Sashe 101
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A dakinsu na jiya sumayyan ta tadda su,tana qunshe dariya ta qarasa,dariya amiran ta saka tana harararta
"Wallahi kin maida ni wata iri amira,godiya nake"
"Afuwa namecy,afwa"ta qarasa ciki suna gaisawa da 'yammatan dake ciki,gira ta daga
" to ya zanyi da ke,ni na kai kaina inda ba'a damu da ni ba,muje kimin rakiya wajen baabaa"
"Ya kamata,don nima ina son inje in gaidashi" eesha dake shan tea ta ajjuye cup din tana yiwa sumayyan duban ita kuma a wa?,kamar zata furta sai kuma ta fasa,ta miqe itama tana yafa dan yalolon mayafi kan kayan baccinta tana cewa
"Muje nima nayi rakiya"
"Owk" amira ta fada ta dubi su hibba
"Oya,ku wuce ku tafi wasanku" juyawa sukayi hibba ta tsaya ta karbi abdallah suka wuce.
Sai da suka shiga wajen anty maamaa da ummee ta gaidasu sannan ta suka wuce zuwa sashen tsohon.
Zaune yake gefan umminsa daga shi sai itayana kurbar coffee,idan da kowa a gun ta tabbata bazai sha ba,wanda ta shiga kitchen da kanta ta hada masa,dubanshi take qasa qasa,ita daya take iya gane mustaphan,tayi tsammanin idan yayi aure shikenan komai ya qare,matarsa zata fahimceshi fiye da kowa,saidai kash,sabanin haka ne ya faru,matarsa itace wadda bata fahimceshi ba fiye da kowa,a yanzun kallo daya tayi masa ta fahimci yunwa yake ji,bazai iya gaya mata ba,zai iya ci gaba da zamansa haka har sai an bashi,idan ya gaji ya kuma yana iya fita can wani wajen cin abincin yaci abinshi,time to time yakan sanya matarsa tazo ta karba masa idan yunwar taci tura,hatta da amira tafi matarsa sanin ko shi waye,wani irin mutum ne shi mai wuyar sha'ani,ba kowa ke iya fahimtarsa ba,bai iya sharing damuwarsa ko shawararsa da kowa idan ka dauke ummeen da baabaansa,tayi zaton idan yayi aure wannan zai zama aikin matarsa,saidai ina ma yaga matar bare ta dauki wannan responsibility din,saidai komai tana ganin ya kusa zuwa qarshe tunda gaf su'adan take da kammala karatunta,tana zaton idan ta gama din zata nutsu ta tara hankalinta waje guda ta kula da mijinta kamar kowacce matar aure.
Yana tsaka da amsa waya ta shigo falon kai tsaye tare da sallamarta,a hankali ya daga kanshi don ganin waye,kansa ya kawai gefe yana jin kunyar ganinta a haka a matsayin surukarshi,baki daya babu al'adar bahaushe ko digi cikin jini da jijiyarta,komai nata na mai jan kunne ne,ko qanqanin bata jin kunyar keta gidan a haka,duk da tarin baqi dake gidan,yana yiwa yaronshi sha'awar sauyin rayuwa,duk abinda ke faruwa cikin rayuwar yaron shi da yakeso fiye da kowa cikin yaransa idan ka dauke amira yana sane,saidai baison jefa kanahi cikin sha'anin da ba'a nemi agaji ko tallafinsa,dattijon suruki ne wanda yasan ciwon kanshi da mutucinsa,amma tabbas mustapha ma cikin wani wadi daya cancanci a tallafeshi,tun fari laifinshi ne da bai ganin aibun rayuwar mai jan kunne,gani yake rayuwa ce ta burgewa,baisan babu komai cikinta face tsantsar wahala da rashin nutsuwa.
