Sashe 195
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A daidai wannan lokacin almustapha ne zaune bakin system yana aiki,tun yanayi da qarfinshi tuquru har ya soma gazawa,baki daya ta tafi da dukkan wani walwala da karsashinsa,hatta da manya da qananun ma'aikata sunsan walwalar yallabai ta ragu,duk da dama can shi ba mai yawan fara'a bane,amma karsashinsa da son aikinsa cikin kaso dari babu hamsin,hannunshi ya dora saman kanshi yana shafa bayan ya jinginar da bayanshi jikin makarin kujerar,a hankali zuciyarshi ke masa quna,wani bala'in qishirwarta na ratsashi,ji yake a lokacin da yana da ikon komawa tsuntsu ba abinda zai hanashi yin fiffike ya isa gareta,duk wani qwarin qwiwa da burin yin aiki da ya taho da shi babu su duka sun yi nasu guri,duk wani alwashi da yaci na nesantarta tunda bata buqatar zama tare da shi ya ruguje,kwanaki bawaki kacal da baiji ta jinsa yake tamkar wani dabaj cikin jinsin mutane,yanzu haka cikin jikinshi zuciyarsa ke gaya masa idanunta biyu batayi bacci ba,idanunsa ya bude ya janyo wayarsa kamar ko yaushe,ya bude hotonya tun wanda tayi cikin wayar sanda suna dubai da doguwat riga,hotunan da yayi mata a dubai garden glow wanda batasan da su ba,wadanda sukayi bala'in yin kyau,tamkar ta kirata ta amsa,hannunshi ya sanya yana shafar fuskar tata,kewayaen labbanta wadanda idan ya tuna taushinsu tsingar jikinsa ke zubawa,kyakwawan idanunta da kwantacciyar sumarta,tamkar wanda aka bawa aikin zana taswirar fuskarta haka ya dinga zooming yana qare mata kallo,wata wawuyar ajiyar zuciya ya saki tana jin zuciyarshi kamar zata fito waje,ba tare da ya shirya ba ya samu kanshi da yin dialing number dinta,ya zubawa wayar ido yana sauraren jin koda saukar numfashinta ne,saidai wayar harta qaraci rurinta ta tsinke ba'a daga ba.
Sumayyan na zaune dirshan a inda tayi aman tana maida numfashi,ta hangi wayar na haske,saidai ko data miqe ta dauko taga number dinshi ce sai ta maidata ta ajjiye,ranta na wani irin baci,sai yau zaya nemeta,sai yau yaga daman magana da ita?,wato kota mutu ko tayi rai ko?tunda yana da wata matar,zuciyar kishi ta soma saqa mata wannan maganan,hawaye ne ya balle mata wani mahaukacin kishin su'ad na ratsata,ta shiga toilet ta dauko mopper ta gyara wajem fes sannan ta dawo saman kujera ta zauna tana maida numfashi,tana kallon wayar nata fidda haske alamun kira ne,amma saita lumshe idanunta ma ta daina ganin wulgawar haskenta baki daya,hangoshi kawai take shi da su'ad cikin walwala wanda hakan shi ya sanya kenan ita ya bagarar da ita.
Baki daya hankalinsa ya dugunzuma,tunda yake ita ce mutum ta farko a duniya daya taba kira sama da sau biyu,duka shi ba wannan bace damuwarshi,me ya hanata daga kiranshi bayan jikinsa na bashi idanunta biyu?,tun yana zaune har sai da ya miqe tsaye,baisan sanda ya samu kansa yana kiran layin ummi ba ha tare daya tuna cewa dare ya fara nisa ba ko kuma tana wajen baba,cikin tsakiyar baccinta taji qarar wayar tata,dama ba wani nisa can baccin nata yayi ba,gama sallolin nafikarta kenan ta kwanta din ko hijabin jikinta bata cire ba,macace mai yawan tashi dare,bata fiya kashe darenta baki daya wajen yin bacci ba,sunan almustapha data gani ya dan sata faduwar gaba
"Lafiya dai almustapha sha biyu da minti biyar na dare?" Sai a sannan hankalinshi ya koma jikinshi,ya dan gyara muryarshi
"Aaaa.....dama....ba komai...inata kiran sumayyah bata daga bane" ajiyar zuciya ta saki
"Ka sani fa lokacin bacci je yanzu,kuma kasan muhimmancinsa wajen mace mai ciki,ka bari da safe ka kirata ko ita ta kiraka don na tabbata yanzun ta dade da yin bacci,don yau ana gama sallar isha'i taje ta kwanta" gabanshi ya soma faduwa,addu'a yake kada Allah yasa ummi ta tursasashi kan ya bari sai goben,shi kadai yasan me yake ji a qirjinsa game da ita,muryarta kawai yake da muradin ji,Allah yasa ta fahimceshi
"Batayi bacci ba ummi.....don Allah ko zaki hada....." Sai kuma ya kasa qarsawa,nayin ummin yake ji,itama a nata bangaren kasaqe tayi,tausayi irin na d'a da uwa ya kamata,ta tabbata ba zaya samu rabin kulawar da yake samu wajen sumayya ba,tsanin miji da mata sai Allah,kada kuma ta shiga haqqinsa da yawa
"Barin kai mata" cewar ummi
"Yauwa ummi thanks" ya fada cikin wani irin zumudi tare da sauke ajiyar zuciya wadda har sai da ummin ta jiyo,murmushi ta saki tana saukowa daga saman gadon,tasan halin yaronta sarai,tun yana qarami bai iya son abu ba,bai iya sanya abu a zuciya ba,duk abinda yake so bai riqonsa da wasa,hakan ya sanya tun da can baya ta duqufa masa addu'ar samun mace ta gari wadda zata masa yadda yake so ba tare data wahalar da shi ba.
