Sashe 220
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
"Kiyi haquri ki kwantar da hankalinki kada ki jawo mana ya gane abinda ake ciki,in sha Allahu Allah zai baki lafiya" kai ta girgiza
"Ki qyaleni mummy,ki barni,kinsan me likitan ya aikata a gareni?,almustapha akwai nakeson gani,na tabbbatar da cewa rayuwata tazo qarshe kuma wuta zanje bayan na mutu" ta fada kuka na qwace mata,dai dai sanda almustapha ya turo qofar,ajiyar zuciya ya saki sanda ya ganta idanunta biyu,har ma sun cire mata oxcygyn din dake hancinta,idanunta a kanshi har ya shigo,ya qarasa gaban gadon mummyn ta janye baya gabanta na dukan uku uku,hannunshi su'ad din ta kama ta riqe qam tare da sakin kuka
"Shshshs....ya isa,ki daina kuka a irin wannan yanayin" ya fada yana shafa kanta cikin tausasawa
"Qyaleni almustapha nayi kuka,kasan me na aikata maka?,kasan me nayi maka?"kai yake kadawa bacin ranshi na sake tasowa yana qoqarin dannewa
"bance ki gaya min ba,ni kuka kawai nace ki bari" zata sake magana kenan aka turo qofar dakin aka shigo,baba professor ne sai alhj abdus samad mahaifinta da kuma ummee,daga baya sumayya ke biye da su da 'yan biyu wanda sam bai tunanin zuwanta ba,duba daya ta masa taga rama sosai tattare da shi,yayin data dubi su'ad kuma sai hankali ta ya tashi matuqa,cikin mutuwar jiki ta qaraso ciki,haj khaulat ce ta miqe tana musu sannu da zuwa suka amsa suna samun wajen zama,banda alhj abdus samad da ya qarasa gadon da su'ad ke kwance,sannu yayi mata saidai shiru tayi taqi amsa masa,sunyi tunanin ko zafin ciwo ne,baba prof ne ya sake mata sannu ba tare da tunanin zata amsa ba,ga mamakinsu sai ta waiwayo,ta daga hannunta ta yafici baban,cikin mamaki ya miqe,ya isa gefan alhj abdus samad ya tsaya
"Baaba,idan mutum ya haihu haka rayuwa take ka qyale yaronaka yayita abinda ransa yake so?,kaman ba haka bane,saboda naga yadda wasu masu yaran suke hana yaransu abinda ransu yake so,amma kaman zalunci ne hakan nake tunani a da,sai yanzu da lokaci ya quremin nake shanshano akwai dalili" kowa yayi mamakin maganar tata,amma sai baba ya gyara zama
"Ba d'a ba ko babba daya girma yana buqatar wanda zai dinga masa burki yana saitashi kan hanya,ya hanashi ba dai dai ba ya sashi dai dai" kai take gyadawa cikin gamsuwa
"Kaman yadda ka so ka nunamin a baya nace maka bana so kada ka sakemin haka?" Idanu suka hada da alhj abdus samad,bashi da zabi illa yace mata eh
"To wannan meye?"
"Gata ne kakewa rayuwar yaro" dubanta ta maida kan alhj abdus samad
"Wannan ne mahaifina amma baimin haka ba,bai taba tsayawa ya damu da halin da rayuwata ke ciki ba,bai taba zama ya tsawatar min ba,bai tana tsayawa ba bare yaga nayi dai dai ko na kuskure ba,ko yaushe kasuwancinsa ne gaba da komai,kanje gida na qaraci zamana ba tare daya sani ba...."