Cikin sheshsheqar kuka ta zube a gabansa
"Baabaa don Allah kayi masa fada,ka masa magana,yana son takurani,yana son tauyen 'yancina" sosai yake dubanta,a nutse yace
"Nutsu su'adah,zauna,zauna sosai,gayamin,me ya faru?,me ya hadaku" zama tayi gabansa tana goge hawayen nata da tissue,don ko dan mayafin da zata kama ta goge hawayen babu a jikinta
"Baabaa,mustapha ne,haka kawai muna zamanmu yadda muka saba,shekaran jiya yaje gidan hamza,ya gano wata zamantakewa ta daban yace dole muma irinta zamuyi,bayan zamantakewar tasu sam babu 'yanci ko walwala a cikinta,sai dinbim takura kai da rayuwa cikin duhu da rashin wayewa,lallai wai saidai na dawo nan qasar na zauna daku na qarasa karatuna don bai amince da duk qawaye na da abokaina ba,sannan wai idan na kammala na bishi dubai mu zauna tare na dinga kula da shi,don Allah baaba wannan ba takura bace,ni ban taba ganin inda da quruciyarki kike rayuwa irin haka ba,a gun africans kawai nake gani suma rashin wayewa ce da duhun kai" idanu baban ya runtse kafin ya bude,duka ta hadu ta zagesu su da iyayensy,babu shakka ba qaramin tasiri rayuwar yaro take ba a duk inda aka haifeshi ko ya taso,sai Allah ya taimaka iyaye sunyi tsaiwar daka sannan za'a samu yaro ya tashi da dabi'a halayya da al'adunshi.
Cup din ya dire dai dai sanda wayarshi tayi tsuwwa,ya duba yaga kiran daga baabaa ne,tun kafin ya daga ranshi ya raya masa mishkilar su'adah ce,daya daga din kuwa ce masa baabaan yayi
"Kana ina?,duk inda kake kazo ka sameni a falo,ina jiranka" daga maganar tasa kawai ya fahimci mawuyaci ne ba qararsa ta kai wajen baabaan ba,duk da cewa hakan ba baqon lamari bane wajensa,amma abun yayi masa ciwo fiye da kullum,ranshi bace ya maida wayar aljihunsa yana duban ummee
"Baabaa na kira" ya fadi a taqaice
"Ok,ka qoshi kenan coffee kawai ya isheka,bayanshi banga kaci komai ba?"
"I'm ok ummee" ya fadi yana takawa ya fice daga dakin.
Cikin sanyi da qasaita yayi sallama cikin falon baaban,wani kallo yajefa mata wanda ya sanyata sadda kanta qasa,take jikinta yayi sanyi,nadamar kawo qarar ta baibayeta,kwarjininsa kadai ya ladabtar da ita,cikin girmamawa ya isa gaban baaban ya zauna gami da lanqwashe qafafunsa,ajjiye takaddun hannayensa yayi sannan ya maida hankalinsa gareshi
"Mustapha,me ya shiga tsakaninka da matarka" shiru yayi na wasu daqiqu kanshi na qasa,idanunshi bisa carfet din dake dakin,a hankali ya motsa bakinsa
"Baabaa,ina da buqatar mata ta ne kawai kusa dani,na buqaci ta ajjiye karatunta ta zauna tare da ni" yasan a rina,mustaphan ba mai boyon abu bane cikin zuciya,komai tsaurin gaskiya ko dacinta sai ya fadeta,tabbas mustaphan bashi da laifi cikin maganarlaifinshi daya tun fari a haka ya tarbiyyanci matarsa,amma kowanne magidanci zaiso kasancewa da iyalinshi,bawai kowannansu da inda ya sanya kanshi ba sannan ace wai a haka za'a rayu,tausayinshi ya kama shi,yana jin wannan karon ya kamata yayi wani hobbasa cikin rayuwar yaron nashi
"Baka kyauta ba mustapha" maganar data sanyashi daga ido cikin mamaki ya tsare babaa da kallo,yayi zaton shine na farko da zai goya masa baya?,ya zaci shima yasan ba haka rayuwar ma'aurata take ba
"Tun farko haka ka dora bigiren rayuwarku kai da ita,ka manta ice tun yana danye ake tanqwarashi,basai ya bushe ba sannan kace zaka tanqwarashi" kai su'adah ke kadawa cike da jin dadi tare da alamun samun nasara cikin zancan baban ba tare data fuskanci dungun dake cikin maganar ba
"Mustapha,komai ya kusa qarewa,ka qyale matarka ta kammala karatunta a inda ta fara,shekara guda ya rage mata ta kammala,idan yaso koma meyw zai biyi baya sai ka zauna ku yanke" shiru ne ya ratsa falon,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi,zuciyar su'adah ciki fal da fatan samun nasara.
Bayajin a duniya akwai wani umarni da baban zai bashi ya tsallakeshi,ya numfasa a hankali sannan ya furta
"Na barta baabaa"
"Yes dad,thank you" sa'adah ta fada cikin daga murya,murmushi ya subucewa baabaan,addu'a yaje da fatan saisaituwar halayen su'adah ko kyakkyawar rayuwa zata samu ga diyansa,miqewa tayi cikin farinciki ta fice,fes taje jin ranta,don ta mustapha tana tunanin tasan yadda zata shawo kansa,don ko kadan bata jin zata iya tabbata cikin nijeria tayi rayuwa a cikinta.
