Sashe 28
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin su sake cewa wani abu zainab din ta daga labulen dakin ta danno tana fadin
"Dear fito mana na rakaka,ina ta jira fa"
"Ai gani nan" ya fada yana fiddo kudin cefane daga aljihunsa,wani banzan kallo da sumayyan batasan ta iyashi ba sai yau ta jefawa zainab sannan ta miqe zata fice ta bar musu dakin,mukhtar yace
"Ina kuma zaki sumayya bamu gama magana ba"
"Baka shirya yin maganar da ni bane" ta fada tana shigewa toilet abinta ta soma daura alwalar sallar walhar da dama ita take shirib tashi tayi.
Tana jiyosu daga nan zainab din na gaya masa ya qyaleta yazo su tafi,yace a'a taje falo ta jirashi zaya fito yanzu,a bandakin ya cimmata ta gama alwalar tana gyara daurin kallabinta,fuska a hade cikin kakkaurar murya yace mata
"Wai wane irin hali kika koya sumayya wanda ban sanki da shi ba,wannan wannw irin wulaqanci ne ina miki magana kina tafiya gaban zainab salon ki koya mata yadda zata raina ni", tsayawa tayi tana kallon ikon Allah,lallai a daki mutum a kuma hanashi kuka.
" ai tare muka siyi foam din makarantar koyon sabbin halaye ni da kai muka cike,muka kuma fara daukar darasi a ciki"sarai yaso ya fahimceta amma sai ya waske
"Wai duka sumayya don na qarawa zainab kwanaki kike wannan abun,yanzun ban isa da gidana ba kenan?"
"Isa kai,tunda gashi ka nuna salon taka isar" ta fada tana kashe famfo tare da qoqarin rabeshi ta wuce,sai ya janyota jikinsa ya matse gam,yasan kan abarsa take ya fara sauke mata fushinta,yayi nasara kam don itama bata bijire masa ba,don babu qarya tayi kewar mijinta sosai.
Ita ta fara zame jikinta sannan tace
"Ka gayawa matarka kada ta sake shigo kin daki kanta tsaye,sabida hakan ya sabawa dokar addinin musulunci idan ita din bata sani ba" sai ya lumshe ido ya dafe kai
"Oh sumayya harda mita ma sai da kika koya,to ayi haquri" daga nan sukayi sallama ya ajjiye mata kudin cefane duk da suna da komai.
Sosai zainab din ta qulu,ta fara lura sumayyan ta shalle zatonta,amma daga yau zata fara dasa bamabamanta cikin gidan,shanye komai tayi ta masa rakiya kamar ta hadeshu,duk yadda ya nuna jin dadinsa a fili amma zuciyarsa ta gaza karbar hakan,a boye ma Allah Allah yake ta koma ya samu ya fice daga gidan.
Da azahar ta shiga kitchen ta musu girkin rana,tana fitowa ta samu zainab din a falon zaune tana kallo,qafarta daya kan daya tana amsa waya,har sumayyan ta gifata ta taji ance
"Ke!" Da fari tayi zatan cikin wayarta ne sai taji ta sake cewa
"Ke dake nake magana sumayyata" waiwayowa tayi tana tsaye daga inda take
"Wai da ni kike?"
"Akwai wata mai sunan ne bayanke a gidan nan,koma ki dauko min abinci na".
Baki ta sake tana kallonta cikin mamaki,ita kuma nata salon kenan,sai ta kada kai kawai tace
" idan kin damu ki shiga da kanki ki dauko"
"Ni kike gayawa wannan maganar,lallai yau zaki gane niba irin sauran kishiyoyinki bane,wallahi yau sai kin gane matsayina gun mukhtar" bata tsaya bi ta kanta ba tayi komawarta daki don tana da abunyi.
Lambar mukhtar ta soma laluba tana huci,yana tsaka da sallamar custumer yaga kiran nata,sai da yaji wani dumm cikin kansa da yaga sunar,ko kadan baiyi farinciki ba amma sai ya gaza share kiran
"Amarya bakya laifi,ya gidan"
"Gida ba lafiya ba,mukhtar na fuskanci ka auroni ne don matarka ta rainani"
"Ya salam,me ya faru me tayi miki?"
