Sashe 50
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sau daya yaya yahansu ta taba tuntubarsa da batun bazayayi aure bane,murmushi kawai yayi mata yace tabar batun don ko sha'awar sa bayayi,tilas ta ja bakinta ta tsuke,domin har yau tana tuhumar kanta da cewa ita ce sila,zuwa yanzu itama ta fara gani,don kuwa yaron da jamila ke ao kamar ta mutu shima yayarsa ta hana auren sam tace bata yarda ba,ga fatima nan ma a gabanta babu wani bayani,fiddausi kuwa uwar miji ta sakota gaba,yau tana gidanta gobe tana gidan yaya yahanasun
*_KOMAI NISAN JIFA_*
Tunda dukka ayyukanta suka kammalu wajen malaminta data bawa hadin kai wanda har ta kaita da kwanciya da shi,ki a jikinta babu abinda taji tunda har ya mata alqawarin tabbas tamkar ta samu kukhtar ta gama koda kuwa zata sanar masa ita ta shirya duk abinda ya faru a baya da sumayya,babu abinda zai iya aikatawa ba zaiga aibunta ba face sabuwar soyayya da zata sake ballewa a tsakaninsu.
Ranar lahadi ta shirya zuwa har gida saboda ta tabbatar a ranar bai fita kasuwa,dinki na musamman tayi sabo,baya ga sabon kitso da gidan kwalliya da taje duka aka sauya halittar Allah,saboda tana rayawa matuqar ciniki ya fada tofa ba lallai bane ma ta dawo gidansu ba saidai a biyota da kayanta,tunda har yau a matsayin saki daya yayi mata haka ta sanarwa mamanta,wanda koda sakin ukun tace an mata ta kuma ce zata koma babu abinda uwar ta isa tayi don ba a bakin komai take a gunta ba.
Qarfe sha goma na safe ta kammala komai,a nan cikin shagon masu kwalliya wadda ta sanya fitowa tunda safen tayi mata ta sauya kaya,double ta biya kudin makeup din hakan ya sanya ta yiwa jakarta qarqaf,bata da damuwa tunda tana saka ran kome wanda zata fanshe dukkan abinda ta kashe gun mukhtar,ba shakka sai ta rama wahalar da ya bata ba zata sassauta masa ba.
Qarfe goma sha daya saura mintuna goma ta sauka qofar gidan mukhtar din,wani farinciki ya lullubeta ta soma shaqar iskar komawa cikin gidan,cikin sa'a tana tura qofar gidan ta taddata a bude,a hankali take takawa saboda cogen dake qafarta har ta sada kanta da falon gidan,a hankali take qarewa falon kallo yadda ya sake maidashi ya gyarashi bayan barinsu gidan,sai abun ya sake burgeta,ko ina tsaf kamar akwai mace a ciki kasancewar yana da mai share share da goge goge,cikin kallon da takeyi ne idanuwanta ya saukan kan abdallah dake zaune tsakiyar falon,sanye yake da jallabiya fara tas ta yara wadda ta masa kyau kamar dan larabawa,wasansa yake da kayan wasa turmus a gabansa nau'i daban daban.
Idanuwa ta zuba masa kamar yadda shima ya zuba mata idanuwa yana kallonta tamkar ya santa,karkata kai take tana gano kamannin mutum biyu tattare da shi,sumayya sumayya mukhtar mukhtar,ci gaba tayi da kallon nasa tana son tantance dan waye?,miqewa yaron yayi yana ci gaba da kallonta sai kuma ya saki kuka tare da juyawa a guje ya shige bangaren baban nasa wanda ke ciki.
*mrs muhammad ce*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣2⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wala tahsabannal lazina qutilu fi sabilillahi amwaataa,bal ahya'u inda rabbihim yurzaqun*
*_kada ku zaci wadanda aka kashe ta hanyar Allah(shahidai)matattu ne,rayayyu ne a gun ubangijinsu ana azurtasu_*
_______________________________
Mukhtar dake falo zaune saman abun sallah yayi saurin sallame raka'arsa ta qarshe wadda dama zaman tahiya yake,qarasowa abdallah yayi yana kebe baki ya fada jikin mukhtar,tambayarsa yake menene kamar wani babba,babu baki sai gwalanto da yake masa wanda bai gane mai yake cewa,miqewa yayi da sauri sabe da shi a kafadarsa sabida tunawar da yayi dazu da ya fita siyo ma abdallan alawa ya manta ya bar qofar gidan a bude.