Fitarta sukayi kacibus da su amira na niyyar shigowa,babu wanda ta kalla cikinsu tayi gaba abinta,yayin da eesha ta bita da harara kamar idanuwanta zai fado,babu wanda ta tsana a duniyarta sama da su'adah din,tana ganin baki daya ta kanainaye rayuwar mustapha,ta hanashi duban kowacce mace da qima,bayan ita din ba wata uwa take tsinanawa gareshi ba,abinda bata sani ba,abun a jininsa yake,tsaki ta ja wanda ya sanya amira waiwaya ta dubeta,tasan meke kai kawo a zuciyarta,saidai koma mene bata fatan Allah ya ida nufi,don qwaryar sama ke dukan ta qasa,banbancin ita da itan kadan ne.
Bayan sallama da tayi ganinsa shine abu na biyu daya biyo baya bayan shigowarta falon,nutsuwarta yaji na nemam gushewa
"Bafa mukhtar bane,ba kuma zai taba zama mukhtar ba" wannan shine kalaman sa suka dawo mata cikin kwanyarta,sai ta lumshe ido taja dogon numfashi kafin ta ajiye nunfashi ta kuma daidaita nutsuwarta.
Fuskarsa dauke da fara'a yake dubansu
"Mommies dina ne da kuma mai sunan uwar mumunai" ya furta cikin fara'a,su dinma fuskarsu washe take suka samu waje gefe da shi suka zauna,yayin da eesha tafi daura da mustapha,satar kallonshi take,baki daya man din ya sake tafiya da tunaninta,
"Allah ka mallakamin shi" ta fada cikin zuciyarta tana lumshe idanuwa tana ci gaba da satar kallonshi,wanda sam shi baisan ma tana yi ba,abinda ke gabansa kawai shi ya dameshi,gaisuwansun ma bai dago kai ba bare ya gane su waye ya amsa musu baki daya kudin goro,ba haka eesha taso ba,gaida baabaa sukayi baki daya ya amsa cikin fara'a
"Mutan kano,gaki ga mutuniyar dai,bata qyaleki ba,nan ta addabeni sai da na siya musu ticket ta taho" dariya suka dan saka baki dayansu.
"Wallahi kin maida ni wata iri amira,godiya nake"
"Afuwa namecy,afwa"ta qarasa ciki suna gaisawa da 'yammatan dake ciki,gira ta daga
" to ya zanyi da ke,ni na kai kaina inda ba'a damu da ni ba,muje kimin rakiya wajen baabaa"
"Ya kamata,don nima ina son inje in gaidashi" eesha dake shan tea ta ajjuye cup din tana yiwa sumayyan duban ita kuma a wa?,kamar zata furta sai kuma ta fasa,ta miqe itama tana yafa dan yalolon mayafi kan kayan baccinta tana cewa
"Muje nima nayi rakiya"
"Owk" amira ta fada ta dubi su hibba
"Oya,ku wuce ku tafi wasanku" juyawa sukayi hibba ta tsaya ta karbi abdallah suka wuce.
Sai da suka shiga wajen anty maamaa da ummee ta gaidasu sannan ta suka wuce zuwa sashen tsohon.
Zaune yake gefan umminsa daga shi sai itayana kurbar coffee,idan da kowa a gun ta tabbata bazai sha ba,wanda ta shiga kitchen da kanta ta hada masa,dubanshi take qasa qasa,ita daya take iya gane mustaphan,tayi tsammanin idan yayi aure shikenan komai ya qare,matarsa zata fahimceshi fiye da kowa,saidai kash,sabanin haka ne ya faru,matarsa itace wadda bata fahimceshi ba fiye da kowa,a yanzun kallo daya tayi masa ta fahimci yunwa yake ji,bazai iya gaya mata ba,zai iya ci gaba da zamansa haka har sai an bashi,idan ya gaji ya kuma yana iya fita can wani wajen cin abincin yaci abinshi,time to time yakan sanya matarsa tazo ta karba masa idan yunwar taci tura,hatta da amira tafi matarsa sanin ko shi waye,wani irin mutum ne shi mai wuyar sha'ani,ba kowa ke iya fahimtarsa ba,bai iya sharing damuwarsa ko shawararsa da kowa idan ka dauke ummeen da baabaansa,tayi zaton idan yayi aure wannan zai zama aikin matarsa,saidai ina ma yaga matar bare ta dauki wannan responsibility din,saidai komai tana ganin ya kusa zuwa qarshe tunda gaf su'adan take da kammala karatunta,tana zaton idan ta gama din zata nutsu ta tara hankalinta waje guda ta kula da mijinta kamar kowacce matar aure.