Qofar dakin data ji an turo shi ya sanyata bude idanunta,suka hada ido da ummin sanda ta kunna wutar dakin
"Me kike zaune kikeyi amira?,da gasken ashe baki bacci ba"murmushi ta dan qaqalo
"gajiya nayi da kwanciyar sai na zauna na dan huta"
"Ko dai wani abu ke damunki?,ki gayan gaskiya" kai ta kada kanta a qasa
"A'ah ummi babu komai,kawai na gaji da kwanciya ne"
"To ko dakina zaki koma?" Ta fadi tana qarasowa gabanta
"Nan din ma yayi fa ummi"
"Indai akwai wani abu da bai miki dai dai da yadda kikeso kada kiyi nauyin baki ki sanar min......mijinki ne dama ya tasoni....maimakon ya kira taki wayar" ta fada tana dan murmushi tare da miqa mata wayar sannan ta juya zata fice
"Idan kin gama ki barta nan wajenki ko zuwa safiya na karba" ta fada tana ficewa tare da rufe mata qofar,wayar sumayya tabi da kallo sanda ta sake ruru,sunanshi ya fito baro baro,sai ta kauda kai kibiyar kishi na sukarta,wani kiran ne ya sake shigowa,a hankali ta shafa wajen amsawa ta daga ta kara a kunnenta
"Sumayyah!" Ya fada a tausashe cikin salon muryarshi dake ratsa zuciyarta,muryar nan da take mutuwar so,
"Sai yau kaga daman nemana?,ba ruwanka da hakin da nake ciki ko?,dama ba sona kake ba baka damu da ni ba...."
"Sumayyah" ya sake kiran sunanta karo na biyu ya katse ta a tausashe,kiran sunanta kadai ya karya mata zuciya kawai sai ta saki kukamai hade da sheshsheqa,idanunsa ya lumshe bugun zuciyarsa na qaruwa
"Ya salam!" Ya dinga furtawa can qasa tana shiga cikin kunnenta,ita kanta batasan me ya saka ta kukan ba,daga inda yake tsayen sai tsaiwar ta gagareshi,komawa yayi saman kujerar shima yayi kwance rigingine,wani dafi take zubawa zuciyarshi ba tare da ta sani ba,nadama ta kamashi,me yasa ya watsar da ita don kawai taqi binshi,shi kansa yasan cewa kansa da kansa ya hora,yama fita jigata,sabida shi din ya rasa komai,duk wani abu data sabar masa da shi a yanzu babu,sannu a hankali ta soma tsagaita kukan don kanta,bayan taji zuciyarta ya soma yin sanyi
"Kiyi haquri" ya fada kamar yana mata rada
"Ki yafemin.....na kasa sabawa ne.....na kasa daurewa rashinki....kamar maraya haka nake jina....am really sorry banyi da niyya ba" ajiyar zuciyar itama ta sauke,tana jin yadda kewarshi ke illatata,kalamanshi kamar sake tunzura qaunarsa suke cikin zuciyarta,saidai sarautar ta motsa,sai tayi mishi shuru kaman bada ita yake ba
"Summy....kice wani abu mana" yadda ya kira sunan nata sai taji kaman mukhtar,sake narkewa tayi cikin kujera ta kuma qi cewa komai din
"Samayyahh...." Ya kuma kiran sunanta,ya gane cewa kawai azabtar da shi take sonyi,kamar ya saki mata kuka haka yake ji
"Ki kulani ko don babynmu mana,i missed him alort shima fa" nan ba amsa,amma can qasan ranta wani sanyi na ratsata,wanda yayi tasiri har saman fuskarta,ta soma fidda wani boyayyen murmushi
"Wallahi tallahi na rantse idan baki ce min komai ba a gobe zaki ganni abuja" dariyar da take boyeea ta qwace mata,zata fi kowa son hakan,saidai bata masa adalci ba idan har tasa daga komawarsa cikin sati guda ya kashe kudin ticket dinshi ya sake dawowa,me zata cewa su ummi ya kawoshi
"My happiness...." Ta amsa mishi cikin wani irin salo wanda ya saukar da gungun farinciki wa zuciyarshi,ya sauke qatuwar ajiyar zuciya
"Ki tabbatar min da cewa kina lafiya keda baby na"a shagwabe tace
"ba wani.....bayan baka damu dani ni da babyn ba...."
