Sashe 125
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai data tsaya suka gaisa da baaba mai gadi kamar yadda suka saba sannan ta sanya kanta cikin gidan,tunda ta shiga gabanta ke wani irin faduwa,kusan yara sunfi yawa a harabar gidan suna wasanninsu,jifa jifa mutane na kai kawo,juyiwar da abdallah zaiyi ya hangota,duk da niqabin dake fuskarta da hijabinta hakan bai sanya ya kasa ganeta ba,da gudu ya tafi yana kiran
"Ammiiiii....amminaaaa" cak yaran suka tsaya suna kallonshi ganin suna tsaka da wasa ya bar gun.
Da idanuwa yabi yaron ganin yayi wani guri da gudu,hannayenta ta bude baki daya duk da har yanzu niqabin na kan fuskarta amma murmushi ne kan fuskarta,durqusawa tayi ta daga shi tana nishi saboda nauyin da abdallahn ya dan yi mata sannan ta dage niqaf din,fararen jerarrun haqoranta a waje
"Wai abdallah,na kusa fara kasa dagaka,me kaci yau ka qara nauyi?" Dariya ya saki irin ta quruciya sannan yace
"Ammi,wata ummi ce,na kwana a dakinta,ta yimin wanka ta bani chips da qwai ni kadai na cinye,harda tea da suger sosai" dariya ta kamata,har sai data dora tafin hannunta kan bakinta,kafin tace wani abu hibba tayo gaba da gudu itama sauran yaran suka biyota,bata ankara ba taji an ruqunqumeta ana fadin
"Anty,kin dawo zaki mana labarin?" Waiwayowa tayi tana dariya,ta sauke abdallah tana fadin
"Kin manta yau ana bikin anty ameeraa?,sai idan an gama zan muku,muje ku rakani inda anty amiran take" gaba tayi yaran na binta a baya wannan ya riqe hannunta wannan ya riqe hijabinta a haka suka tafi.
Baisan yana binsu da kallo ba sai da suka bacewa ganinsa,ya lumshe idanunsa sannan ya bude a hankali,abun ya burgeshi ya bashi sha'awa,yana son yara har cikin zuciyarsa,bayansa ya jinginar jikin kujerar yana fidda zazzafan huci daga bakinsa
"My man" yaji an ambata a tausashe,yasan ko wace hakan ya sanya yaqi waiwayawa,sannu a hankali ta tako gabanshi,sanye take cikin riga da wando,ire iren shigar da tasan yana muradi suna burgeshi qwarai idan tayi,jikinta na fidda wani irin qamshi mai dadi,duka hannayenta ta zuba a kafadarsa,cikin shagwaba salon da tasan yafiso tace
"My man,ka sanyani a damuwa jiya,kasan cewa ina buqatar ka,baki daya kwanakin da zamu kasance tare ba masu yawa bane,amma man ka qauracemin" ko kadan bai da buqatar maganarta,hakan ya sanya ya saka hannunshi ya sauke hannayenta dake kafadarsa sannan ya ture kujerar ya miqe tsaye ta juya yana shirin barin gun,ranta ne ya baci,hankalinta ya tashi,ta tabbatar cewa ya hau bigerin da shawo kansa zaiyi wuya,bata kuma isa ta sha gabanshi don hakan zai iya jawo mata wata matsalar,tilas ta janye jiki tana kallonshi ya wuceta,hannayenta ta saki zuciyarta na zafi,idanuwanta na neman tara qwalla,babu shakka idan banda mustapha mustapha ne da babu namijin da zata zauna a duniya yayi mata haka,saidai mustaphan na dabanne kamar yadda yake daban a zuciyarta,mafita daya gareta ta kaishu gaba inda za'a sashi tilas yayi mata abinda take so din,bama inda ta saba kaishi ba wannan karon na can zata kaishi ba,sai ta juya da dan sassarfa ta ratsa ta dakinsa zuwa falonsa ta sauko qasa ta nemi hanyar ficewa ba tare data damu da sauya kaya ko daukar babban mayani ta suturta jikinta ba ko don girman wanda zata gurinsa.