"Su'ad,wai me kike fada haka?" Haj khaukat ta tasi tana fada,saboda kada ta kwance musu zani a akasuwa,sosai idanuta suka firfito tana duban hajiyan
"Kada kice komai,inaga qwara shima a kanki,tunda tare yake barinmu ni da ke,duk abinda nace ina so komai girmanshi baki taba cemin a'ah ba,kince talaka ba mutum bane,talaka abun qyama ne na yarda hakanne,naga dabi'u masu yawa a wajenki na doru akai,wanda hakan ya sanya nake ganin namu dabi'un ne kawai daidai,dau tari zanga wasu dabi'um da suka burgeni,amma da zarar nayi niyyar aiwatarwa sai tarbiyyarki ta rinjayi tunani na na watsar,duk abinda nayi dai dai ne,sam baki taka rawarki ta uwa ba,ne zance dake momy?,cikin rashin sani kika dorani kan wannan hanyar ko kinsan ba dai dai bace kika nakasta rayuwata kika dorani?" Shiru ya ratsa dakin,kusan kowa jikinsa yayi sanyi qalau,sumayya tuni ta soma qwalla cikin mayafinta,wani abu take ji yana ratsata,tausayi ne,ita din shaida ce kan su'ad wata iriyar hargitsatsiyar rayuwa take
"Baba...." Ta kira sunanshi tana kallonshi,sai ya amsa yana sake nuna kulawarshi a gareta
"Ina jin ciwo cikin jikina,ina ji sama sama sanda doctor james ke cinikin qodata,ina jinsa,amma bansan me zan karanta ba wanda zai qwaceni daga sharrinsa,tun yana dariya yana gayamin bansan cewa babu amana tsakanin bayahude da musulmi ba?,bansan cewa basa sonmu nasa qaunarmu ba?,bansan cewa ba zasu taba taimakawa musulmi a banza ba ba tare da wata boyayyiyar manufarsu qasan ransu ba,yace har abada....baba.....magana ta qarshe ta kunne na yaji yace min,wani abokin karatunsa musulmi yaji yana gayawa 'yan uwansa cikin littafinmu Allahn mu yace "yahudu da nasara ba zasu taba yarda da kai ba har sai kabi addininsu"(wannan haka yake aya ce da tazo cikin alqur'ani mai girma,babu yadda babu amana tsakanin musulmi da bayahude matuqar ba addininsu kabi ba,saidai su nuna maka a baka kawai amma sam zuciyarsu ba haka take ba,kuma har yau muna kan wannan qadamin saidai mun kasa fahinta,bama kuna ganewa din har sai sun amana illa sannan zamu zo muna kaico,Allah kasa mu dace),wannan ne lafazin qarshe da yayi min" sai ta saki kuka cikin wahala yayin da sautin kukan sumayya ya fito,qirjinta ya dinga wani bugawa,tsoro ya kamata,lamarin har yayi girman haka?,rabata da qodarta?,sannan ta juya tana duban almustapha da ya kasa motsawa,ya dunqule hannayenshi cikin aljihunsa ya zubasu,idanunsa sun kada jajur
"Zo don Allah....zo" tace da shi,da qyar ya iya takawa zuwa inda take,hannunshi ta kama
"Da fari dukanmu munyi kuskuren zamantakewa ni da kai,saidai nawa kuskuren yafi naka,tunda har ka rigani gane kuskuren,ka kuma yi qoqarin maidoni hanya amma na bijire,tun kafin nan,naqi mu'amala da matan abokanka,naqi mu'amala da yarena addinina 'yan asalin qasar iyayena bare na gane kuskurena ta silar zamana da su na gyara,gani nake tunda arziqinsu bai kai na mijina ba basu isa ba,ba komai bane su,ban ganin su da gashi,kamin rarrashi a boye wanda daga ni saikai sai Allah muka sani naqi,kazo kamin na fili amma naqi,ban manta lafazin da ka yimin tafiyata ta qarshe wanda daga ita sai sabon aurenka KADA KI ZARGENI NAN GABA....kaci gaba da yimin qoqari naci gaba da sanya qafa ina shurewa,bayan babu abinda ka daukemin na game da haqqina harda wanda bai zama dole a kanka ba,baka fasa adalci tsakaninmu ba,hakanan duk wanda zaiyi ba daidai ba tsakaninmu zaka tsawatar masa,zata daumi nata laifin ta bada haquri ina kallo,amma nikam....sam sam...gani nake nafi qarfin juyawar namiji,nafi qarfin a zaunar da ni ana min fada,na dauka cewa namiji da mace duka dai dai suke......"
