Sashe 72
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari tana zaune falo ita da hafiz da minal suna kallo,hafiz kuma na goge musu uniform dinsu,da yake da kansu suke wankinsu saboda suna da inji wanki(washing machine),sumayya ke girkin dare suna ta murna yau zasu ci tuwo saboda haka hankalinta ta rabashi gida biyu,anty dije ce ta sauko daga sama laila na binta a baya hannunta riqe da turamen atamfofi guda biyar,har suka qaraso falon laila na wa anty dujin rakin kayan sun mata nauyi
"To hafiz guga yake muku da ya rakaki,khalipha kuma nasan idan ya bikin ba dawowa zaiyi da wuri ba,kuma aiki ne da shi zaiyi gyaran jakankunan makaranta,idan kinje bakin get baba haruna ya karba miki ku qarasa ciki"
"To" lailan ta fada tana nishi ta fice,dariya sumayya ta dinga yi mata tana tsokanarta wai taji kunya.
Minti kusan ashirin shiru laila bata dawo ba har sumayyan ta kammala abincin dare,anty dije dake shirin shiga wanka ta sauko qasa tana duban sumayya
"Kinji lailan itama shiru kamar an aiki bawa garinsu?"
"Ko a tura khalipha ya ganota tunda har yanzu hafiz bai gama gugar ba?"
"A'ah,ai duk kanwar ja ce,sanya mayafinki don Allah ya rakaki ki gano min ita" fuska ta yamutsa
"Banson fita anty wlh"hararata tayi
"ke kam ko gajiya da zama a gida bakiyi,tun jiya da kika shigo ko waje baki leqa ba,to ba wani gu bane gidan Baabaa prof ne,gashinan yana kallon gidan nan" dan jim ta sake yi,haka kawai bata son shiga gidan,don tun daga qofar get din zaka ga banbamci qarara da sauran gidajen da ke dukka layin da kewayen unguwan,ba yadda ta iya ta shiga daki ta fiddo dogon hijabinta ta dora saman riga da skert na atamfa dake jikinta ta zura silifa ta fito khalipha ya biyo bayanta.
Khalipha na gaba tana biye da shi har bakin tamqamemen get din gidan,qwanqwasawa ya shiga yi a hankali,daga ciki taji ance cikin wata dattijuwar murya
"Kai,waye a nan"
"Khalipha ne"
"A'ah,khalipha khalipha 'yan kano" taji ana fadi kafin taji motsin bude qofar,dattijo ne wanda a qalla zaiyi shekaru sittin tsaye a gabansu hannunsa riqe da buta yana murmushi
"Ina wuni baba halliru"
"Lafiya qalau khalipopi,dazu naga laila ta wuce ai tana tafiya da qyar da kaya a hannu,sai haruna ne ya qarasa mata da su" baban ya fada yana basu hanya su wuce,russunawa rayi cikin girmamawa kamar yadda halayyarta take ta gaidashi amsawa yayi cikin fara'a,khalipha uban 'yan surutu yayi caraf yace
"Yayarmu ce baba daga kano muka taho da ita"
"Sannu da zuwa" baban yace ta amsa da yauwa sannan ta ja khalipha suka wuce ciki.
A darare taki bin bayan khaliphan wanda yayi gaba abinsa da alamun sabo da gidan a tattare da shi,girma da kyawun gida ya ratsata tare da bata mamaki,zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba ganin gida kwatankwacinsa ba,ko ina ka kalla qasan gidan a shimfide yake da grass carfet,babban gida ne wanda aka tsara gininsa,sannan aka baje fasaha aka fidda sassa sassa a gidan a zamanance masu kyau da kama da juna,gidan na dauke da sassa biyu manya,kowanne sashe akwai sasanni a cikinsa guda uku masu yalwa da tsari kuma kowanne ma dauke da bene,babban sashin dake hannun dama sashi ne na mai gidan da matansa guda biyu,daya sashen kuma sashe ne da tun usuli yake mallakar yaransa maza su uku tun zamanin samartakarsu har ya zuwa yanzu da dukkansu sukayi aure mallakarsu ne suna amfani da shi lokaci zuwa lokaci,kallo daya zaka yiwa gidan ya burgeka saboda tsarinsa da yanayinsa,komai luf luf a tsaftace a killace,kama daga wajen hutawa dake gefe guda,gun ajiyar motoci wajej wasannin motsa jiki da lambun dake daga bayan gidan.
Sashen dake hannun dama khalipha ya dosa,ganin sun tunkari wata qofa ya sanya sumayya riqeshi
"Kai,wai ina zamu?" Dariya yayi
"Kiran anty laila mana"
"A wanne guri?"