"Bazan hanaka sana'a ba kabari idan ka dawo kaji koma mene ne,amma wallahi idan baka dauki mataki ba bazan ci gaba da zama cikin gidan nan ba" sai yaji wata faduwar gaba da sauri yace
"Haba zainab ki daina fadar wannan maganar mana,mai rabu mu ai sai Allah,bari na kira ita sumayyan naji" da sauri ta katseshi don bata son ya mata fadan tun yanzu lamarin ya wuce ba tare data iza wutar tafi haka ba
"A'ah nidai ban saka ba,nace ka bari kawai ka dawo"
"To shikenan sai na dawo din" ya fadi yana sauke wayar,sam jikinsa bai bashi sumayyan zata aikata wani abu na rashin mutunci ga zaina din ba,amma sai ya samu kansa da yarda da duka magan ganun zainab din.
Tun shuda saura ta gama fesa kwalliya tare da bade jikinta da turarenta data tanada na musamman wanda ke hargitsa tunani da lissafin mukhtar ya dinga maida su ba dai dai ba.
Cikin izza da isa ta fito daga dakin nata hannunta dauke da jug na kwalba wanda ta cikashi da lemin zobo da cups dinsa,tana tafe tana murmushin tarkon data d'ana ta ratso ta falo don fita harabar gidan,so take mukhtar din ya fara karo da ita kafin kowa saboda abinda ta tsara ya tafi dai dai ba tare da mishkila ba,idanunta ne suka sauka kan sumayya tada tsume cikin tata kwalliyar,wani irin material ne mai santsi kamar yanayin shufom saidai ya fishi kauri da aka matsawa dinkin wata shegiyar gown wadda ta fidda duk wata qira tata,kalar pink(ruwan hoda) ne mai turuwa,tayi amfani da dankunne da siririyar sarqa fashion baqaqe,hakanan abun hannunta zuwa zobe,take farincikin dake ranta ya ja baya ta raina tata kwalliyar data hasko farar fata ta hadu da pink da baqi,kishi ya sake taso mata,ya zama lallai kota halin qaqa tayi rugu rugu da gwamnatin sumayyan cikin zuciyar mukhtar ya zama tata ke wannan tashen,ta yadda zata yaga yarinyar yadda taga dama,yarinyar na neman fin qarfin zatonta,don ba'a rufe awa ba taga yadda ta tashi hankalin gidan da qamshin girkin abincin dare,ranta na suya ta fuce fuuu wanda sumayya bata ma lura da ita ba sai ficewarta ta gani kamar guguwa.
_tofa,yanzu ake yinta,muje zuwa_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣5⃣
____________________________
*wa tawakkal alal hayyul lazi la yamutu wasabbih bi hamdih*
_kayi tawakkali ka dogara da rayyayyen(Allah S W T)da baya mutuwa,kayi tasbihi/ka tsarkakeshi ka kuma gode masa_
____________________________
Guguwar dawowarta sumayya da taji ya sanyata daga kai ta bita da ido har ta shige dakinta.
Cikin mintinan da basu wuce biyu sumayyan ta fara jiyo qauri wanda yake da alama da wani abu aka sanya cikin garwashin wuta,data lura sosai sai ta fuskanci daga bangaren zainab ke fitowa,mai da kanta tayi taci gaba da kallonta,cikin sakanni qaurin ya buwayeta,hakan ya sanya ta koma dakinta ta dauko burner da turaren wuta ta fito falon wanda hakan yayi dai dai da sake ficewar fa'izan zuwa harabar gidan,jikin socket din dake daura da kayan kallon ta jona ta cikata da turaren wuta,mintina qalilan ya danne qaurin ya koma qamshi.
Tana zaune taji bude get din gidan da qarar motar mukhtar din,wanda hakan ke alamta dawowarsa,sai ta miqe ta koma daki ta sake feshe jikinta da turare sanna ta nufo harabar gidan.