Tana zaune qafa daya kan daya tana kadasu hankalinta kwance,tana jin ba ma sai taje nemansa ba da kanshi zai fito,qamshin turarensa da ta ji shi ya maida hankalinta zuwa qofarsa,shi dinne dauke da abdallah sanye da jallabiya sak irin ta abdallan,har ga Allah bai lura da ita ba sai da yaji an ambaci
"Ranka ya dade" cak ya tsaya sannan ya waiwayo ya dubeta,idanunta ya dan juya don tabbatar da cewar ita din ce?,ita ce don kuwa zuwa yanzu gabansa take takowa,dab da shi ta qaraso tamkar zata shige jikinsa,cikin narke murya ta soma magana
"Haba my mukhtar,ka riga da kasan irin kamun da soyayyarka tawa zuciyata,ta yaya kake tunanin nisanta kanka da ni bayan kasan cewa ina mutuwar sonka,a yau ina so ka maidani dakina ba sai gobe ba domin shine burina kaji" ta qarashe maganar ta sigar bada umarni.
Wani bala'i ke cinsa,ya tabbata cewa idan har baiwa zainab akuyanci ba ba zata taba barin rayuwarsa ba,yarinyar da kullum kwanan duniya ya zauna tunani yake tare da tambayar yaya akayi ya aureta ma wai?,mene ya ja hankalinsa,ko da yaushe yakan godewa Allah da bai QADDARA rabon zuria a tsakaninsu ba.
Cikin tsantsar bacin rai ya soma nuna ta da yatsa kamar zai tsone mata idanuwa
"Cikin halittun dabbobi ke wacce iriya ce a cikinsu?,bakiji gargadin da na miki ba kenan?,tunda nake ban taba ganin ballagazar mace irinki ba,sha sha sha kawai wawiya,to wallahi zan miki gargadi na qarshe,duk sanda kika sake shiga rayuwata sai na miki abinda ko hanyar da nake bi aka ce kibi ba zaki biba,bace min da gani banza qazama kawai" ya fada kamar zai hankadata.
Tsantsar tashin hankali da baqinciki suka taso suka tokareta,amma data tuna yadda bokanta ya jaddada mata kyawun aikin da yayi mata sai taga bari ta sake gwada sa'arta
"Wai mukhtar me na maka da zafi haka,nina shiryawa sumayya dukkan wata gadar zare kuma a idanunka sumayya ce ta aikata laifin,to amma na lura tsanar da ka yimin baka yi mata koda rabinta ba" sosai maganar ta daki kunnensa gangar jiki da zuciyarsa duka lokaci daya,wani abu yaji yana zagaya kansa,wani irin sanyi jikinsa yayi ya zubawa zainab ido har baisan sanda yace
"Kika shirya mata gadar zare kamar yaya?" Wani fari tayi da idanuwa tana ci gaba da kallonsa,a tunaninta sanyin da jikinsa yayi aikinsu ya fara shiga jikinsa ne,sai ta kama hannunsa babu musu ya bita zungui zungui,don baya gane komai a yanzu,abinda ke yawo kansa kawai shine irin abubuwan da suka dinga faruwa tsakaninsa da sumayya a lokacin,sai da ta kaishi gefan kujera ta zaunar sannan ta zauna gefansa.
A hankali ta dinga warware masa zare da abawa tamkar wadda ake umarta,ko da yake umarni ne na rabbil izzati da yaso ya fidda bayinsa daga wani mummunan sharri,ta qare da cewa
"Dukkan wannan saboda tsananin qaunarka da kishinka da nakeyi ne ya janyo na aikata hakan,kuma babu abinda bazan iya aikatawa duk don saboda kai saboda na mallakeka ni kadai,a shirye nake na sadaukar da dukkan abinda na mallaka" ta fadi tana karya wuya tare da sakin murmushin alamun samun nasara a tunaninta.