"Gun ummee ko gun anty maamaa" sakinsa tayi tana kokwanto kafin daga bisani ta bishi.
Shi ya tura qofar falon da sallama kafin itama tayi tata,saka kanta kawai ya sanar mata akwai sauyin yanayi sosai tattare da gun,falo ne na alfarma wanda ya ginu ya kuma tsaru abun burgewa da sha'awa ga idanuwa,tsit falon yake babu kowa sai tafkekiyar t.v plasma dake barazanar mamaye bango dake manne tana aikinta a tashar sunna t.v,carfet ne mamaye da falon duk girmansa a maimakon tiles,labulaye da kujeru na alfarma kalar carfet din mai azabar taushi,flower vase ce masu kyau qirar qasar chaina a sakaye a kowacce kusurwa ta falon,sai tarin kayan turaren wuta da humra dake ajjiye cikin tsari gu guda,da qananun centre table dake tsakanin kujeru don ajjiyewa baqo abin sha,ba wani tarkacen qyale qyale bane a falon amma ya tsaru,hakanan duk abinda ke cikinsa mai kyau ne da tsada,qamshi da sanyin da falon ke bayarwa kadai ya ishi zuciya samun nutsuwa.
Sallama ta qarayi tana wuwwurga idanuwa cikin falon jin shuru ba motsin mutane duk da tana iya jiyo qamshin girki dake tasowa bisa dukkan alamu kitchen din na cikin falon duk da bata iya gano qofar da kitchen din yake,jin still shiru yasa ta juya ta dubi khalipha
"Wai ina ka kawo mu nan ne khalipha,kasan dai nan babu alamun laila,inda tana nan da tuni ka jiyo ka......." Qarar takalmi da ta jiyo alamun ana saukowa daga saman benen ya sanyata yin shuru ba tare da ta qarasa fadar abinda takeson fadin ba
"Ha'an,khalipha ne?" Taji ana fada wanda hakan ya sanyata daga kai.
Farar mace wadda a qalla za'a kira da mai matsakaitan shekaru wanda hutu da tsabta suka kwakwashe shekarunta suka boye,a zahiri ta tasamma shekara hamsin da uku amma kai baka ce haka ba,fara ce tas kamar yadda nace a baya wanda har wani yellow takeyi,kallon farko zaka san cewa zamanin quruciya an kasa maza da yawa a kanta,akwai kyau da kansa zaune a fuskarta,duk da shekarun da take da su amma basu ci nasarar boye kyawun nata ba wanda hakan ke nuna na asali ne ko kuma ace na gado ne,tana da matsakaicin tsaho yayin da jikinta ke a murje,sam babu rama ko qiba tattare da ita,fuskarta a sake take saukowa daga saman tana sanye da jar atamfa da ta haskata dinkin riga da plain zani
"Ummee ina kwana" murmushi ta saki har sai da fararen haqoranta suka bayyana
"Ina kwana ko ina wuni khalipha sarkin shirme,ku zauna mana sai mu gaisa ko?,baquwa mukayi" an aosa masa inda ke masa qaiqayi
"Eh yayarmu ce muka taho da ita ummee,itama ta dawo nan ta zama 'yar gidanmu" dariya sosai ya bawa ummeen duk da kasancewarta mara son hayaniya,gu ta samu ta zauna,hakan ya sanya sumayya dake qame gu daya ta qaraso a hankali kanta a qasa ta samu gefan kujera ta zauna,hakanan take jin matar ta mata wani kwarjini da girma
"A'ah tashi baquwa ki koma saman kujera... Me sunanta khalipha?"
"Anty sumayya"
"Tashi sumayya ki koma sama" kai ta girgiza don ta qagu ta koma gida
"Yanzu zamu koma laila muka zo dubawa anty taji shiru" ta fada sannan ta soma gaidata,amsawa tayi tana cewa
"Na tsammaci ai ta koma tun dazun data kawomin aiken ta fita,amma ba mamaki suna wajen maamaa bilkisu,don nayi hayaniyan yaran gunta"
"To sai anjima" ta fada tana miqewa
"Yauwa rakata khalipha wajen maaamaanku,ki yiwa khadijan godiya naga sautu sunyi kyau"
"To zataji" ta fada suna nufar qofar fita daga bangaren nata,saidai kafin sukai ta shigo,budurwar rannan ce sanye take da gown mara nauyi wadda take armless bata da hannu,sai siririn mayafi data yane tulin tsefaffen gashin kanta da shi ,kumatunta duka biyun da hannunta jagale suke da wani abu kamar butter,sallama tayi tana dariya idanunta a kan ummee dake dubanta itama,harara ta watsa mata
"Da kyau,sannu shugabar masu shiririta,shine kika dora mishi girki sannan kika tafi kika tara yara kuna wani birthday din shirme,to sai ki wuce ki duba Allah yasa ya qone,wallahi ya shigo kada ma ki dosheni don baxan qwaceki ba a hannunshi" idanuwa ta qwalalo cike da tsoro,sannan ta kwashi sauri ta nufi hanyar kitchen din fuska a kwabe kamar zatayi kuka tana cewa
"Wayyo ummee na banu don Allah kada kicemin girkin ya qone"
"Ke kika sani" ummin ta fada.