Turus tayi ganin zainab gefan mukhtar tamkar zata shige jikinsa tana dubansa,hannunsa riqe da cup wanda ta cika masa da zobo wanda tuni ya fara kwankwada,yi tayi kamar ta juya saboda takaici sai kuna taga sam hakan baiyi tsari ba,zai kuma faranta ran zainab har taci karenta babu babbaka tunda ta riga da taga tsaiwarta.
Fuskarta ta fadada da fara'a,sannu a hankai ta soma takowa gun wanda takalmin qafarta duj da plate ne ya dinga bada sauti,hakan shi ya janye hankalin mukhtar ya zuba mata ido,ta masa kyau sosai,ji yake kamar ya tafi ya sureta ya daga sama yadfa suka saba,yau ta sauya masa sosai sumayyan,da wannan tunanin ta qaraso inda suke ta tsaya gabansa tana jifansa da murmushi,so yake take sumayyata kinyi kyau,so yake ya yaba mata,amma wani dunqulallen abun ya danne zuciyarsa,ya sake duban qwayar idanunta sai yaji wani bacin rai ya kamashi,murmushin da yakeson maida mata sai ya musanyashi da hade fusjarsa tsaf wanda hakan ya baiwa sumayyan mamaki,saidai duk da haka bata karaya ba ta miqa hannu ta amshi jakarsa tana masa sannu da zuwa.
Bai amsa ba don ji yayi ya gaza amsawar
"Wash" zainab ta fada wanda shi ya sanya su duja suka dubeta,baikai ga tambaya ba ta dora da nata jawabin
"Ka gani ko mukhtar,kaga abinda nake gaya maka ko?,yanzu fisabilillahi duk fadin gurin nan bai isheta ba sai ta takani saboda tsabar raini?" Mamaki fal zuciyar sumayya take dubanta,ya Allahu,nata salon kenan?matar da tazarar dake tsakaninsu ya isa tiqa tiqan mata biyu su tsaya shibe zata ce har ta taka ta?,tamkar dama neman abun fadan yake ya sake tunzura yana ji ana azqlzalar zuciyarsa,juyawa yayi yana jifan sumayyan da wani irin kallo
"Halayyar banzan da kike son koya kenan ko sumayya?,halayyar da ban sanki da ita ba?,to bari kiji ni bazan lamunta ba,bana son tashin hankali kin sani,har sau yaushe zan huta daga dawowata ko iskar gidan ban gama shaqa ba daga shigowarki zaki tada mana fitina?,to ki shiga hankalinki da ni idan ba haka ba zanyi mugun saba miki", bata data cewa,to me zata fada ma tunda ya riga ya yarda ya hau kai kuma ya zauna?,bata baki ne kawai tsayawa kare kai,saboda haka aladabce tace
" bansan na taka ta ba in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba kayi haquri ya mukhtar"sai da yaja fasali sannan yace
"Shikenan ta wuce"
"Au ni ba zaka ce ma ta ban haquri ba shikenan na gane matsayina wallahi" ta fada a zafafe tana fashewa da kukan kirsa sannan ta kwasa tayi cikin gidan da sauri,don sosai ta shaqa ba haka taso ya kasance ba,so tayi cikin biyu ayi daya,imma yace sumayyan ta durqusa ta bata haquri,ko kuma tayi qoqarin kare kanta ko ta masa turjiya ya jibgi banza a gabanta taci dariya ta more.
Da idanu sumayyan tabi mukhtar din ganin yadda ya diba shima ya bita cikin wani tashin hankali da yaji ya rikito masa sanda ya fara jiyo sautin kukanta,wanda babu qwalla ko daya sai tsabar ihu da iya manaqisa,kai sumayya ta kada zuciyarta ta karye,lallai babu shakka wani sabon SHAFIN QADDARAR TA NE YA SAKE BUDEWA CIKIN KUNDIN QADDARARTA,sau ta lallashi kanta kawai ta shige ciki da jakar tasa ta ratsa ta cikin falon nasu ta wuce sashen sa.
