga ranar take matsanta min da kira ba yau ta fara ba,na gargadeta na kuma ja mata kunne amma bata ji ba,wannan shine abinda na sani" shiru sumayyan tayi taba nazarin maganar,sosai wani kishinsa ke taso mata
"Allah ya kyauta" ta iya cewa kawai,sai ya juyo da ita ta fuskanceshi
"Haka ma kadai zaki fada ko?,wato ma baki kishi na kenan sumayya" ya fada yana matse mata yatsu har sai da taji zafi ta saki 'yar qaramar qaara,sai ya hade bakinsa da nata cikin wani irin salo da ya mantar da su komai
*** *** ***
Ta maida kiransa ya zame mata tamkar ibada,idan ma bai daga ba zata yita jelan tura masa saqonni iri iri wadanda dukkaninsu a akwatin share saqonni yake zuba su.
Sau tari wani abun dariya yake bawa sumayya,tana mamakin yadda mata suka sauke farashinsu ya fadi qasa warwas,tana jin inda ita dince sam ba zata iya haka ba,ko babu komai akwai kunya irin ta diya mace,duk da ta sani cewa koda matar ma'aiki ta farko nana khadijatul kubra ta nemi ma'aiki da ya aureta,amma bata irin wannan sigar bace,ta siga ce mai tsafta,mai ban sha'awa mai cike da hankali nutsuwa da kuma KARAMCI,sa'an nan ta nemi a aureta a inda take da yaqinin samun qauna da kulawa,a 'inda ko babu qauna akwai tausayi girmamawa da kuma MUTUNCI.
"A'ah,sumayya da kece haka da daren nan?" Mama ta fada tana sake bude tabarmar da take kai,gefanta ta qaraso ta zauna bakinta yaqi rufuwa
"Wallahi mama nice,ke kadai ce?"
"Eh duka sun tafi makarantar dare,amma gab suke da dawowa"
"Malam fa?"
"Sun tafi dubiya asibitin murtala shi da abubkar,maqwafcin mu malam sule ba lafiya"
"Ayyah baba sule,Allah ya sawwaqe......bari na yiwa yaya mukhtar din magana to ya shigo ku gaisa"
"Au tare ashe kuke......maza shigo da shi" inji mama tana janyo hijabinta dake gefanta ta zura.
Cikin girmama juna suja gaisa sannan ya fada mata motarsa ya kawo su sa mata albarka,tayi kuwa addu'a sosai don babu damar ta leqa malam din baya nan,nan ya fice qofar gida ya barsu.
Bai jima da fitar ba mama ta matsa mata ta shi su tafi tunda zasu gidan yahanasu,ta miqe suka yi sallama da maman ta fito.
Sai ta tadda mukhtar din da su zainab da halima ya bude musu motar suna ciki,malam kuma yana gefe da alama isowarsa shi kenan don gaisawa ma suke,ta qarasa cikin girmamawa itama tabi sahun mukhtar ta duqa ta gaidashi sannan ta gaida ya abbakar,ya shiga tsokanarta ta hanyar cewa tayi qiba ta zama lukuta me mukhtar ke dura mata ita kadai,ta kasa tanka masa sai dariya da takeyi kanta a qasa saboda kunyar malam da takeyi.
"Ai sai ku wuce ko kada dare ya muku" cewar malam yana shigewa gidan bayan sunyi sallama,mukhtar ya fidda dubu biyu ya bawa su halima yace su sayi kayan kwalliya,qin karba sukayi sai da sumayyan ta sanya baki sannan suka amsa auna godiya suka shige gidan.
Shiru ya biyo baya cikin motar,mukhtar ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Tarbiyyan gidanku na birgeni sumayya,naso a ce ina da wani dan uwa namiji da babu shakka sai na aura masa halima ko zainab" murmushi kawai sumayyan tayi sabida tasan koda yana da dan uwan babu ta yadfa su yaya yahanasu su yadda su sake hada zuri'a da 'yan gidansu.
Mintina qalilan suka isa gidan,ya kashe motar ya fice ta bishi a baya bakinta cike da addu'a.
Dukansu suna tsakar gida zaune kan tabarma suma saboda zafin dake dan busawa a 'yan kwanakin,ga matsalar rashin isashshiyar wutar lantarki da muke fama da ita ta kowanne bangare na qasar nan.