Shikam khalipha fuska ya bata bayan sun fito
"Ina ga yau bithday din siddiqa shi yasa ma anty laila taqi dawowa gida tunda aka aiketa,tunda naga anty amira ma nasam da qyar idan ba yau bane,dama tun kafin mu tafi kano anty amira tace an kusa,wayyo mami duk ita ta hanamu zuwa" ya qarashe kamar zaiyi kuka,itakam sumayya bata ce komai ba,duban hanya take ganin sun nufi wani sashen na daban.
Tun kafin su shiga ta tabbatar akwai banbanci tsakanin waccen sashen da wannan,tun a qofa ta fara jiyo hayaniya da ifce ifcen yara,da banbancin kam,don wannan falon cike yake da yara sun kusa su goma sha biyu,qananu da matsakaita,baki dayansu sanye suke da gown suma mara hannu,dukkan rigunan irin daya ne,hatta safunan qafafunsu(socks)iri daya ne,yaran sunyi kyau gwanin sha'awa,tsakiyar falon qaton cake ne wanda suka dora kan center suna ta wadaqarsu da shi,da alamu shi ya bata jikin budurwar data gani dazu,kusan ba wanda yaji sallamarsu sai wata mata dake tsaye daura da su tana kallonsu idan zasuyi ba dai dai ba ta gyara musu,ita ta juyo murmushi dauke a fuskarta tana amsa musu sallamar idanuwanta kan sumayya,gaidata tayi tana duban laila da ta nufo gun saboda taga shigowarsu
"Wuce muje" sumayya ta fada tana mai juyawa tare da cewa sai anjima tasa laila a gaba.
Daf da zasu fice taji matar na fadi cikin daga murya
"kuyi maza ku kwashe kayayyakinku zansa a gyara gurin kada uncle ya shigo ya tadda wajen haka...." Bata qarasa jin me suke cewa ba don sun fice.
"To hafiz guga yake muku da ya rakaki,khalipha kuma nasan idan ya bikin ba dawowa zaiyi da wuri ba,kuma aiki ne da shi zaiyi gyaran jakankunan makaranta,idan kinje bakin get baba haruna ya karba miki ku qarasa ciki"
"To" lailan ta fada tana nishi ta fice,dariya sumayya ta dinga yi mata tana tsokanarta wai taji kunya.
Minti kusan ashirin shiru laila bata dawo ba har sumayyan ta kammala abincin dare,anty dije dake shirin shiga wanka ta sauko qasa tana duban sumayya
"Kinji lailan itama shiru kamar an aiki bawa garinsu?"
"Ko a tura khalipha ya ganota tunda har yanzu hafiz bai gama gugar ba?"
"A'ah,ai duk kanwar ja ce,sanya mayafinki don Allah ya rakaki ki gano min ita" fuska ta yamutsa
"Banson fita anty wlh"hararata tayi
"ke kam ko gajiya da zama a gida bakiyi,tun jiya da kika shigo ko waje baki leqa ba,to ba wani gu bane gidan Baabaa prof ne,gashinan yana kallon gidan nan" dan jim ta sake yi,haka kawai bata son shiga gidan,don tun daga qofar get din zaka ga banbamci qarara da sauran gidajen da ke dukka layin da kewayen unguwan,ba yadda ta iya ta shiga daki ta fiddo dogon hijabinta ta dora saman riga da skert na atamfa dake jikinta ta zura silifa ta fito khalipha ya biyo bayanta.