"Silence please su'ad" ya fada yana qoqarin tsaidata,dukka wannan ba shine gabanshi ba,plan dinsa ta yadda zai samo doctor james,murmushi ta saki
"Ka barni na fada na roqi yafiya mana,nasanka farin sani,nasan tunaninka a yanzu kawai na yadda zaka dauki fansa kan james don tunda mommy ta gayan kamin gwaje gwaje ina da tabbacin kaga abubuwan da na rasa a halitta ta,na rasa qodojina na kuma rasa mahaifata"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" dukkan wanda ke dakin ya furta cikin tsakanin kaduwa,banda momy wadda ta zube a qasa ba tare data shirya ba,duk da cewa furuci daya ne yake sabo a wajenta
"Eh....doctor james shi ya saida min qoda ga wani mutumi,amma mahaifa ni da kaina na kai kaina aka cire min ita" rintse idanunsa almustapha yayi
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya dinga furtawa can qasan ranshi,bakinshi ne kadai ke motsawa
"Nayi tunanin cewa haihuwa bata da wata rana matuqar kana da kudi,na dauka abu mai kyau nayi tunda mommy ta juya tata mahaifar,almustapha,idan kaso ka yafemin idan kuma ba zaka iya ba duk daya nasan idan na mutu wuta zan tafi,amma dai ina roqonka ka yafemin" ta fada tana zubda qwalla,rasa me zaice yayi?,a wacce duniya yake ciki?,hannunta ne kawai riqe cikin nashi,hango sumayya tayi dake sharar qwalla
"Zo...zo kema" sautin kukanta ne ya dadu,firgici da tsoro na cikata,wacce iriyar duniya ce wannan muke ciki?,da qyar ta iya tashi a daddafe ta isa gaban gadon itama saitin kanta
"Duk naga abubuwan da kike a zamanki da almustapha,wanda a sannan wani abu ya kange zuciyata na kasa ganin kyawun hakan bare nayi koyi,wanda ina da tabbacin ko nice shi a wannan bigiren dole na soki,a baya laifinsa nake gani,amma a yanzu na tabbatar da cewa baida laifi ko kadan,banfa san kwanansa da tashinsa ba,bansan cinsa da shansa ba,bansan me yakeso da wanda ke qona ranshi ba,duka ba ruwana,kawai ya jiqani da kudi ya bani freedom shikenan,girki kadai nasan na taba yi masa wanda zai iya dan shiga sahun nuna kyautatawa bayan shi din tunda muke da shi ban taba nema na rasa ba wajensa,koda zan jera wata ina tambaya,don me ya samu mai masa dukka irin wannan kulawa hakan zai kasa sonta?,ki yafemi kema duk da ba lallai yafiyar taki ta amfane ni ba" kuka ta saka sosai,tana jin su'ad kamar 'yar uwarta,a iya zamanta da ita banda furuci ko kallo bata taba wani abu na cutarwa a gareta koma bayan wannan ba,akan me zata riqeta?,meye zainab karima da a'iza basuyi mata ba?,tamkar zata shide ta furta
"Ki daina fadin haka,ki daina yanke qauna daga rahamar Allah,kowanne bawa da kalar qaddarashi,bakisan rayuwar da nayi ba abaya wanda ban taba tunanin a yanzu zanyi rayuwa irin wannan ba,ki godewa Allah daya sanya kika gane kuskuren naki,duk wanda kuma ya yafe maka ta karbu har a wajen Allah,nikam bakiyimin komai ba,ba abinda kika yimin,na yafemiki ina roqon Allah ya baki lafiya,ki yafemin nima idan na taba bata miki koda da mugun kallo ne" murmushi ta saka
"Kina da zuciya mai kyau wanda na tabbatar da kece na ganki cikin ciwo irin haka ba lallai na tausaya miki har nayi miki kuka haka ba,baki taba yimin komai ba saboda ko yaushe kina takatsantsan da hakan,koda kin yimin ma ya wuce har bada.....ki riqe almustapha da kyau wallahi kun dace....ya hada duk wani hali mai kyau amma rashin samun tarbiyya ta gari daga iyaye na gari ya janyo min na kasa riqeshi har na mori rayuwa mai inganci....ki kawo min 'yan biyu na sake ganinsu,na tabbatar da ace na zauna nayi rayuwa mai kyau da tuni ni haifesu....ummi" ta kira ummi dake gefe,itana qarasowa tayi