Gaba daya daina zagayawa jini yayi a jikinsa,kansa ya masa nauyi,cak qwaqwalwarsa ta tsaya da aiki,wani duba yakewa zainab din mai cike da tsantsar tsana,daki daki musgunawa da zargi da kallon tsana da ya dinga yiwa sumayya ya dinga dawo masa kamar bitar karatu,yanzu duk baki daya ba bisa laifinta bane ashe?,ashe ita din bata aikata komai ba kamar yadda tasha sanar masa?,bai taba jin ya tsani wata halitta a duniya ba kamar yadda yake jin tsanar zainab na yawo cikin jininsa da ruhinsa ba,sai da wuta ta dauke masa na wasu mintuna kafin ya fara tunaninsa ya fara dawowa kan hanya.
Yana jin yau idan bai ci uban zainab a duniya ba yayi asarar rayuwarsa,baisan wanne ne hukunci na qarshe da ya cancanci yayi mata ba,miqewa yayi da hanzari ta ruqo hannunsa
"Ina zaka?" Wani kallo ya juya ya watsa mata wanda ya sata sanqamewa,fargaba ta lullubeta tana fatan ba abinda take tunani bane ke shirin aukuwa
"Gidan uwarki da ubanki zani,zauna ki jirani" ya fada a tsawace yana tsige hannunsa daga nata,wani malolon takaici ya cika zuciyarta,kada dai ace mukhtar din na cikin saitinsa tayi wannan barin zancen?,yana nufin aikinta baiyi tasiri a kansa ba?,waishin wani irin mutum ne mukhtar din?,yana nufin dukka kashe kudi bata lokaci da sadaukar da jikinta da tayi ya tashi a banza?,to wallahi wannan karo kam bai isa ba,bai isa ya sanyata ci gaba da yin asara ba,kota hanyar tsiya kota arziqi,tsaye ta miqe a zafafe tana dubansa
"Kai mukhtar,na gaji,na gaji da asarar lokacina da kudina a kanka,me yasa bakasan darajar soyayya ba?"
Dauketa yayi da wani zazzafan mari wanda ya haddasa mata ganin wulgawar wasu taurari tare da zubewa warwas a qasa,lokaci guda jini yayi kwance gefan qwayar idanuwanta,kafin ta kai ga dawowa hayyacinta tuni ya garqame qofar falon sannan ya wuce ciki cikin matsanancin sauri,bedroom dinsa ya shiga ya kwantar da abdallah da bacci ya daukeshi kan fadar mukhtar din sannan ya fito ya rufe qofar dakin baccin ya rufe ta falo baki daya don bai fatan yaji ko yaga abinda yake shirin aikatawa,wani irin suya qirjinsa yake a fuskarsa yana jin wani hucin zafi na fita kamar wanda aka cilla cikin rumbun gasa biredi.
*_KOMAI NISAN JIFA_*
Tunda dukka ayyukanta suka kammalu wajen malaminta data bawa hadin kai wanda har ta kaita da kwanciya da shi,ki a jikinta babu abinda taji tunda har ya mata alqawarin tabbas tamkar ta samu kukhtar ta gama koda kuwa zata sanar masa ita ta shirya duk abinda ya faru a baya da sumayya,babu abinda zai iya aikatawa ba zaiga aibunta ba face sabuwar soyayya da zata sake ballewa a tsakaninsu.
Ranar lahadi ta shirya zuwa har gida saboda ta tabbatar a ranar bai fita kasuwa,dinki na musamman tayi sabo,baya ga sabon kitso da gidan kwalliya da taje duka aka sauya halittar Allah,saboda tana rayawa matuqar ciniki ya fada tofa ba lallai bane ma ta dawo gidansu ba saidai a biyota da kayanta,tunda har yau a matsayin saki daya yayi mata haka ta sanarwa mamanta,wanda koda sakin ukun tace an mata ta kuma ce zata koma babu abinda uwar ta isa tayi don ba a bakin komai take a gunta ba.
Qarfe sha goma na safe ta kammala komai,a nan cikin shagon masu kwalliya wadda ta sanya fitowa tunda safen tayi mata ta sauya kaya,double ta biya kudin makeup din hakan ya sanya ta yiwa jakarta qarqaf,bata da damuwa tunda tana saka ran kome wanda zata fanshe dukkan abinda ta kashe gun mukhtar,ba shakka sai ta rama wahalar da ya bata ba zata sassauta masa ba.