A dakinsu na jiya sumayyan ta tadda su,tana qunshe dariya ta qarasa,dariya amiran ta saka tana harararta
"Wallahi kin maida ni wata iri amira,godiya nake"
"Afuwa namecy,afwa"ta qarasa ciki suna gaisawa da 'yammatan dake ciki,gira ta daga
" to ya zanyi da ke,ni na kai kaina inda ba'a damu da ni ba,muje kimin rakiya wajen baabaa"
"Ya kamata,don nima ina son inje in gaidashi" eesha dake shan tea ta ajjuye cup din tana yiwa sumayyan duban ita kuma a wa?,kamar zata furta sai kuma ta fasa,ta miqe itama tana yafa dan yalolon mayafi kan kayan baccinta tana cewa
"Muje nima nayi rakiya"
"Owk" amira ta fada ta dubi su hibba
"Oya,ku wuce ku tafi wasanku" juyawa sukayi hibba ta tsaya ta karbi abdallah suka wuce.
Sai da suka shiga wajen anty maamaa da ummee ta gaidasu sannan ta suka wuce zuwa sashen tsohon.
Zaune yake gefan umminsa daga shi sai itayana kurbar coffee,idan da kowa a gun ta tabbata bazai sha ba,wanda ta shiga kitchen da kanta ta hada masa,dubanshi take qasa qasa,ita daya take iya gane mustaphan,tayi tsammanin idan yayi aure shikenan komai ya qare,matarsa zata fahimceshi fiye da kowa,saidai kash,sabanin haka ne ya faru,matarsa itace wadda bata fahimceshi ba fiye da kowa,a yanzun kallo daya tayi masa ta fahimci yunwa yake ji,bazai iya gaya mata ba,zai iya ci gaba da zamansa haka har sai an bashi,idan ya gaji ya kuma yana iya fita can wani wajen cin abincin yaci abinshi,time to time yakan sanya matarsa tazo ta karba masa idan yunwar taci tura,hatta da amira tafi matarsa sanin ko shi waye,wani irin mutum ne shi mai wuyar sha'ani,ba kowa ke iya fahimtarsa ba,bai iya sharing damuwarsa ko shawararsa da kowa idan ka dauke ummeen da baabaansa,tayi zaton idan yayi aure wannan zai zama aikin matarsa,saidai ina ma yaga matar bare ta dauki wannan responsibility din,saidai komai tana ganin ya kusa zuwa qarshe tunda gaf su'adan take da kammala karatunta,tana zaton idan ta gama din zata nutsu ta tara hankalinta waje guda ta kula da mijinta kamar kowacce matar aure.
Yana tsaka da amsa waya ta shigo falon kai tsaye tare da sallamarta,a hankali ya daga kanshi don ganin waye,kansa ya kawai gefe yana jin kunyar ganinta a haka a matsayin surukarshi,baki daya babu al'adar bahaushe ko digi cikin jini da jijiyarta,komai nata na mai jan kunne ne,ko qanqanin bata jin kunyar keta gidan a haka,duk da tarin baqi dake gidan,yana yiwa yaronshi sha'awar sauyin rayuwa,duk abinda ke faruwa cikin rayuwar yaron shi da yakeso fiye da kowa cikin yaransa idan ka dauke amira yana sane,saidai baison jefa kanahi cikin sha'anin da ba'a nemi agaji ko tallafinsa,dattijon suruki ne wanda yasan ciwon kanshi da mutucinsa,amma tabbas mustapha ma cikin wani wadi daya cancanci a tallafeshi,tun fari laifinshi ne da bai ganin aibun rayuwar mai jan kunne,gani yake rayuwa ce ta burgewa,baisan babu komai cikinta face tsantsar wahala da rashin nutsuwa.
Cikin sheshsheqar kuka ta zube a gabansa
"Baabaa don Allah kayi masa fada,ka masa magana,yana son takurani,yana son tauyen 'yancina" sosai yake dubanta,a nutse yace
"Nutsu su'adah,zauna,zauna sosai,gayamin,me ya faru?,me ya hadaku" zama tayi gabansa tana goge hawayen nata da tissue,don ko dan mayafin da zata kama ta goge hawayen babu a jikinta
"Baabaa,mustapha ne,haka kawai muna zamanmu yadda muka saba,shekaran jiya yaje gidan hamza,ya gano wata zamantakewa ta daban yace dole muma irinta zamuyi,bayan zamantakewar tasu sam babu 'yanci ko walwala a cikinta,sai dinbim takura kai da rayuwa cikin duhu da rashin wayewa,lallai wai saidai na dawo nan qasar na zauna daku na qarasa karatuna don bai amince da duk qawaye na da abokaina ba,sannan wai idan na kammala na bishi dubai mu zauna tare na dinga kula da shi,don Allah baaba wannan ba takura bace,ni ban taba ganin inda da quruciyarki kike rayuwa irin haka ba,a gun africans kawai nake gani suma rashin wayewa ce da duhun kai" idanu baban ya runtse kafin ya bude,duka ta hadu ta zagesu su da iyayensy,babu shakka ba qaramin tasiri rayuwar yaro take ba a duk inda aka haifeshi ko ya taso,sai Allah ya taimaka iyaye sunyi tsaiwar daka sannan za'a samu yaro ya tashi da dabi'a halayya da al'adunshi.