Yana tsaka da amsa waya ta shigo falon kai tsaye tare da sallamarta,a hankali ya daga kanshi don ganin waye,kansa ya kawai gefe yana jin kunyar ganinta a haka a matsayin surukarshi,baki daya babu al'adar bahaushe ko digi cikin jini da jijiyarta,komai nata na mai jan kunne ne,ko qanqanin bata jin kunyar keta gidan a haka,duk da tarin baqi dake gidan,yana yiwa yaronshi sha'awar sauyin rayuwa,duk abinda ke faruwa cikin rayuwar yaron shi da yakeso fiye da kowa cikin yaransa idan ka dauke amira yana sane,saidai baison jefa kanahi cikin sha'anin da ba'a nemi agaji ko tallafinsa,dattijon suruki ne wanda yasan ciwon kanshi da mutucinsa,amma tabbas mustapha ma cikin wani wadi daya cancanci a tallafeshi,tun fari laifinshi ne da bai ganin aibun rayuwar mai jan kunne,gani yake rayuwa ce ta burgewa,baisan babu komai cikinta face tsantsar wahala da rashin nutsuwa.
Cikin sheshsheqar kuka ta zube a gabansa
"Baabaa don Allah kayi masa fada,ka masa magana,yana son takurani,yana son tauyen 'yancina" sosai yake dubanta,a nutse yace
"Nutsu su'adah,zauna,zauna sosai,gayamin,me ya faru?,me ya hadaku" zama tayi gabansa tana goge hawayen nata da tissue,don ko dan mayafin da zata kama ta goge hawayen babu a jikinta
"Baabaa,mustapha ne,haka kawai muna zamanmu yadda muka saba,shekaran jiya yaje gidan hamza,ya gano wata zamantakewa ta daban yace dole muma irinta zamuyi,bayan zamantakewar tasu sam babu 'yanci ko walwala a cikinta,sai dinbim takura kai da rayuwa cikin duhu da rashin wayewa,lallai wai saidai na dawo nan qasar na zauna daku na qarasa karatuna don bai amince da duk qawaye na da abokaina ba,sannan wai idan na kammala na bishi dubai mu zauna tare na dinga kula da shi,don Allah baaba wannan ba takura bace,ni ban taba ganin inda da quruciyarki kike rayuwa irin haka ba,a gun africans kawai nake gani suma rashin wayewa ce da duhun kai" idanu baban ya runtse kafin ya bude,duka ta hadu ta zagesu su da iyayensy,babu shakka ba qaramin tasiri rayuwar yaro take ba a duk inda aka haifeshi ko ya taso,sai Allah ya taimaka iyaye sunyi tsaiwar daka sannan za'a samu yaro ya tashi da dabi'a halayya da al'adunshi.
Cup din ya dire dai dai sanda wayarshi tayi tsuwwa,ya duba yaga kiran daga baabaa ne,tun kafin ya daga ranshi ya raya masa mishkilar su'adah ce,daya daga din kuwa ce masa baabaan yayi
"Kana ina?,duk inda kake kazo ka sameni a falo,ina jiranka" daga maganar tasa kawai ya fahimci mawuyaci ne ba qararsa ta kai wajen baabaan ba,duk da cewa hakan ba baqon lamari bane wajensa,amma abun yayi masa ciwo fiye da kullum,ranshi bace ya maida wayar aljihunsa yana duban ummee
"Baabaa na kira" ya fadi a taqaice
"Ok,ka qoshi kenan coffee kawai ya isheka,bayanshi banga kaci komai ba?"
"I'm ok ummee" ya fadi yana takawa ya fice daga dakin.