"Ya ilahi....daina fada don Allah kada ki sani cikin wani hali.....ki fadi abunda zai miki yanzu wanda zan wanke kaina,wanda zai nuna miki tsantsar damuwar da nayi da ku"
"Just kiss me...." Ya subuce daga bakinta ba tare da tasan ta fadi hakan ba,wani wawan kiss ya bata ta cikin wayar wanda babu inda bai aika saqo ba cikin gangar jikinta da ruhinta sannan ya dora
"Ku raba ke da baby na"
"Baby yana godiya.....ka kwanta da safe mayi waya,sabida su'ad" ta hada kalaman da qyar,idanunshi ya daga ya dubi qofar bedroom din da take ciki,tunda suka zo ungulu ta koma gidanta na tsamiya,wani abun ma don yana taka mata birki ne
"Ban yarda ba" ya maidawa sumayya amsa
"Da gaske my happiness.....kaga idan ni kama haka ko bazanji dadi ba" shiru yayi yana murmushi kamar tana gabanshi,sunan data kirashi da shi ya tsaya masa
"Da gaske ni happiness dinki ne?"
"Sosai.....ban kuma sake tabbatar da hakan ba sai yanzu,na rasa farinciki da walwala na tsahon sati guda sabida batan dabo daka yiwa rayuwata,sai gashi cikin mintina qalilan da jin muryarka komai ya dawo min,farinciki na yadawo,sai tsananin kewarka da nake ji kamar zata rabani da ruhina..." Ta bashi amsa kai tsaye tare da katse kiran saboda tana ji tayi amfani da kalamai masu nauyi,mutuwar zaune kawai yayi daga wancan bangaren,kalan soyayyar da yake da buqata,kalan soyayyar da yake nema ido rufe yau gashi Allah ya bashi,baki daya ta gama kasheshi,dan qaramin ihu ya saki shi kadai kaman wanda ya soma zaucewa,gaskiya wannan karon baya jin zai iya bin umarnin su baba,ko sato matarshi sai yayi,bazai iya jurewa zama ba tare da ita ba,haka ya dinga jera kiranta amma tawi dagawa,daga bisani ta tura masa saqo tana shaida masa bacci zatayi sai da safe,wanda ita kanta bata gaji da jin muryarshi ba,tayi hakanne kawai don kada ta shiga hurumin su'ad.
Sumayyan na zaune dirshan a inda tayi aman tana maida numfashi,ta hangi wayar na haske,saidai ko data miqe ta dauko taga number dinshi ce sai ta maidata ta ajjiye,ranta na wani irin baci,sai yau zaya nemeta,sai yau yaga daman magana da ita?,wato kota mutu ko tayi rai ko?tunda yana da wata matar,zuciyar kishi ta soma saqa mata wannan maganan,hawaye ne ya balle mata wani mahaukacin kishin su'ad na ratsata,ta shiga toilet ta dauko mopper ta gyara wajem fes sannan ta dawo saman kujera ta zauna tana maida numfashi,tana kallon wayar nata fidda haske alamun kira ne,amma saita lumshe idanunta ma ta daina ganin wulgawar haskenta baki daya,hangoshi kawai take shi da su'ad cikin walwala wanda hakan shi ya sanya kenan ita ya bagarar da ita.
