Sashe 149
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummeen na zaune a falon tana karyawa,a hankali ta qarasa gabanta ta zube tana kwasar gaisuwa,ajjiye cup din ummen tayi tana dubanta,lokaci guda yarinyar ta soma burgeta,tana hango tsantsar nutsuwa hankali da tarbiyya irin na diyan bahaushen asali tattare da ita,zata iya cewa kaf DANGANTAKAR da suka taba da su'ad bata taba gani ta ko russuna ba wajen gaida daya daga cikinsu,gaisuwa take musu irin ta turawa,a tausashe cikin qauna ummeen ta masa kafin tace
"Na aika a kai muku abun kari,su kuma gyara sashen halan kunyi sabani ne"
"Eh ummi,amma na kammala gyaran sashen ma"
"Masha Allah" ummin ta fada cikin farinciki gane da sauyin da ya fara samuwa shiru ya biyo baya saboda ficewar mahmoud bayan ya gama tsokane tsokanenshi
"Kije ku gaisa da maamaa ko,idan kun gama ki hawo sama ina so muyi magana" a ladabce ta amsa mata kana ta miqe a nutse ta fice.
Bata jima wajen anty maman ba ta dawo,a darare ta haura saman,ta tura qofar dakin ta shiga bayan ta nemi izini wajen ummeen tayi mata,nuni tayi mata da gefanta inda take zaune gefan gado,a kunyace sannan a darare ta zauna,hannayenta baki daya ummee ta kamo cikin nata
"Ki saki jikinki amiran umman khalipha,ki daukeni kamar mamanki kamar yadda na daukeki tamkar tawa amiran" kai ta gyada alamun to
"Ina fata jiyan kin min alfarmar dana roqa wajenki ko?" Ta jefo mata tambayar,nauyi ya saukar mata,ta yayq zata gaya mata baici abincin ba sabida abinda ya faru a sashen nasu?sai data gama karantarta sannan tace
"Kada ki damu,na tabbata jiya akwai abinda ya faru mara dadi a bangarenku,tunda yau naga ya fice ba tare da yazi gurina ba,yakan yi hakanne matuqar akwai matsala,baya son yazo naga damuwa kan fuskarshi bare hakan ya shafi tawa walwalar......sumayya"
"Na'am ummee" ta amsa kanta a qasa
"Ta iya yiwuwa baki son almustapha,ta iya yiwuwa bai miki ba,ni da baabaanshi duka shaidane biyayya ce ta hadaku kuke zaune,ban sani ba ko zan iya neman wata alfarma wajenki"
"Ummee ki fadi ko meye,in sha Allah ni mai biyayya ce a gareki" ajiyar zuciya ta saki
"Sumayya,ina son don Allah don annabi ki dauka min alqwarin bawa almustapha dukkan wata kulawa da macen qwarai ke baiwa mijinta,ki taimaka ki zama sikar dawowar walwala da jim dadinsa,rashin kyakkyawar zamantakewar auren mustapha ta jima tana cimin rai,ba tonon asiri ba sam almustapha baisan dadin aure ba,bashi da abun fada game da aure tsawon shekarun daya kwashe,yana da buqatar samun wata mace a gefansa,macen data kasance ba uwa bace,macen da zata karbi sunan abokiyar rayuwa mai tallafar damuwa farinciki nasara dama asara,macen da zqi jingina da ita ya sauke damuwarsa,macan da zata iya daukar role na mahaifiya a bigiren da mahaifiyar tayi nisa ko babu ita,macen da zata kasance ko yaushe daura da shi,zaki iya zama dukkan wadan nan abubuwa a rayuwar mustapha?,zaki iya min wannan alfarmar wadda ni ban isa na yiwa rayuwar tasa ba?,zaki taimaka wajen gyaran rayuwarshi kamar yadda baabaa ya taba roqa daga gareki?" Nauyi kunya da tausayin ummeen suka dabaibayeta,babu shakka kowacce uwa tana qaunar danta,tana buri da fatan ingantuwar rayuwarsa,don me ba zata yiwa wadan nan mutane masu karamcin wannan karamcin ba?