"Duk cikin yaranki kinfison almustapha,amma kika yi haquri kika zuba min ido ina yiwa rayuwarshi yadda naga dama,kinso nunan hanya kaman yadda baba yayi amma na taka miki birki,a ranan na miki rashin kunya gatse gatse wanda ina da yaqinim baki gayawa kowa ba sai yanzu dani na fada,kiyi haquri ki yafemin ummi,ki nema min gafara wajen duk wanda na taba batawa" itama ummin share qwalla take,tana ajjiye mata ummulkhir da ummu kulsun gefanta tana dubansu su'ad din
"Ba wanda baya kuskure cikin rayuwarshi su'ad,ma'aiki yana cewa tabbas ba don kuna ainata zunubi ba da tuni Allah ya tafiyar daku ya halicci wadansu,kuskure siffa ce ta dan adam saidai mafi alkhairinsu sune masu tuba,na yafe miki har abada,Allah ya tashi kafadarki don ya ara miki daman a nan gaba"
"Na gode ummi" ta fada tana shafa kansu ummulkhair a hankali ta furta
"I love you my kids"ta fada tana jin qaunar kyawawan yaran har cikin zuciyarta.
"Ki qyaleni mummy,ki barni,kinsan me likitan ya aikata a gareni?,almustapha akwai nakeson gani,na tabbbatar da cewa rayuwata tazo qarshe kuma wuta zanje bayan na mutu" ta fada kuka na qwace mata,dai dai sanda almustapha ya turo qofar,ajiyar zuciya ya saki sanda ya ganta idanunta biyu,har ma sun cire mata oxcygyn din dake hancinta,idanunta a kanshi har ya shigo,ya qarasa gaban gadon mummyn ta janye baya gabanta na dukan uku uku,hannunshi su'ad din ta kama ta riqe qam tare da sakin kuka
"Shshshs....ya isa,ki daina kuka a irin wannan yanayin" ya fada yana shafa kanta cikin tausasawa
"Qyaleni almustapha nayi kuka,kasan me na aikata maka?,kasan me nayi maka?"kai yake kadawa bacin ranshi na sake tasowa yana qoqarin dannewa
"bance ki gaya min ba,ni kuka kawai nace ki bari" zata sake magana kenan aka turo qofar dakin aka shigo,baba professor ne sai alhj abdus samad mahaifinta da kuma ummee,daga baya sumayya ke biye da su da 'yan biyu wanda sam bai tunanin zuwanta ba,duba daya ta masa taga rama sosai tattare da shi,yayin data dubi su'ad kuma sai hankali ta ya tashi matuqa,cikin mutuwar jiki ta qaraso ciki,haj khaulat ce ta miqe tana musu sannu da zuwa suka amsa suna samun wajen zama,banda alhj abdus samad da ya qarasa gadon da su'ad ke kwance,sannu yayi mata saidai shiru tayi taqi amsa masa,sunyi tunanin ko zafin ciwo ne,baba prof ne ya sake mata sannu ba tare da tunanin zata amsa ba,ga mamakinsu sai ta waiwayo,ta daga hannunta ta yafici baban,cikin mamaki ya miqe,ya isa gefan alhj abdus samad ya tsaya
"Baaba,idan mutum ya haihu haka rayuwa take ka qyale yaronaka yayita abinda ransa yake so?,kaman ba haka bane,saboda naga yadda wasu masu yaran suke hana yaransu abinda ransu yake so,amma kaman zalunci ne hakan nake tunani a da,sai yanzu da lokaci ya quremin nake shanshano akwai dalili" kowa yayi mamakin maganar tata,amma sai baba ya gyara zama
"Ba d'a ba ko babba daya girma yana buqatar wanda zai dinga masa burki yana saitashi kan hanya,ya hanashi ba dai dai ba ya sashi dai dai" kai take gyadawa cikin gamsuwa
"Kaman yadda ka so ka nunamin a baya nace maka bana so kada ka sakemin haka?" Idanu suka hada da alhj abdus samad,bashi da zabi illa yace mata eh
"To wannan meye?"