Cup din ya dire dai dai sanda wayarshi tayi tsuwwa,ya duba yaga kiran daga baabaa ne,tun kafin ya daga ranshi ya raya masa mishkilar su'adah ce,daya daga din kuwa ce masa baabaan yayi
"Kana ina?,duk inda kake kazo ka sameni a falo,ina jiranka" daga maganar tasa kawai ya fahimci mawuyaci ne ba qararsa ta kai wajen baabaan ba,duk da cewa hakan ba baqon lamari bane wajensa,amma abun yayi masa ciwo fiye da kullum,ranshi bace ya maida wayar aljihunsa yana duban ummee
"Baabaa na kira" ya fadi a taqaice
"Ok,ka qoshi kenan coffee kawai ya isheka,bayanshi banga kaci komai ba?"
"I'm ok ummee" ya fadi yana takawa ya fice daga dakin.
Cikin sanyi da qasaita yayi sallama cikin falon baaban,wani kallo yajefa mata wanda ya sanyata sadda kanta qasa,take jikinta yayi sanyi,nadamar kawo qarar ta baibayeta,kwarjininsa kadai ya ladabtar da ita,cikin girmamawa ya isa gaban baaban ya zauna gami da lanqwashe qafafunsa,ajjiye takaddun hannayensa yayi sannan ya maida hankalinsa gareshi
"Mustapha,me ya shiga tsakaninka da matarka" shiru yayi na wasu daqiqu kanshi na qasa,idanunshi bisa carfet din dake dakin,a hankali ya motsa bakinsa
"Baabaa,ina da buqatar mata ta ne kawai kusa dani,na buqaci ta ajjiye karatunta ta zauna tare da ni" yasan a rina,mustaphan ba mai boyon abu bane cikin zuciya,komai tsaurin gaskiya ko dacinta sai ya fadeta,tabbas mustaphan bashi da laifi cikin maganarlaifinshi daya tun fari a haka ya tarbiyyanci matarsa,amma kowanne magidanci zaiso kasancewa da iyalinshi,bawai kowannansu da inda ya sanya kanshi ba sannan ace wai a haka za'a rayu,tausayinshi ya kama shi,yana jin wannan karon ya kamata yayi wani hobbasa cikin rayuwar yaron nashi
"Baka kyauta ba mustapha" maganar data sanyashi daga ido cikin mamaki ya tsare babaa da kallo,yayi zaton shine na farko da zai goya masa baya?,ya zaci shima yasan ba haka rayuwar ma'aurata take ba
"Tun farko haka ka dora bigiren rayuwarku kai da ita,ka manta ice tun yana danye ake tanqwarashi,basai ya bushe ba sannan kace zaka tanqwarashi" kai su'adah ke kadawa cike da jin dadi tare da alamun samun nasara cikin zancan baban ba tare data fuskanci dungun dake cikin maganar ba
"Mustapha,komai ya kusa qarewa,ka qyale matarka ta kammala karatunta a inda ta fara,shekara guda ya rage mata ta kammala,idan yaso koma meyw zai biyi baya sai ka zauna ku yanke" shiru ne ya ratsa falon,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi,zuciyar su'adah ciki fal da fatan samun nasara.
Bayajin a duniya akwai wani umarni da baban zai bashi ya tsallakeshi,ya numfasa a hankali sannan ya furta
"Na barta baabaa"
"Yes dad,thank you" sa'adah ta fada cikin daga murya,murmushi ya subucewa baabaan,addu'a yaje da fatan saisaituwar halayen su'adah ko kyakkyawar rayuwa zata samu ga diyansa,miqewa tayi cikin farinciki ta fice,fes taje jin ranta,don ta mustapha tana tunanin tasan yadda zata shawo kansa,don ko kadan bata jin zata iya tabbata cikin nijeria tayi rayuwa a cikinta.