Cikin sanyi da qasaita yayi sallama cikin falon baaban,wani kallo yajefa mata wanda ya sanyata sadda kanta qasa,take jikinta yayi sanyi,nadamar kawo qarar ta baibayeta,kwarjininsa kadai ya ladabtar da ita,cikin girmamawa ya isa gaban baaban ya zauna gami da lanqwashe qafafunsa,ajjiye takaddun hannayensa yayi sannan ya maida hankalinsa gareshi
"Mustapha,me ya shiga tsakaninka da matarka" shiru yayi na wasu daqiqu kanshi na qasa,idanunshi bisa carfet din dake dakin,a hankali ya motsa bakinsa
"Baabaa,ina da buqatar mata ta ne kawai kusa dani,na buqaci ta ajjiye karatunta ta zauna tare da ni" yasan a rina,mustaphan ba mai boyon abu bane cikin zuciya,komai tsaurin gaskiya ko dacinta sai ya fadeta,tabbas mustaphan bashi da laifi cikin maganarlaifinshi daya tun fari a haka ya tarbiyyanci matarsa,amma kowanne magidanci zaiso kasancewa da iyalinshi,bawai kowannansu da inda ya sanya kanshi ba sannan ace wai a haka za'a rayu,tausayinshi ya kama shi,yana jin wannan karon ya kamata yayi wani hobbasa cikin rayuwar yaron nashi
"Baka kyauta ba mustapha" maganar data sanyashi daga ido cikin mamaki ya tsare babaa da kallo,yayi zaton shine na farko da zai goya masa baya?,ya zaci shima yasan ba haka rayuwar ma'aurata take ba
"Tun farko haka ka dora bigiren rayuwarku kai da ita,ka manta ice tun yana danye ake tanqwarashi,basai ya bushe ba sannan kace zaka tanqwarashi" kai su'adah ke kadawa cike da jin dadi tare da alamun samun nasara cikin zancan baban ba tare data fuskanci dungun dake cikin maganar ba
"Mustapha,komai ya kusa qarewa,ka qyale matarka ta kammala karatunta a inda ta fara,shekara guda ya rage mata ta kammala,idan yaso koma meyw zai biyi baya sai ka zauna ku yanke" shiru ne ya ratsa falon,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi,zuciyar su'adah ciki fal da fatan samun nasara.
Bayajin a duniya akwai wani umarni da baban zai bashi ya tsallakeshi,ya numfasa a hankali sannan ya furta
"Na barta baabaa"
"Yes dad,thank you" sa'adah ta fada cikin daga murya,murmushi ya subucewa baabaan,addu'a yaje da fatan saisaituwar halayen su'adah ko kyakkyawar rayuwa zata samu ga diyansa,miqewa tayi cikin farinciki ta fice,fes taje jin ranta,don ta mustapha tana tunanin tasan yadda zata shawo kansa,don ko kadan bata jin zata iya tabbata cikin nijeria tayi rayuwa a cikinta.
Fitarta sukayi kacibus da su amira na niyyar shigowa,babu wanda ta kalla cikinsu tayi gaba abinta,yayin da eesha ta bita da harara kamar idanuwanta zai fado,babu wanda ta tsana a duniyarta sama da su'adah din,tana ganin baki daya ta kanainaye rayuwar mustapha,ta hanashi duban kowacce mace da qima,bayan ita din ba wata uwa take tsinanawa gareshi ba,abinda bata sani ba,abun a jininsa yake,tsaki ta ja wanda ya sanya amira waiwaya ta dubeta,tasan meke kai kawo a zuciyarta,saidai koma mene bata fatan Allah ya ida nufi,don qwaryar sama ke dukan ta qasa,banbancin ita da itan kadan ne.
Bayan sallama da tayi ganinsa shine abu na biyu daya biyo baya bayan shigowarta falon,nutsuwarta yaji na nemam gushewa
"Bafa mukhtar bane,ba kuma zai taba zama mukhtar ba" wannan shine kalaman sa suka dawo mata cikin kwanyarta,sai ta lumshe ido taja dogon numfashi kafin ta ajiye nunfashi ta kuma daidaita nutsuwarta.
Fuskarsa dauke da fara'a yake dubansu
"Mommies dina ne da kuma mai sunan uwar mumunai" ya furta cikin fara'a,su dinma fuskarsu washe take suka samu waje gefe da shi suka zauna,yayin da eesha tafi daura da mustapha,satar kallonshi take,baki daya man din ya sake tafiya da tunaninta,
"Allah ka mallakamin shi" ta fada cikin zuciyarta tana lumshe idanuwa tana ci gaba da satar kallonshi,wanda sam shi baisan ma tana yi ba,abinda ke gabansa kawai shi ya dameshi,gaisuwansun ma bai dago kai ba bare ya gane su waye ya amsa musu baki daya kudin goro,ba haka eesha taso ba,gaida baabaa sukayi baki daya ya amsa cikin fara'a
"Mutan kano,gaki ga mutuniyar dai,bata qyaleki ba,nan ta addabeni sai da na siya musu ticket ta taho" dariya suka dan saka baki dayansu.