"Gata ne kakewa rayuwar yaro" dubanta ta maida kan alhj abdus samad
"Wannan ne mahaifina amma baimin haka ba,bai taba tsayawa ya damu da halin da rayuwata ke ciki ba,bai taba zama ya tsawatar min ba,bai tana tsayawa ba bare yaga nayi dai dai ko na kuskure ba,ko yaushe kasuwancinsa ne gaba da komai,kanje gida na qaraci zamana ba tare daya sani ba...."
"Su'ad,wai me kike fada haka?" Haj khaukat ta tasi tana fada,saboda kada ta kwance musu zani a akasuwa,sosai idanuta suka firfito tana duban hajiyan
"Kada kice komai,inaga qwara shima a kanki,tunda tare yake barinmu ni da ke,duk abinda nace ina so komai girmanshi baki taba cemin a'ah ba,kince talaka ba mutum bane,talaka abun qyama ne na yarda hakanne,naga dabi'u masu yawa a wajenki na doru akai,wanda hakan ya sanya nake ganin namu dabi'un ne kawai daidai,dau tari zanga wasu dabi'um da suka burgeni,amma da zarar nayi niyyar aiwatarwa sai tarbiyyarki ta rinjayi tunani na na watsar,duk abinda nayi dai dai ne,sam baki taka rawarki ta uwa ba,ne zance dake momy?,cikin rashin sani kika dorani kan wannan hanyar ko kinsan ba dai dai bace kika nakasta rayuwata kika dorani?" Shiru ya ratsa dakin,kusan kowa jikinsa yayi sanyi qalau,sumayya tuni ta soma qwalla cikin mayafinta,wani abu take ji yana ratsata,tausayi ne,ita din shaida ce kan su'ad wata iriyar hargitsatsiyar rayuwa take
"Baba...." Ta kira sunanshi tana kallonshi,sai ya amsa yana sake nuna kulawarshi a gareta
"Ina jin ciwo cikin jikina,ina ji sama sama sanda doctor james ke cinikin qodata,ina jinsa,amma bansan me zan karanta ba wanda zai qwaceni daga sharrinsa,tun yana dariya yana gayamin bansan cewa babu amana tsakanin bayahude da musulmi ba?,bansan cewa basa sonmu nasa qaunarmu ba?,bansan cewa ba zasu taba taimakawa musulmi a banza ba ba tare da wata boyayyiyar manufarsu qasan ransu ba,yace har abada....baba.....magana ta qarshe ta kunne na yaji yace min,wani abokin karatunsa musulmi yaji yana gayawa 'yan uwansa cikin littafinmu Allahn mu yace "yahudu da nasara ba zasu taba yarda da kai ba har sai kabi addininsu"(wannan haka yake aya ce da tazo cikin alqur'ani mai girma,babu yadda babu amana tsakanin musulmi da bayahude matuqar ba addininsu kabi ba,saidai su nuna maka a baka kawai amma sam zuciyarsu ba haka take ba,kuma har yau muna kan wannan qadamin saidai mun kasa fahinta,bama kuna ganewa din har sai sun amana illa sannan zamu zo muna kaico,Allah kasa mu dace),wannan ne lafazin qarshe da yayi min" sai ta saki kuka cikin wahala yayin da sautin kukan sumayya ya fito,qirjinta ya dinga wani bugawa,tsoro ya kamata,lamarin har yayi girman haka?,rabata da qodarta?,sannan ta juya tana duban almustapha da ya kasa motsawa,ya dunqule hannayenshi cikin aljihunsa ya zubasu,idanunsa sun kada jajur
"Zo don Allah....zo" tace da shi,da qyar ya iya takawa zuwa inda take,hannunshi ta kama