"Ammiiiii....amminaaaa" cak yaran suka tsaya suna kallonshi ganin suna tsaka da wasa ya bar gun.
Da idanuwa yabi yaron ganin yayi wani guri da gudu,hannayenta ta bude baki daya duk da har yanzu niqabin na kan fuskarta amma murmushi ne kan fuskarta,durqusawa tayi ta daga shi tana nishi saboda nauyin da abdallahn ya dan yi mata sannan ta dage niqaf din,fararen jerarrun haqoranta a waje
"Wai abdallah,na kusa fara kasa dagaka,me kaci yau ka qara nauyi?" Dariya ya saki irin ta quruciya sannan yace
"Ammi,wata ummi ce,na kwana a dakinta,ta yimin wanka ta bani chips da qwai ni kadai na cinye,harda tea da suger sosai" dariya ta kamata,har sai data dora tafin hannunta kan bakinta,kafin tace wani abu hibba tayo gaba da gudu itama sauran yaran suka biyota,bata ankara ba taji an ruqunqumeta ana fadin
"Anty,kin dawo zaki mana labarin?" Waiwayowa tayi tana dariya,ta sauke abdallah tana fadin
"Kin manta yau ana bikin anty ameeraa?,sai idan an gama zan muku,muje ku rakani inda anty amiran take" gaba tayi yaran na binta a baya wannan ya riqe hannunta wannan ya riqe hijabinta a haka suka tafi.
Baisan yana binsu da kallo ba sai da suka bacewa ganinsa,ya lumshe idanunsa sannan ya bude a hankali,abun ya burgeshi ya bashi sha'awa,yana son yara har cikin zuciyarsa,bayansa ya jinginar jikin kujerar yana fidda zazzafan huci daga bakinsa
"My man" yaji an ambata a tausashe,yasan ko wace hakan ya sanya yaqi waiwayawa,sannu a hankali ta tako gabanshi,sanye take cikin riga da wando,ire iren shigar da tasan yana muradi suna burgeshi qwarai idan tayi,jikinta na fidda wani irin qamshi mai dadi,duka hannayenta ta zuba a kafadarsa,cikin shagwaba salon da tasan yafiso tace
"My man,ka sanyani a damuwa jiya,kasan cewa ina buqatar ka,baki daya kwanakin da zamu kasance tare ba masu yawa bane,amma man ka qauracemin" ko kadan bai da buqatar maganarta,hakan ya sanya ya saka hannunshi ya sauke hannayenta dake kafadarsa sannan ya ture kujerar ya miqe tsaye ta juya yana shirin barin gun,ranta ne ya baci,hankalinta ya tashi,ta tabbatar cewa ya hau bigerin da shawo kansa zaiyi wuya,bata kuma isa ta sha gabanshi don hakan zai iya jawo mata wata matsalar,tilas ta janye jiki tana kallonshi ya wuceta,hannayenta ta saki zuciyarta na zafi,idanuwanta na neman tara qwalla,babu shakka idan banda mustapha mustapha ne da babu namijin da zata zauna a duniya yayi mata haka,saidai mustaphan na dabanne kamar yadda yake daban a zuciyarta,mafita daya gareta ta kaishu gaba inda za'a sashi tilas yayi mata abinda take so din,bama inda ta saba kaishi ba wannan karon na can zata kaishi ba,sai ta juya da dan sassarfa ta ratsa ta dakinsa zuwa falonsa ta sauko qasa ta nemi hanyar ficewa ba tare data damu da sauya kaya ko daukar babban mayani ta suturta jikinta ba ko don girman wanda zata gurinsa.
A dakinsu na jiya sumayyan ta tadda su,tana qunshe dariya ta qarasa,dariya amiran ta saka tana harararta
"Wallahi kin maida ni wata iri amira,godiya nake"
"Afuwa namecy,afwa"ta qarasa ciki suna gaisawa da 'yammatan dake ciki,gira ta daga
" to ya zanyi da ke,ni na kai kaina inda ba'a damu da ni ba,muje kimin rakiya wajen baabaa"
"Ya kamata,don nima ina son inje in gaidashi" eesha dake shan tea ta ajjuye cup din tana yiwa sumayyan duban ita kuma a wa?,kamar zata furta sai kuma ta fasa,ta miqe itama tana yafa dan yalolon mayafi kan kayan baccinta tana cewa
"Muje nima nayi rakiya"
"Owk" amira ta fada ta dubi su hibba
"Oya,ku wuce ku tafi wasanku" juyawa sukayi hibba ta tsaya ta karbi abdallah suka wuce.