Baki daya hankalinsa ya dugunzuma,tunda yake ita ce mutum ta farko a duniya daya taba kira sama da sau biyu,duka shi ba wannan bace damuwarshi,me ya hanata daga kiranshi bayan jikinsa na bashi idanunta biyu?,tun yana zaune har sai da ya miqe tsaye,baisan sanda ya samu kansa yana kiran layin ummi ba ha tare daya tuna cewa dare ya fara nisa ba ko kuma tana wajen baba,cikin tsakiyar baccinta taji qarar wayar tata,dama ba wani nisa can baccin nata yayi ba,gama sallolin nafikarta kenan ta kwanta din ko hijabin jikinta bata cire ba,macace mai yawan tashi dare,bata fiya kashe darenta baki daya wajen yin bacci ba,sunan almustapha data gani ya dan sata faduwar gaba
"Lafiya dai almustapha sha biyu da minti biyar na dare?" Sai a sannan hankalinshi ya koma jikinshi,ya dan gyara muryarshi
"Aaaa.....dama....ba komai...inata kiran sumayyah bata daga bane" ajiyar zuciya ta saki
"Ka sani fa lokacin bacci je yanzu,kuma kasan muhimmancinsa wajen mace mai ciki,ka bari da safe ka kirata ko ita ta kiraka don na tabbata yanzun ta dade da yin bacci,don yau ana gama sallar isha'i taje ta kwanta" gabanshi ya soma faduwa,addu'a yake kada Allah yasa ummi ta tursasashi kan ya bari sai goben,shi kadai yasan me yake ji a qirjinsa game da ita,muryarta kawai yake da muradin ji,Allah yasa ta fahimceshi
"Batayi bacci ba ummi.....don Allah ko zaki hada....." Sai kuma ya kasa qarsawa,nayin ummin yake ji,itama a nata bangaren kasaqe tayi,tausayi irin na d'a da uwa ya kamata,ta tabbata ba zaya samu rabin kulawar da yake samu wajen sumayya ba,tsanin miji da mata sai Allah,kada kuma ta shiga haqqinsa da yawa
"Barin kai mata" cewar ummi
"Yauwa ummi thanks" ya fada cikin wani irin zumudi tare da sauke ajiyar zuciya wadda har sai da ummin ta jiyo,murmushi ta saki tana saukowa daga saman gadon,tasan halin yaronta sarai,tun yana qarami bai iya son abu ba,bai iya sanya abu a zuciya ba,duk abinda yake so bai riqonsa da wasa,hakan ya sanya tun da can baya ta duqufa masa addu'ar samun mace ta gari wadda zata masa yadda yake so ba tare data wahalar da shi ba.
Qofar dakin data ji an turo shi ya sanyata bude idanunta,suka hada ido da ummin sanda ta kunna wutar dakin
"Me kike zaune kikeyi amira?,da gasken ashe baki bacci ba"murmushi ta dan qaqalo
"gajiya nayi da kwanciyar sai na zauna na dan huta"
"Ko dai wani abu ke damunki?,ki gayan gaskiya" kai ta kada kanta a qasa
"A'ah ummi babu komai,kawai na gaji da kwanciya ne"
"To ko dakina zaki koma?" Ta fadi tana qarasowa gabanta
"Nan din ma yayi fa ummi"
"Indai akwai wani abu da bai miki dai dai da yadda kikeso kada kiyi nauyin baki ki sanar min......mijinki ne dama ya tasoni....maimakon ya kira taki wayar" ta fada tana dan murmushi tare da miqa mata wayar sannan ta juya zata fice
"Idan kin gama ki barta nan wajenki ko zuwa safiya na karba" ta fada tana ficewa tare da rufe mata qofar,wayar sumayya tabi da kallo sanda ta sake ruru,sunanshi ya fito baro baro,sai ta kauda kai kibiyar kishi na sukarta,wani kiran ne ya sake shigowa,a hankali ta shafa wajen amsawa ta daga ta kara a kunnenta
"Sumayyah!" Ya fada a tausashe cikin salon muryarshi dake ratsa zuciyarta,muryar nan da take mutuwar so,
"Sai yau kaga daman nemana?,ba ruwanka da hakin da nake ciki ko?,dama ba sona kake ba baka damu da ni ba...."