Khalipha na gaba tana biye da shi har bakin tamqamemen get din gidan,qwanqwasawa ya shiga yi a hankali,daga ciki taji ance cikin wata dattijuwar murya
"Kai,waye a nan"
"Khalipha ne"
"A'ah,khalipha khalipha 'yan kano" taji ana fadi kafin taji motsin bude qofar,dattijo ne wanda a qalla zaiyi shekaru sittin tsaye a gabansu hannunsa riqe da buta yana murmushi
"Ina wuni baba halliru"
"Lafiya qalau khalipopi,dazu naga laila ta wuce ai tana tafiya da qyar da kaya a hannu,sai haruna ne ya qarasa mata da su" baban ya fada yana basu hanya su wuce,russunawa rayi cikin girmamawa kamar yadda halayyarta take ta gaidashi amsawa yayi cikin fara'a,khalipha uban 'yan surutu yayi caraf yace
"Yayarmu ce baba daga kano muka taho da ita"
"Sannu da zuwa" baban yace ta amsa da yauwa sannan ta ja khalipha suka wuce ciki.
A darare taki bin bayan khaliphan wanda yayi gaba abinsa da alamun sabo da gidan a tattare da shi,girma da kyawun gida ya ratsata tare da bata mamaki,zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba ganin gida kwatankwacinsa ba,ko ina ka kalla qasan gidan a shimfide yake da grass carfet,babban gida ne wanda aka tsara gininsa,sannan aka baje fasaha aka fidda sassa sassa a gidan a zamanance masu kyau da kama da juna,gidan na dauke da sassa biyu manya,kowanne sashe akwai sasanni a cikinsa guda uku masu yalwa da tsari kuma kowanne ma dauke da bene,babban sashin dake hannun dama sashi ne na mai gidan da matansa guda biyu,daya sashen kuma sashe ne da tun usuli yake mallakar yaransa maza su uku tun zamanin samartakarsu har ya zuwa yanzu da dukkansu sukayi aure mallakarsu ne suna amfani da shi lokaci zuwa lokaci,kallo daya zaka yiwa gidan ya burgeka saboda tsarinsa da yanayinsa,komai luf luf a tsaftace a killace,kama daga wajen hutawa dake gefe guda,gun ajiyar motoci wajej wasannin motsa jiki da lambun dake daga bayan gidan.
Sashen dake hannun dama khalipha ya dosa,ganin sun tunkari wata qofa ya sanya sumayya riqeshi
"Kai,wai ina zamu?" Dariya yayi
"Kiran anty laila mana"
"A wanne guri?"
"Gun ummee ko gun anty maamaa" sakinsa tayi tana kokwanto kafin daga bisani ta bishi.
Shi ya tura qofar falon da sallama kafin itama tayi tata,saka kanta kawai ya sanar mata akwai sauyin yanayi sosai tattare da gun,falo ne na alfarma wanda ya ginu ya kuma tsaru abun burgewa da sha'awa ga idanuwa,tsit falon yake babu kowa sai tafkekiyar t.v plasma dake barazanar mamaye bango dake manne tana aikinta a tashar sunna t.v,carfet ne mamaye da falon duk girmansa a maimakon tiles,labulaye da kujeru na alfarma kalar carfet din mai azabar taushi,flower vase ce masu kyau qirar qasar chaina a sakaye a kowacce kusurwa ta falon,sai tarin kayan turaren wuta da humra dake ajjiye cikin tsari gu guda,da qananun centre table dake tsakanin kujeru don ajjiyewa baqo abin sha,ba wani tarkacen qyale qyale bane a falon amma ya tsaru,hakanan duk abinda ke cikinsa mai kyau ne da tsada,qamshi da sanyin da falon ke bayarwa kadai ya ishi zuciya samun nutsuwa.
Sallama ta qarayi tana wuwwurga idanuwa cikin falon jin shuru ba motsin mutane duk da tana iya jiyo qamshin girki dake tasowa bisa dukkan alamu kitchen din na cikin falon duk da bata iya gano qofar da kitchen din yake,jin still shiru yasa ta juya ta dubi khalipha
"Wai ina ka kawo mu nan ne khalipha,kasan dai nan babu alamun laila,inda tana nan da tuni ka jiyo ka......." Qarar takalmi da ta jiyo alamun ana saukowa daga saman benen ya sanyata yin shuru ba tare da ta qarasa fadar abinda takeson fadin ba
"Ha'an,khalipha ne?" Taji ana fada wanda hakan ya sanyata daga kai.