Sai da suka shiga wajen anty maamaa da ummee ta gaidasu sannan ta suka wuce zuwa sashen tsohon.
Zaune yake gefan umminsa daga shi sai itayana kurbar coffee,idan da kowa a gun ta tabbata bazai sha ba,wanda ta shiga kitchen da kanta ta hada masa,dubanshi take qasa qasa,ita daya take iya gane mustaphan,tayi tsammanin idan yayi aure shikenan komai ya qare,matarsa zata fahimceshi fiye da kowa,saidai kash,sabanin haka ne ya faru,matarsa itace wadda bata fahimceshi ba fiye da kowa,a yanzun kallo daya tayi masa ta fahimci yunwa yake ji,bazai iya gaya mata ba,zai iya ci gaba da zamansa haka har sai an bashi,idan ya gaji ya kuma yana iya fita can wani wajen cin abincin yaci abinshi,time to time yakan sanya matarsa tazo ta karba masa idan yunwar taci tura,hatta da amira tafi matarsa sanin ko shi waye,wani irin mutum ne shi mai wuyar sha'ani,ba kowa ke iya fahimtarsa ba,bai iya sharing damuwarsa ko shawararsa da kowa idan ka dauke ummeen da baabaansa,tayi zaton idan yayi aure wannan zai zama aikin matarsa,saidai ina ma yaga matar bare ta dauki wannan responsibility din,saidai komai tana ganin ya kusa zuwa qarshe tunda gaf su'adan take da kammala karatunta,tana zaton idan ta gama din zata nutsu ta tara hankalinta waje guda ta kula da mijinta kamar kowacce matar aure.
Yana tsaka da amsa waya ta shigo falon kai tsaye tare da sallamarta,a hankali ya daga kanshi don ganin waye,kansa ya kawai gefe yana jin kunyar ganinta a haka a matsayin surukarshi,baki daya babu al'adar bahaushe ko digi cikin jini da jijiyarta,komai nata na mai jan kunne ne,ko qanqanin bata jin kunyar keta gidan a haka,duk da tarin baqi dake gidan,yana yiwa yaronshi sha'awar sauyin rayuwa,duk abinda ke faruwa cikin rayuwar yaron shi da yakeso fiye da kowa cikin yaransa idan ka dauke amira yana sane,saidai baison jefa kanahi cikin sha'anin da ba'a nemi agaji ko tallafinsa,dattijon suruki ne wanda yasan ciwon kanshi da mutucinsa,amma tabbas mustapha ma cikin wani wadi daya cancanci a tallafeshi,tun fari laifinshi ne da bai ganin aibun rayuwar mai jan kunne,gani yake rayuwa ce ta burgewa,baisan babu komai cikinta face tsantsar wahala da rashin nutsuwa.
Cikin sheshsheqar kuka ta zube a gabansa
"Baabaa don Allah kayi masa fada,ka masa magana,yana son takurani,yana son tauyen 'yancina" sosai yake dubanta,a nutse yace
"Nutsu su'adah,zauna,zauna sosai,gayamin,me ya faru?,me ya hadaku" zama tayi gabansa tana goge hawayen nata da tissue,don ko dan mayafin da zata kama ta goge hawayen babu a jikinta
"Baabaa,mustapha ne,haka kawai muna zamanmu yadda muka saba,shekaran jiya yaje gidan hamza,ya gano wata zamantakewa ta daban yace dole muma irinta zamuyi,bayan zamantakewar tasu sam babu 'yanci ko walwala a cikinta,sai dinbim takura kai da rayuwa cikin duhu da rashin wayewa,lallai wai saidai na dawo nan qasar na zauna daku na qarasa karatuna don bai amince da duk qawaye na da abokaina ba,sannan wai idan na kammala na bishi dubai mu zauna tare na dinga kula da shi,don Allah baaba wannan ba takura bace,ni ban taba ganin inda da quruciyarki kike rayuwa irin haka ba,a gun africans kawai nake gani suma rashin wayewa ce da duhun kai" idanu baban ya runtse kafin ya bude,duka ta hadu ta zagesu su da iyayensy,babu shakka ba qaramin tasiri rayuwar yaro take ba a duk inda aka haifeshi ko ya taso,sai Allah ya taimaka iyaye sunyi tsaiwar daka sannan za'a samu yaro ya tashi da dabi'a halayya da al'adunshi.