"Da fari dukanmu munyi kuskuren zamantakewa ni da kai,saidai nawa kuskuren yafi naka,tunda har ka rigani gane kuskuren,ka kuma yi qoqarin maidoni hanya amma na bijire,tun kafin nan,naqi mu'amala da matan abokanka,naqi mu'amala da yarena addinina 'yan asalin qasar iyayena bare na gane kuskurena ta silar zamana da su na gyara,gani nake tunda arziqinsu bai kai na mijina ba basu isa ba,ba komai bane su,ban ganin su da gashi,kamin rarrashi a boye wanda daga ni saikai sai Allah muka sani naqi,kazo kamin na fili amma naqi,ban manta lafazin da ka yimin tafiyata ta qarshe wanda daga ita sai sabon aurenka KADA KI ZARGENI NAN GABA....kaci gaba da yimin qoqari naci gaba da sanya qafa ina shurewa,bayan babu abinda ka daukemin na game da haqqina harda wanda bai zama dole a kanka ba,baka fasa adalci tsakaninmu ba,hakanan duk wanda zaiyi ba daidai ba tsakaninmu zaka tsawatar masa,zata daumi nata laifin ta bada haquri ina kallo,amma nikam....sam sam...gani nake nafi qarfin juyawar namiji,nafi qarfin a zaunar da ni ana min fada,na dauka cewa namiji da mace duka dai dai suke......"
"Silence please su'ad" ya fada yana qoqarin tsaidata,dukka wannan ba shine gabanshi ba,plan dinsa ta yadda zai samo doctor james,murmushi ta saki
"Ka barni na fada na roqi yafiya mana,nasanka farin sani,nasan tunaninka a yanzu kawai na yadda zaka dauki fansa kan james don tunda mommy ta gayan kamin gwaje gwaje ina da tabbacin kaga abubuwan da na rasa a halitta ta,na rasa qodojina na kuma rasa mahaifata"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" dukkan wanda ke dakin ya furta cikin tsakanin kaduwa,banda momy wadda ta zube a qasa ba tare data shirya ba,duk da cewa furuci daya ne yake sabo a wajenta
"Eh....doctor james shi ya saida min qoda ga wani mutumi,amma mahaifa ni da kaina na kai kaina aka cire min ita" rintse idanunsa almustapha yayi
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya dinga furtawa can qasan ranshi,bakinshi ne kadai ke motsawa
"Nayi tunanin cewa haihuwa bata da wata rana matuqar kana da kudi,na dauka abu mai kyau nayi tunda mommy ta juya tata mahaifar,almustapha,idan kaso ka yafemin idan kuma ba zaka iya ba duk daya nasan idan na mutu wuta zan tafi,amma dai ina roqonka ka yafemin" ta fada tana zubda qwalla,rasa me zaice yayi?,a wacce duniya yake ciki?,hannunta ne kawai riqe cikin nashi,hango sumayya tayi dake sharar qwalla
"Zo...zo kema" sautin kukanta ne ya dadu,firgici da tsoro na cikata,wacce iriyar duniya ce wannan muke ciki?,da qyar ta iya tashi a daddafe ta isa gaban gadon itama saitin kanta