Farar mace wadda a qalla za'a kira da mai matsakaitan shekaru wanda hutu da tsabta suka kwakwashe shekarunta suka boye,a zahiri ta tasamma shekara hamsin da uku amma kai baka ce haka ba,fara ce tas kamar yadda nace a baya wanda har wani yellow takeyi,kallon farko zaka san cewa zamanin quruciya an kasa maza da yawa a kanta,akwai kyau da kansa zaune a fuskarta,duk da shekarun da take da su amma basu ci nasarar boye kyawun nata ba wanda hakan ke nuna na asali ne ko kuma ace na gado ne,tana da matsakaicin tsaho yayin da jikinta ke a murje,sam babu rama ko qiba tattare da ita,fuskarta a sake take saukowa daga saman tana sanye da jar atamfa da ta haskata dinkin riga da plain zani
"Ummee ina kwana" murmushi ta saki har sai da fararen haqoranta suka bayyana
"Ina kwana ko ina wuni khalipha sarkin shirme,ku zauna mana sai mu gaisa ko?,baquwa mukayi" an aosa masa inda ke masa qaiqayi
"Eh yayarmu ce muka taho da ita ummee,itama ta dawo nan ta zama 'yar gidanmu" dariya sosai ya bawa ummeen duk da kasancewarta mara son hayaniya,gu ta samu ta zauna,hakan ya sanya sumayya dake qame gu daya ta qaraso a hankali kanta a qasa ta samu gefan kujera ta zauna,hakanan take jin matar ta mata wani kwarjini da girma
"A'ah tashi baquwa ki koma saman kujera... Me sunanta khalipha?"
"Anty sumayya"
"Tashi sumayya ki koma sama" kai ta girgiza don ta qagu ta koma gida
"Yanzu zamu koma laila muka zo dubawa anty taji shiru" ta fada sannan ta soma gaidata,amsawa tayi tana cewa
"Na tsammaci ai ta koma tun dazun data kawomin aiken ta fita,amma ba mamaki suna wajen maamaa bilkisu,don nayi hayaniyan yaran gunta"
"To sai anjima" ta fada tana miqewa
"Yauwa rakata khalipha wajen maaamaanku,ki yiwa khadijan godiya naga sautu sunyi kyau"
"To zataji" ta fada suna nufar qofar fita daga bangaren nata,saidai kafin sukai ta shigo,budurwar rannan ce sanye take da gown mara nauyi wadda take armless bata da hannu,sai siririn mayafi data yane tulin tsefaffen gashin kanta da shi ,kumatunta duka biyun da hannunta jagale suke da wani abu kamar butter,sallama tayi tana dariya idanunta a kan ummee dake dubanta itama,harara ta watsa mata
"Da kyau,sannu shugabar masu shiririta,shine kika dora mishi girki sannan kika tafi kika tara yara kuna wani birthday din shirme,to sai ki wuce ki duba Allah yasa ya qone,wallahi ya shigo kada ma ki dosheni don baxan qwaceki ba a hannunshi" idanuwa ta qwalalo cike da tsoro,sannan ta kwashi sauri ta nufi hanyar kitchen din fuska a kwabe kamar zatayi kuka tana cewa
"Wayyo ummee na banu don Allah kada kicemin girkin ya qone"
"Ke kika sani" ummin ta fada.
Shikam khalipha fuska ya bata bayan sun fito
"Ina ga yau bithday din siddiqa shi yasa ma anty laila taqi dawowa gida tunda aka aiketa,tunda naga anty amira ma nasam da qyar idan ba yau bane,dama tun kafin mu tafi kano anty amira tace an kusa,wayyo mami duk ita ta hanamu zuwa" ya qarashe kamar zaiyi kuka,itakam sumayya bata ce komai ba,duban hanya take ganin sun nufi wani sashen na daban.
Tun kafin su shiga ta tabbatar akwai banbanci tsakanin waccen sashen da wannan,tun a qofa ta fara jiyo hayaniya da ifce ifcen yara,da banbancin kam,don wannan falon cike yake da yara sun kusa su goma sha biyu,qananu da matsakaita,baki dayansu sanye suke da gown suma mara hannu,dukkan rigunan irin daya ne,hatta safunan qafafunsu(socks)iri daya ne,yaran sunyi kyau gwanin sha'awa,tsakiyar falon qaton cake ne wanda suka dora kan center suna ta wadaqarsu da shi,da alamu shi ya bata jikin budurwar data gani dazu,kusan ba wanda yaji sallamarsu sai wata mata dake tsaye daura da su tana kallonsu idan zasuyi ba dai dai ba ta gyara musu,ita ta juyo murmushi dauke a fuskarta tana amsa musu sallamar idanuwanta kan sumayya,gaidata tayi tana duban laila da ta nufo gun saboda taga shigowarsu
"Wuce muje" sumayya ta fada tana mai juyawa tare da cewa sai anjima tasa laila a gaba.
Daf da zasu fice taji matar na fadi cikin daga murya
"kuyi maza ku kwashe kayayyakinku zansa a gyara gurin kada uncle ya shigo ya tadda wajen haka...." Bata qarasa jin me suke cewa ba don sun fice.