Qarfe goma sha daya saura mintuna goma ta sauka qofar gidan mukhtar din,wani farinciki ya lullubeta ta soma shaqar iskar komawa cikin gidan,cikin sa'a tana tura qofar gidan ta taddata a bude,a hankali take takawa saboda cogen dake qafarta har ta sada kanta da falon gidan,a hankali take qarewa falon kallo yadda ya sake maidashi ya gyarashi bayan barinsu gidan,sai abun ya sake burgeta,ko ina tsaf kamar akwai mace a ciki kasancewar yana da mai share share da goge goge,cikin kallon da takeyi ne idanuwanta ya saukan kan abdallah dake zaune tsakiyar falon,sanye yake da jallabiya fara tas ta yara wadda ta masa kyau kamar dan larabawa,wasansa yake da kayan wasa turmus a gabansa nau'i daban daban.
Idanuwa ta zuba masa kamar yadda shima ya zuba mata idanuwa yana kallonta tamkar ya santa,karkata kai take tana gano kamannin mutum biyu tattare da shi,sumayya sumayya mukhtar mukhtar,ci gaba tayi da kallon nasa tana son tantance dan waye?,miqewa yaron yayi yana ci gaba da kallonta sai kuma ya saki kuka tare da juyawa a guje ya shige bangaren baban nasa wanda ke ciki.
*mrs muhammad ce*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣2⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wala tahsabannal lazina qutilu fi sabilillahi amwaataa,bal ahya'u inda rabbihim yurzaqun*
*_kada ku zaci wadanda aka kashe ta hanyar Allah(shahidai)matattu ne,rayayyu ne a gun ubangijinsu ana azurtasu_*
_______________________________
Mukhtar dake falo zaune saman abun sallah yayi saurin sallame raka'arsa ta qarshe wadda dama zaman tahiya yake,qarasowa abdallah yayi yana kebe baki ya fada jikin mukhtar,tambayarsa yake menene kamar wani babba,babu baki sai gwalanto da yake masa wanda bai gane mai yake cewa,miqewa yayi da sauri sabe da shi a kafadarsa sabida tunawar da yayi dazu da ya fita siyo ma abdallan alawa ya manta ya bar qofar gidan a bude.
Tana zaune qafa daya kan daya tana kadasu hankalinta kwance,tana jin ba ma sai taje nemansa ba da kanshi zai fito,qamshin turarensa da ta ji shi ya maida hankalinta zuwa qofarsa,shi dinne dauke da abdallah sanye da jallabiya sak irin ta abdallan,har ga Allah bai lura da ita ba sai da yaji an ambaci
"Ranka ya dade" cak ya tsaya sannan ya waiwayo ya dubeta,idanunta ya dan juya don tabbatar da cewar ita din ce?,ita ce don kuwa zuwa yanzu gabansa take takowa,dab da shi ta qaraso tamkar zata shige jikinsa,cikin narke murya ta soma magana
"Haba my mukhtar,ka riga da kasan irin kamun da soyayyarka tawa zuciyata,ta yaya kake tunanin nisanta kanka da ni bayan kasan cewa ina mutuwar sonka,a yau ina so ka maidani dakina ba sai gobe ba domin shine burina kaji" ta qarashe maganar ta sigar bada umarni.
Wani bala'i ke cinsa,ya tabbata cewa idan har baiwa zainab akuyanci ba ba zata taba barin rayuwarsa ba,yarinyar da kullum kwanan duniya ya zauna tunani yake tare da tambayar yaya akayi ya aureta ma wai?,mene ya ja hankalinsa,ko da yaushe yakan godewa Allah da bai QADDARA rabon zuria a tsakaninsu ba.
Cikin tsantsar bacin rai ya soma nuna ta da yatsa kamar zai tsone mata idanuwa
"Cikin halittun dabbobi ke wacce iriya ce a cikinsu?,bakiji gargadin da na miki ba kenan?,tunda nake ban taba ganin ballagazar mace irinki ba,sha sha sha kawai wawiya,to wallahi zan miki gargadi na qarshe,duk sanda kika sake shiga rayuwata sai na miki abinda ko hanyar da nake bi aka ce kibi ba zaki biba,bace min da gani banza qazama kawai" ya fada kamar zai hankadata.