Cup din ya dire dai dai sanda wayarshi tayi tsuwwa,ya duba yaga kiran daga baabaa ne,tun kafin ya daga ranshi ya raya masa mishkilar su'adah ce,daya daga din kuwa ce masa baabaan yayi
"Kana ina?,duk inda kake kazo ka sameni a falo,ina jiranka" daga maganar tasa kawai ya fahimci mawuyaci ne ba qararsa ta kai wajen baabaan ba,duk da cewa hakan ba baqon lamari bane wajensa,amma abun yayi masa ciwo fiye da kullum,ranshi bace ya maida wayar aljihunsa yana duban ummee
"Baabaa na kira" ya fadi a taqaice
"Ok,ka qoshi kenan coffee kawai ya isheka,bayanshi banga kaci komai ba?"
"I'm ok ummee" ya fadi yana takawa ya fice daga dakin.
Cikin sanyi da qasaita yayi sallama cikin falon baaban,wani kallo yajefa mata wanda ya sanyata sadda kanta qasa,take jikinta yayi sanyi,nadamar kawo qarar ta baibayeta,kwarjininsa kadai ya ladabtar da ita,cikin girmamawa ya isa gaban baaban ya zauna gami da lanqwashe qafafunsa,ajjiye takaddun hannayensa yayi sannan ya maida hankalinsa gareshi
"Mustapha,me ya shiga tsakaninka da matarka" shiru yayi na wasu daqiqu kanshi na qasa,idanunshi bisa carfet din dake dakin,a hankali ya motsa bakinsa
"Baabaa,ina da buqatar mata ta ne kawai kusa dani,na buqaci ta ajjiye karatunta ta zauna tare da ni" yasan a rina,mustaphan ba mai boyon abu bane cikin zuciya,komai tsaurin gaskiya ko dacinta sai ya fadeta,tabbas mustaphan bashi da laifi cikin maganarlaifinshi daya tun fari a haka ya tarbiyyanci matarsa,amma kowanne magidanci zaiso kasancewa da iyalinshi,bawai kowannansu da inda ya sanya kanshi ba sannan ace wai a haka za'a rayu,tausayinshi ya kama shi,yana jin wannan karon ya kamata yayi wani hobbasa cikin rayuwar yaron nashi
"Baka kyauta ba mustapha" maganar data sanyashi daga ido cikin mamaki ya tsare babaa da kallo,yayi zaton shine na farko da zai goya masa baya?,ya zaci shima yasan ba haka rayuwar ma'aurata take ba
"Tun farko haka ka dora bigiren rayuwarku kai da ita,ka manta ice tun yana danye ake tanqwarashi,basai ya bushe ba sannan kace zaka tanqwarashi" kai su'adah ke kadawa cike da jin dadi tare da alamun samun nasara cikin zancan baban ba tare data fuskanci dungun dake cikin maganar ba
"Mustapha,komai ya kusa qarewa,ka qyale matarka ta kammala karatunta a inda ta fara,shekara guda ya rage mata ta kammala,idan yaso koma meyw zai biyi baya sai ka zauna ku yanke" shiru ne ya ratsa falon,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi,zuciyar su'adah ciki fal da fatan samun nasara.
Bayajin a duniya akwai wani umarni da baban zai bashi ya tsallakeshi,ya numfasa a hankali sannan ya furta
"Na barta baabaa"
"Yes dad,thank you" sa'adah ta fada cikin daga murya,murmushi ya subucewa baabaan,addu'a yaje da fatan saisaituwar halayen su'adah ko kyakkyawar rayuwa zata samu ga diyansa,miqewa tayi cikin farinciki ta fice,fes taje jin ranta,don ta mustapha tana tunanin tasan yadda zata shawo kansa,don ko kadan bata jin zata iya tabbata cikin nijeria tayi rayuwa a cikinta.