"Dear fito mana na rakaka,ina ta jira fa"
"Ai gani nan" ya fada yana fiddo kudin cefane daga aljihunsa,wani banzan kallo da sumayyan batasan ta iyashi ba sai yau ta jefawa zainab sannan ta miqe zata fice ta bar musu dakin,mukhtar yace
"Ina kuma zaki sumayya bamu gama magana ba"
"Baka shirya yin maganar da ni bane" ta fada tana shigewa toilet abinta ta soma daura alwalar sallar walhar da dama ita take shirib tashi tayi.
Tana jiyosu daga nan zainab din na gaya masa ya qyaleta yazo su tafi,yace a'a taje falo ta jirashi zaya fito yanzu,a bandakin ya cimmata ta gama alwalar tana gyara daurin kallabinta,fuska a hade cikin kakkaurar murya yace mata
"Wai wane irin hali kika koya sumayya wanda ban sanki da shi ba,wannan wannw irin wulaqanci ne ina miki magana kina tafiya gaban zainab salon ki koya mata yadda zata raina ni", tsayawa tayi tana kallon ikon Allah,lallai a daki mutum a kuma hanashi kuka.
" ai tare muka siyi foam din makarantar koyon sabbin halaye ni da kai muka cike,muka kuma fara daukar darasi a ciki"sarai yaso ya fahimceta amma sai ya waske
"Wai duka sumayya don na qarawa zainab kwanaki kike wannan abun,yanzun ban isa da gidana ba kenan?"
"Isa kai,tunda gashi ka nuna salon taka isar" ta fada tana kashe famfo tare da qoqarin rabeshi ta wuce,sai ya janyota jikinsa ya matse gam,yasan kan abarsa take ya fara sauke mata fushinta,yayi nasara kam don itama bata bijire masa ba,don babu qarya tayi kewar mijinta sosai.
Ita ta fara zame jikinta sannan tace
"Ka gayawa matarka kada ta sake shigo kin daki kanta tsaye,sabida hakan ya sabawa dokar addinin musulunci idan ita din bata sani ba" sai ya lumshe ido ya dafe kai
"Oh sumayya harda mita ma sai da kika koya,to ayi haquri" daga nan sukayi sallama ya ajjiye mata kudin cefane duk da suna da komai.
Sosai zainab din ta qulu,ta fara lura sumayyan ta shalle zatonta,amma daga yau zata fara dasa bamabamanta cikin gidan,shanye komai tayi ta masa rakiya kamar ta hadeshu,duk yadda ya nuna jin dadinsa a fili amma zuciyarsa ta gaza karbar hakan,a boye ma Allah Allah yake ta koma ya samu ya fice daga gidan.
Da azahar ta shiga kitchen ta musu girkin rana,tana fitowa ta samu zainab din a falon zaune tana kallo,qafarta daya kan daya tana amsa waya,har sumayyan ta gifata ta taji ance
"Ke!" Da fari tayi zatan cikin wayarta ne sai taji ta sake cewa
"Ke dake nake magana sumayyata" waiwayowa tayi tana tsaye daga inda take
"Wai da ni kike?"
"Akwai wata mai sunan ne bayanke a gidan nan,koma ki dauko min abinci na".
Baki ta sake tana kallonta cikin mamaki,ita kuma nata salon kenan,sai ta kada kai kawai tace
" idan kin damu ki shiga da kanki ki dauko"
"Ni kike gayawa wannan maganar,lallai yau zaki gane niba irin sauran kishiyoyinki bane,wallahi yau sai kin gane matsayina gun mukhtar" bata tsaya bi ta kanta ba tayi komawarta daki don tana da abunyi.
Lambar mukhtar ta soma laluba tana huci,yana tsaka da sallamar custumer yaga kiran nata,sai da yaji wani dumm cikin kansa da yaga sunar,ko kadan baiyi farinciki ba amma sai ya gaza share kiran
"Amarya bakya laifi,ya gidan"
"Gida ba lafiya ba,mukhtar na fuskanci ka auroni ne don matarka ta rainani"
"Ya salam,me ya faru me tayi miki?"