Tsantsar tashin hankali da baqinciki suka taso suka tokareta,amma data tuna yadda bokanta ya jaddada mata kyawun aikin da yayi mata sai taga bari ta sake gwada sa'arta
"Wai mukhtar me na maka da zafi haka,nina shiryawa sumayya dukkan wata gadar zare kuma a idanunka sumayya ce ta aikata laifin,to amma na lura tsanar da ka yimin baka yi mata koda rabinta ba" sosai maganar ta daki kunnensa gangar jiki da zuciyarsa duka lokaci daya,wani abu yaji yana zagaya kansa,wani irin sanyi jikinsa yayi ya zubawa zainab ido har baisan sanda yace
"Kika shirya mata gadar zare kamar yaya?" Wani fari tayi da idanuwa tana ci gaba da kallonsa,a tunaninta sanyin da jikinsa yayi aikinsu ya fara shiga jikinsa ne,sai ta kama hannunsa babu musu ya bita zungui zungui,don baya gane komai a yanzu,abinda ke yawo kansa kawai shine irin abubuwan da suka dinga faruwa tsakaninsa da sumayya a lokacin,sai da ta kaishi gefan kujera ta zaunar sannan ta zauna gefansa.
A hankali ta dinga warware masa zare da abawa tamkar wadda ake umarta,ko da yake umarni ne na rabbil izzati da yaso ya fidda bayinsa daga wani mummunan sharri,ta qare da cewa
"Dukkan wannan saboda tsananin qaunarka da kishinka da nakeyi ne ya janyo na aikata hakan,kuma babu abinda bazan iya aikatawa duk don saboda kai saboda na mallakeka ni kadai,a shirye nake na sadaukar da dukkan abinda na mallaka" ta fadi tana karya wuya tare da sakin murmushin alamun samun nasara a tunaninta.
Gaba daya daina zagayawa jini yayi a jikinsa,kansa ya masa nauyi,cak qwaqwalwarsa ta tsaya da aiki,wani duba yakewa zainab din mai cike da tsantsar tsana,daki daki musgunawa da zargi da kallon tsana da ya dinga yiwa sumayya ya dinga dawo masa kamar bitar karatu,yanzu duk baki daya ba bisa laifinta bane ashe?,ashe ita din bata aikata komai ba kamar yadda tasha sanar masa?,bai taba jin ya tsani wata halitta a duniya ba kamar yadda yake jin tsanar zainab na yawo cikin jininsa da ruhinsa ba,sai da wuta ta dauke masa na wasu mintuna kafin ya fara tunaninsa ya fara dawowa kan hanya.
Yana jin yau idan bai ci uban zainab a duniya ba yayi asarar rayuwarsa,baisan wanne ne hukunci na qarshe da ya cancanci yayi mata ba,miqewa yayi da hanzari ta ruqo hannunsa
"Ina zaka?" Wani kallo ya juya ya watsa mata wanda ya sata sanqamewa,fargaba ta lullubeta tana fatan ba abinda take tunani bane ke shirin aukuwa
"Gidan uwarki da ubanki zani,zauna ki jirani" ya fada a tsawace yana tsige hannunsa daga nata,wani malolon takaici ya cika zuciyarta,kada dai ace mukhtar din na cikin saitinsa tayi wannan barin zancen?,yana nufin aikinta baiyi tasiri a kansa ba?,waishin wani irin mutum ne mukhtar din?,yana nufin dukka kashe kudi bata lokaci da sadaukar da jikinta da tayi ya tashi a banza?,to wallahi wannan karo kam bai isa ba,bai isa ya sanyata ci gaba da yin asara ba,kota hanyar tsiya kota arziqi,tsaye ta miqe a zafafe tana dubansa
"Kai mukhtar,na gaji,na gaji da asarar lokacina da kudina a kanka,me yasa bakasan darajar soyayya ba?"
Dauketa yayi da wani zazzafan mari wanda ya haddasa mata ganin wulgawar wasu taurari tare da zubewa warwas a qasa,lokaci guda jini yayi kwance gefan qwayar idanuwanta,kafin ta kai ga dawowa hayyacinta tuni ya garqame qofar falon sannan ya wuce ciki cikin matsanancin sauri,bedroom dinsa ya shiga ya kwantar da abdallah da bacci ya daukeshi kan fadar mukhtar din sannan ya fito ya rufe qofar dakin baccin ya rufe ta falo baki daya don bai fatan yaji ko yaga abinda yake shirin aikatawa,wani irin suya qirjinsa yake a fuskarsa yana jin wani hucin zafi na fita kamar wanda aka cilla cikin rumbun gasa biredi.