"Sumayyah" ya sake kiran sunanta karo na biyu ya katse ta a tausashe,kiran sunanta kadai ya karya mata zuciya kawai sai ta saki kukamai hade da sheshsheqa,idanunsa ya lumshe bugun zuciyarsa na qaruwa
"Ya salam!" Ya dinga furtawa can qasa tana shiga cikin kunnenta,ita kanta batasan me ya saka ta kukan ba,daga inda yake tsayen sai tsaiwar ta gagareshi,komawa yayi saman kujerar shima yayi kwance rigingine,wani dafi take zubawa zuciyarshi ba tare da ta sani ba,nadama ta kamashi,me yasa ya watsar da ita don kawai taqi binshi,shi kansa yasan cewa kansa da kansa ya hora,yama fita jigata,sabida shi din ya rasa komai,duk wani abu data sabar masa da shi a yanzu babu,sannu a hankali ta soma tsagaita kukan don kanta,bayan taji zuciyarta ya soma yin sanyi
"Kiyi haquri" ya fada kamar yana mata rada
"Ki yafemin.....na kasa sabawa ne.....na kasa daurewa rashinki....kamar maraya haka nake jina....am really sorry banyi da niyya ba" ajiyar zuciyar itama ta sauke,tana jin yadda kewarshi ke illatata,kalamanshi kamar sake tunzura qaunarsa suke cikin zuciyarta,saidai sarautar ta motsa,sai tayi mishi shuru kaman bada ita yake ba
"Summy....kice wani abu mana" yadda ya kira sunan nata sai taji kaman mukhtar,sake narkewa tayi cikin kujera ta kuma qi cewa komai din
"Samayyahh...." Ya kuma kiran sunanta,ya gane cewa kawai azabtar da shi take sonyi,kamar ya saki mata kuka haka yake ji
"Ki kulani ko don babynmu mana,i missed him alort shima fa" nan ba amsa,amma can qasan ranta wani sanyi na ratsata,wanda yayi tasiri har saman fuskarta,ta soma fidda wani boyayyen murmushi
"Wallahi tallahi na rantse idan baki ce min komai ba a gobe zaki ganni abuja" dariyar da take boyeea ta qwace mata,zata fi kowa son hakan,saidai bata masa adalci ba idan har tasa daga komawarsa cikin sati guda ya kashe kudin ticket dinshi ya sake dawowa,me zata cewa su ummi ya kawoshi
"My happiness...." Ta amsa mishi cikin wani irin salo wanda ya saukar da gungun farinciki wa zuciyarshi,ya sauke qatuwar ajiyar zuciya
"Ki tabbatar min da cewa kina lafiya keda baby na"a shagwabe tace
"ba wani.....bayan baka damu dani ni da babyn ba...."
"Ya ilahi....daina fada don Allah kada ki sani cikin wani hali.....ki fadi abunda zai miki yanzu wanda zan wanke kaina,wanda zai nuna miki tsantsar damuwar da nayi da ku"
"Just kiss me...." Ya subuce daga bakinta ba tare da tasan ta fadi hakan ba,wani wawan kiss ya bata ta cikin wayar wanda babu inda bai aika saqo ba cikin gangar jikinta da ruhinta sannan ya dora
"Ku raba ke da baby na"
"Baby yana godiya.....ka kwanta da safe mayi waya,sabida su'ad" ta hada kalaman da qyar,idanunshi ya daga ya dubi qofar bedroom din da take ciki,tunda suka zo ungulu ta koma gidanta na tsamiya,wani abun ma don yana taka mata birki ne
"Ban yarda ba" ya maidawa sumayya amsa
"Da gaske my happiness.....kaga idan ni kama haka ko bazanji dadi ba" shiru yayi yana murmushi kamar tana gabanshi,sunan data kirashi da shi ya tsaya masa
"Da gaske ni happiness dinki ne?"
"Sosai.....ban kuma sake tabbatar da hakan ba sai yanzu,na rasa farinciki da walwala na tsahon sati guda sabida batan dabo daka yiwa rayuwata,sai gashi cikin mintina qalilan da jin muryarka komai ya dawo min,farinciki na yadawo,sai tsananin kewarka da nake ji kamar zata rabani da ruhina..." Ta bashi amsa kai tsaye tare da katse kiran saboda tana ji tayi amfani da kalamai masu nauyi,mutuwar zaune kawai yayi daga wancan bangaren,kalan soyayyar da yake da buqata,kalan soyayyar da yake nema ido rufe yau gashi Allah ya bashi,baki daya ta gama kasheshi,dan qaramin ihu ya saki shi kadai kaman wanda ya soma zaucewa,gaskiya wannan karon baya jin zai iya bin umarnin su baba,ko sato matarshi sai yayi,bazai iya jurewa zama ba tare da ita ba,haka ya dinga jera kiranta amma tawi dagawa,daga bisani ta tura masa saqo tana shaida masa bacci zatayi sai da safe,wanda ita kanta bata gaji da jin muryarshi ba,tayi hakanne kawai don kada ta shiga hurumin su'ad.