"Bazan hanaka sana'a ba kabari idan ka dawo kaji koma mene ne,amma wallahi idan baka dauki mataki ba bazan ci gaba da zama cikin gidan nan ba" sai yaji wata faduwar gaba da sauri yace
"Haba zainab ki daina fadar wannan maganar mana,mai rabu mu ai sai Allah,bari na kira ita sumayyan naji" da sauri ta katseshi don bata son ya mata fadan tun yanzu lamarin ya wuce ba tare data iza wutar tafi haka ba
"A'ah nidai ban saka ba,nace ka bari kawai ka dawo"
"To shikenan sai na dawo din" ya fadi yana sauke wayar,sam jikinsa bai bashi sumayyan zata aikata wani abu na rashin mutunci ga zaina din ba,amma sai ya samu kansa da yarda da duka magan ganun zainab din.
Tun shuda saura ta gama fesa kwalliya tare da bade jikinta da turarenta data tanada na musamman wanda ke hargitsa tunani da lissafin mukhtar ya dinga maida su ba dai dai ba.
Cikin izza da isa ta fito daga dakin nata hannunta dauke da jug na kwalba wanda ta cikashi da lemin zobo da cups dinsa,tana tafe tana murmushin tarkon data d'ana ta ratso ta falo don fita harabar gidan,so take mukhtar din ya fara karo da ita kafin kowa saboda abinda ta tsara ya tafi dai dai ba tare da mishkila ba,idanunta ne suka sauka kan sumayya tada tsume cikin tata kwalliyar,wani irin material ne mai santsi kamar yanayin shufom saidai ya fishi kauri da aka matsawa dinkin wata shegiyar gown wadda ta fidda duk wata qira tata,kalar pink(ruwan hoda) ne mai turuwa,tayi amfani da dankunne da siririyar sarqa fashion baqaqe,hakanan abun hannunta zuwa zobe,take farincikin dake ranta ya ja baya ta raina tata kwalliyar data hasko farar fata ta hadu da pink da baqi,kishi ya sake taso mata,ya zama lallai kota halin qaqa tayi rugu rugu da gwamnatin sumayyan cikin zuciyar mukhtar ya zama tata ke wannan tashen,ta yadda zata yaga yarinyar yadda taga dama,yarinyar na neman fin qarfin zatonta,don ba'a rufe awa ba taga yadda ta tashi hankalin gidan da qamshin girkin abincin dare,ranta na suya ta fuce fuuu wanda sumayya bata ma lura da ita ba sai ficewarta ta gani kamar guguwa.
_tofa,yanzu ake yinta,muje zuwa_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣5⃣
____________________________
*wa tawakkal alal hayyul lazi la yamutu wasabbih bi hamdih*
_kayi tawakkali ka dogara da rayyayyen(Allah S W T)da baya mutuwa,kayi tasbihi/ka tsarkakeshi ka kuma gode masa_
____________________________
Guguwar dawowarta sumayya da taji ya sanyata daga kai ta bita da ido har ta shige dakinta.
Cikin mintinan da basu wuce biyu sumayyan ta fara jiyo qauri wanda yake da alama da wani abu aka sanya cikin garwashin wuta,data lura sosai sai ta fuskanci daga bangaren zainab ke fitowa,mai da kanta tayi taci gaba da kallonta,cikin sakanni qaurin ya buwayeta,hakan ya sanya ta koma dakinta ta dauko burner da turaren wuta ta fito falon wanda hakan yayi dai dai da sake ficewar fa'izan zuwa harabar gidan,jikin socket din dake daura da kayan kallon ta jona ta cikata da turaren wuta,mintina qalilan ya danne qaurin ya koma qamshi.
Tana zaune taji bude get din gidan da qarar motar mukhtar din,wanda hakan ke alamta dawowarsa,sai ta miqe ta koma daki ta sake feshe jikinta da turare sanna ta nufo harabar gidan.