Da fara'ar ta ta amsa sallamar amma jin muryar sumayya yasa ta gintse 'yar fara'ar data yo tsaraba,jamila dake gefen tabarmar ta matsa ma mukhtar,yayin da sayyada taqi motsawa ko su samawa sumayya wani abun zaman,hakanne ya sanya mukhtar din dubanta fuska a hade
"Ke,tashi ki bata guri" tuni ta miqe saboda tana shakkarsa kuma tasan halinsa sarai,daki suka shige ita da jamilan baki daya.
A girmame yake gaisheta ta amsa sannan sumayya ta gaidata,sama sama ta amsa mata suka shiga hira da mukhtar din.
Jamila ta fito da ruwan pure water mai sanyi guda biyu ta cup ta ajjiye gaban mukhtar din sai ya turasu duja gaban sumayyan yana cewa
"Bude kisha,kince min kina jin qishirwa dazu" zuciyar yaya yahansu ta tunzura,ta dinga jifansu da harara tana qwafe da su,ya maida dubansa gun yaya yahanasun
"Mota na kawo miki ki gani yaya,ta iso dazun da safe" sai ta harareshi
"Au shine sai yanzu kaga damar kawo min na gani kenan sai da ka gama nunawa duniya"
"Ba haka bane,data iso din ma a gareji na wuni ana mata service,ina dawowa gida kuma nayi wanka naci abinci muka taho kawo miki"
"Sai kace makaho da baka iya tahowa kai kadai,kai Allah ya kyauta,ya warware mana wannan masifar" ta fadi cike da haushi da tsana,don ya kauda zamcan don kada yayi nisa sai ya miqe yana fadin suzo su ga motar,haka suka miqe suka fice suna hayaniyar murna,tana zaune gun burinta kawai yace ta taso su tafi,Allah ya taimaketa sayyada ta leqo tace ta fito su tafi.
Tana zaune gaban motar shima haka amma sai zuba zance yayan taje wanda ya hana musu tafiya
"To Allah ya tsare ya rabaka da sharrin masu sharri,Allah ya qara budi ya kawo masu yi maka addu'a ya rabaka da wannan matsiyacin zaman kadaicin" bai amsa ba ya ciro dubu uku ya miqa mata yana fadin
" ga wannan ku qara"hannu tasa ta karba zata sake barkewa da wani surutun ya samu yaja motar suka wuce.
Duk yadda taso boye damuwarta amma sai da ya fuskanta,kan dole yake zuwa da ita gidan saboda yaya yahanasun dolensa ce,amma banda haka da tuni ta bar zuwan gidan,da tuni ya yanke alaqar dake tsakaninsu,kan hanya ya tsaya ya siya musu yoghourt manyan roba biyu masu sanyi da tsire mutumin sumayyan don duk ya faranta mata,a hankali ya dinga janta da hira da labarukan ban dariya,sosai ta sake sake masa jiki tana qyaqyata dariya wanda hakan shima ya masa dadi.
*~TSUGUNNE BATA QARE BA~*
Shi da ita duka suna zaune cikin falon nata da ya sake gyara mata shi,sanye suke da kayan barci saidai sai banbanta gun zama da ayyukan yi,shi yana zaune kan qaramar kujera ta zaman mutum daya dauke da computer yana aiki,yayin da ita ke kwance saman doguwar kujera tana kallo a tashar mbc inda suke hasko film din ashqui,kusan bata taba zama ta kalli film din complete ba sai yau.
Dakin ya dauki shiru kasancewar kowa ya bada muhimmanci kan abinda yakeyi,wayar mukhtar dake saman jakar laptop dinsa ta dauki tsuwwa,ya dubi wayar sai yaga baquwar lamba ce,kusan ya jima da daina daukar ire iren lambobin,to amma sunyi da wani costumer dinsa zaya kirashi kan wasu kaya da zai siya a shagonsa,sai yayi zaton shine saboda haka ya daga
"Assalamu alaikum" mukhtar din ya fada,kana yayi jim kusan daqiqa talatin sannan ya sake cewa
"Wacce zainab?,daga ina?" Ya sake yin shiru na sakan biyar sannan ya ja tsaki ya kife wayar yaci gaba da binda yakeyi.
Ba'a cika minti biyar ba wani kiran ya kuma shigowa,ya dubi wayar ba tare da yayi niyyar dagawa ba,lambar dazun ce dai sai ya sake dauke kansa yaci gaba da abinda yakeyi din ransa na quna.