"Duk naga abubuwan da kike a zamanki da almustapha,wanda a sannan wani abu ya kange zuciyata na kasa ganin kyawun hakan bare nayi koyi,wanda ina da tabbacin ko nice shi a wannan bigiren dole na soki,a baya laifinsa nake gani,amma a yanzu na tabbatar da cewa baida laifi ko kadan,banfa san kwanansa da tashinsa ba,bansan cinsa da shansa ba,bansan me yakeso da wanda ke qona ranshi ba,duka ba ruwana,kawai ya jiqani da kudi ya bani freedom shikenan,girki kadai nasan na taba yi masa wanda zai iya dan shiga sahun nuna kyautatawa bayan shi din tunda muke da shi ban taba nema na rasa ba wajensa,koda zan jera wata ina tambaya,don me ya samu mai masa dukka irin wannan kulawa hakan zai kasa sonta?,ki yafemi kema duk da ba lallai yafiyar taki ta amfane ni ba" kuka ta saka sosai,tana jin su'ad kamar 'yar uwarta,a iya zamanta da ita banda furuci ko kallo bata taba wani abu na cutarwa a gareta koma bayan wannan ba,akan me zata riqeta?,meye zainab karima da a'iza basuyi mata ba?,tamkar zata shide ta furta
"Ki daina fadin haka,ki daina yanke qauna daga rahamar Allah,kowanne bawa da kalar qaddarashi,bakisan rayuwar da nayi ba abaya wanda ban taba tunanin a yanzu zanyi rayuwa irin wannan ba,ki godewa Allah daya sanya kika gane kuskuren naki,duk wanda kuma ya yafe maka ta karbu har a wajen Allah,nikam bakiyimin komai ba,ba abinda kika yimin,na yafemiki ina roqon Allah ya baki lafiya,ki yafemin nima idan na taba bata miki koda da mugun kallo ne" murmushi ta saka
"Kina da zuciya mai kyau wanda na tabbatar da kece na ganki cikin ciwo irin haka ba lallai na tausaya miki har nayi miki kuka haka ba,baki taba yimin komai ba saboda ko yaushe kina takatsantsan da hakan,koda kin yimin ma ya wuce har bada.....ki riqe almustapha da kyau wallahi kun dace....ya hada duk wani hali mai kyau amma rashin samun tarbiyya ta gari daga iyaye na gari ya janyo min na kasa riqeshi har na mori rayuwa mai inganci....ki kawo min 'yan biyu na sake ganinsu,na tabbatar da ace na zauna nayi rayuwa mai kyau da tuni ni haifesu....ummi" ta kira ummi dake gefe,itana qarasowa tayi
"Duk cikin yaranki kinfison almustapha,amma kika yi haquri kika zuba min ido ina yiwa rayuwarshi yadda naga dama,kinso nunan hanya kaman yadda baba yayi amma na taka miki birki,a ranan na miki rashin kunya gatse gatse wanda ina da yaqinim baki gayawa kowa ba sai yanzu dani na fada,kiyi haquri ki yafemin ummi,ki nema min gafara wajen duk wanda na taba batawa" itama ummin share qwalla take,tana ajjiye mata ummulkhir da ummu kulsun gefanta tana dubansu su'ad din
"Ba wanda baya kuskure cikin rayuwarshi su'ad,ma'aiki yana cewa tabbas ba don kuna ainata zunubi ba da tuni Allah ya tafiyar daku ya halicci wadansu,kuskure siffa ce ta dan adam saidai mafi alkhairinsu sune masu tuba,na yafe miki har abada,Allah ya tashi kafadarki don ya ara miki daman a nan gaba"
"Na gode ummi" ta fada tana shafa kansu ummulkhair a hankali ta furta
"I love you my kids"ta fada tana jin qaunar kyawawan yaran har cikin zuciyarta.