Turus tayi ganin zainab gefan mukhtar tamkar zata shige jikinsa tana dubansa,hannunsa riqe da cup wanda ta cika masa da zobo wanda tuni ya fara kwankwada,yi tayi kamar ta juya saboda takaici sai kuna taga sam hakan baiyi tsari ba,zai kuma faranta ran zainab har taci karenta babu babbaka tunda ta riga da taga tsaiwarta.
Fuskarta ta fadada da fara'a,sannu a hankai ta soma takowa gun wanda takalmin qafarta duj da plate ne ya dinga bada sauti,hakan shi ya janye hankalin mukhtar ya zuba mata ido,ta masa kyau sosai,ji yake kamar ya tafi ya sureta ya daga sama yadfa suka saba,yau ta sauya masa sosai sumayyan,da wannan tunanin ta qaraso inda suke ta tsaya gabansa tana jifansa da murmushi,so yake take sumayyata kinyi kyau,so yake ya yaba mata,amma wani dunqulallen abun ya danne zuciyarsa,ya sake duban qwayar idanunta sai yaji wani bacin rai ya kamashi,murmushin da yakeson maida mata sai ya musanyashi da hade fusjarsa tsaf wanda hakan ya baiwa sumayyan mamaki,saidai duk da haka bata karaya ba ta miqa hannu ta amshi jakarsa tana masa sannu da zuwa.
Bai amsa ba don ji yayi ya gaza amsawar
"Wash" zainab ta fada wanda shi ya sanya su duja suka dubeta,baikai ga tambaya ba ta dora da nata jawabin
"Ka gani ko mukhtar,kaga abinda nake gaya maka ko?,yanzu fisabilillahi duk fadin gurin nan bai isheta ba sai ta takani saboda tsabar raini?" Mamaki fal zuciyar sumayya take dubanta,ya Allahu,nata salon kenan?matar da tazarar dake tsakaninsu ya isa tiqa tiqan mata biyu su tsaya shibe zata ce har ta taka ta?,tamkar dama neman abun fadan yake ya sake tunzura yana ji ana azqlzalar zuciyarsa,juyawa yayi yana jifan sumayyan da wani irin kallo
"Halayyar banzan da kike son koya kenan ko sumayya?,halayyar da ban sanki da ita ba?,to bari kiji ni bazan lamunta ba,bana son tashin hankali kin sani,har sau yaushe zan huta daga dawowata ko iskar gidan ban gama shaqa ba daga shigowarki zaki tada mana fitina?,to ki shiga hankalinki da ni idan ba haka ba zanyi mugun saba miki", bata data cewa,to me zata fada ma tunda ya riga ya yarda ya hau kai kuma ya zauna?,bata baki ne kawai tsayawa kare kai,saboda haka aladabce tace
" bansan na taka ta ba in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba kayi haquri ya mukhtar"sai da yaja fasali sannan yace
"Shikenan ta wuce"
"Au ni ba zaka ce ma ta ban haquri ba shikenan na gane matsayina wallahi" ta fada a zafafe tana fashewa da kukan kirsa sannan ta kwasa tayi cikin gidan da sauri,don sosai ta shaqa ba haka taso ya kasance ba,so tayi cikin biyu ayi daya,imma yace sumayyan ta durqusa ta bata haquri,ko kuma tayi qoqarin kare kanta ko ta masa turjiya ya jibgi banza a gabanta taci dariya ta more.
Da idanu sumayyan tabi mukhtar din ganin yadda ya diba shima ya bita cikin wani tashin hankali da yaji ya rikito masa sanda ya fara jiyo sautin kukanta,wanda babu qwalla ko daya sai tsabar ihu da iya manaqisa,kai sumayya ta kada zuciyarta ta karye,lallai babu shakka wani sabon SHAFIN QADDARAR TA NE YA SAKE BUDEWA CIKIN KUNDIN QADDARARTA,sau ta lallashi kanta kawai ta shige ciki da jakar tasa ta ratsa ta cikin falon nasu ta wuce sashen sa.