Kiran da aketa maimaitawa a kai akai shi ya dami sumayya har ya ja hankalinta,tana daga kwancen ta dubeshi
"Don Allah yaya mukhtar ka daga,wallahi ta dameni" ta fada a shagwabe,bai dubeta ba yace
"Bazan daga ba,barta kawai" sai ta maida kallonta din batason ko gu daya ya wuceta.
Bai haqura ba mai kiran yaci gaba da nacin kiran har sai da sumayyan ta sake tankawa ya bata amsa irin ta dazun,sai ta tashi zaune tana gyara wuyan rigar barcinta da ya salube tare da fadin
"Shikenan,bari ni na daga maka ko a bar kunnuwanmu su huta"
"Kema ba zaki daga ba" ya fada bayan ya dago idonsa wannan karon ya dubeta,dariya ta saka tana tunanin wasa yake mata,dai dai lokacin da kiran ya sake shigowa ta sanya hannunta da sauri ta suri wayar ta daga ta kara a kunnenta tana masa gwalon taci nasara ta daga ba tare da wafce ba kamar yadda yayi niyyar yi da farko.
A hankali ta cire wayar daga kunnenta qirjinta na bugawa jin muryar macace tana gaya mata mukhtar take nema,miqa masa wayar tayi jiki a sanyaye.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣2⃣
_______________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*ma yaftahillahu lin nasi min rahmatin fala mumsika laha,wama yumsik fala mursilalahu bin ba'a dihi*
_Allah ka sanya mu daga cikin wadanda zaka yita saukar da rahamarka garesu,alfarmar sayyadina rasulullahi S A W_
_______________________________
Hannu ya sanya ya amsa,sai ya latse wayar ya kasheta baki daya ya ajjiyeta gefansa yaci gaba da aikinsa,wanda yana duba yanayin ginin gidansa wanda a yanzun ake daf da kammalashi
"Sai da na gaya miki kada ki daga" ya fadi idanunsa na kan computer din,cikin wata iriyar mutuwar jiki da kasala ta lallaba ta koma kan kujerar data tashi taci gaba da kallonta,saidai sam ta daina fuskantar komai,wani abu mai kama da zazzafan kishi ne ya shiga taso maga,ta dinga ambaton sunan Allah har zuwa sanda suka qare film din ta koma dakin gadonta.
Sam bacci yaqi zuwa mata face nazari da take tayi ita kadai har mukhtar din ga gama abinda zaya yi ya cimmata akan gadon,jikinsa ya janyota sannan cikin taushin murya yace
"Meke faruwa ne sumy uhmmm?"
"Babu komai" ta furta can qasan maqoshinta
"Ban santa ba nina sumayya,abinda kawai na sani customer dina ce,tazo shago na siyayya ita da 'yan uwanta,ta buqaci number dita saboda koda zasu tashi zuwa wani lokaci,tun daga ranar take matsanta min da kira ba yau ta fara ba,na gargadeta na kuma ja mata kunne amma bata ji ba,wannan shine abinda na sani" shiru sumayyan tayi taba nazarin maganar,sosai wani kishinsa ke taso mata
"Allah ya kyauta" ta iya cewa kawai,sai ya juyo da ita ta fuskanceshi
"Haka ma kadai zaki fada ko?,wato ma baki kishi na kenan sumayya" ya fada yana matse mata yatsu har sai da taji zafi ta saki 'yar qaramar qaara,sai ya hade bakinsa da nata cikin wani irin salo da ya mantar da su komai
*** *** ***
Ta maida kiransa ya zame mata tamkar ibada,idan ma bai daga ba zata yita jelan tura masa saqonni iri iri wadanda dukkaninsu a akwatin share saqonni yake zuba su.
Sau tari wani abun dariya yake bawa sumayya,tana mamakin yadda mata suka sauke farashinsu ya fadi qasa warwas,tana jin inda ita dince sam ba zata iya haka ba,ko babu komai akwai kunya irin ta diya mace,duk da ta sani cewa koda matar ma'aiki ta farko nana khadijatul kubra ta nemi ma'aiki da ya aureta,amma bata irin wannan sigar bace,ta siga ce mai tsafta,mai ban sha'awa mai cike da hankali nutsuwa da kuma KARAMCI,sa'an nan ta nemi a aureta a inda take da yaqinin samun qauna da kulawa,a 'inda ko babu qauna akwai tausayi girmamawa da kuma MUTUNCI.