"Nayi miki ummee nayi in sha Allah,saidai ki yimin afuwa aduk sanda aka samu gazawa kan hakan" madaukakin farinciki ya kama zuciyar ummeen,lallausan murmushi shinfide kan fuskarta tace
"Ina roqon ubangiji ya albarakaci gabaki da bayanki,damaki da hagunki,samanki da qasanki,ya faranta miki yadda kika saka farinciki a zuciyata,kike kuma da burin sakawa a nan gaba cikin ruhin daana,ba shakka bana zaton za'a samu kasawa,zan tsaya miki sumayya da dukkan tsayawa wadda ta dace suruka tayi cikin rayuwar surukuwarta,na gaya miki waye mijinki almistapha?,me ye tsarin rayuwarsa?,me yafi so me kuma yafi qi?" Kunya ta dabaibaye sumayya,tayi qas da kanta tana murmushi,haqiqa bata taba cin karo da uwar miji ba a tarihin rayuwar aurenta irin ummen
"Daina kunyata,ni uwace amira,ni da nake tsammatar zuwanki gareni neman shawara idan abu ya shige miki duhu"murmushi ta sake saki kawai ba tare da tace komai ba,a hankalu ta dinga gaya mata ra'a yoyin almustaphan,wasu su bata mamaki,wasu taji sunyi mata tsauri,sannan ta rufe da cewa
"ina fata zaki rufe tarihin kaiwa mijinku abinci a duk sanda yake qasar nan,kamar yadda duk lokacin da adam ke gari babu wanda ke aikawa da abinci sashinsa"
"In sha Allah ummee"
"Da kyau,saiki fara daga yau,duk da nasan cewa mawuyacine yadda ranshi ke bacan nan idan bai tsiri komawa dubai ba a gobe,a duk sanda hakan ta hadashi da ita yakan dauki wannan mataki me don ragewa kansa bacin rai,saboda bashi da wani abu da zai iya kawar masa da wannan bacin rai a ganinsa sai nisantar inda ran mashi ya baci,tun yana qarami haka yake,rashin tsayyar mace kusa da shi ya zame masa al'ada,ina kuma fatan nan da lokaci kadan zaki maida wannan al'adar tasa ta zama tarihi,kada ki damu,sannan kada ki hanashi,hakan ma wata dama ce da zaki sake bitar halayensa da shirya yadda zaki bullo"
"To ummee"
"Allah yayi miki albarka" ranta qal take amsawa,tana jin cikim zuciya da gangar jikinta wani muhimmin taimako da sadaukarwa zata yi,karo na biyu a rayuwarta tun bayan barinta gidan lukman
(Gareku iyayenmu mata,wallahi na qaramin lamari banr roqawa yaronki mace ta gari cikin addu'arki tun yana qaraminsa,MACEN JARABA ba qaramin hatsari bace cikin rayuwar d'aa namiji,babu babban dacewa da jin dadin rayuwa ga namiji irin samun MACE TA GARI,manzan Allah S A W yana cewa mafi jin dadin duniya shine mace ta gari,rayuwarshi zata iya tarwatsewa ya rasa walwala har ya koma ga Allah a dalilin rashin mace ta gari,Allah kasa mu dace,ka hada 'ya'yanmu,'yan uwanmu,iyayenmu qannenmu yayyenmu mazajenmu da mata na gari).
Kusan yadda ta dawo qasar bada sanin kowa ba a gidan haka ta hada kayanta ta nufi airphort da zummar komawa america,tana jin wannan karo duk son da takewa muhammad almustapha zata yakiceshi gefe ta hukuntashi,ta azabtar da zuciyarsa ta hanyar yin nesa da shi da hana shi ganinta,sai ta rama ninkin wulaqancin da yayi mata.
Wannan kenan.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
7⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*RANAR DA WASU FUSKOKI ZASUYI HASKE,WASU FUSKOKI KUMA SUYI BAQI(RANAR QIYAMA)*
___________________________________
sai la'asar sannan sumayyan ta koma bangarenta,sosai taji dadin zama wajen,sunyi hira mai muhimmanci da ummee,wanda tun tana jin kunya da d'ari d'ari har ta soma sakin jiki,ta sake qwarai cikin ma'aikatan gidan,wucewa tayi bangarenta tana tunanin me zata tanadar masa,kasancewar baison cin abun mai nauyi da daddare,yayin da itama ummee ta shiga tata sabgar tana tunanin yadda zata bullowa mustaphan matuqar ya tada maganar tafiya dubai,wanda tasan mawuyacine bai ambaceta ba.
Qarfe takwas na dare da mintuna ashirin ya tako cikin falon wanda babu motsin kowa sai na na'urori da kuma hasken qwayaye,samanshi ya nufa kai tsaye yana furzar da hucin iska daga bakinsa,shi daya yake tuno gamonsa da su'ad lamarin na sake bata ranshi,ya tabbatar da cewa ta tafin kamar yadda ta fadi,hakanan shima yana kan nashi qudurin na baiga abinda zai sanya shi nemanta ba koda zasu shekara dubu a haka,turus ya danyi yana mamakin yadda dakin ya dawo hayyacinshi bayan yasan me gayaran dakinshi baya nan,don bai gaya mishi zuwanshi abuja ba,da yake idan ba kowa a sashin sallamarsu yake har sai randa suka zo,a hankali tamkar mai ciwon qafa yake takawa yana duban yadda komai ya zama neat kamar ba'a yi waccar barnar ba ciki,a haka har yaqarasa bakin gado ya soma fidda kayan jikinsa yana mamakin wanda ya aikata hakan,bandaki ya shige yana niyyar hada ruwan wanka,tsayawa yayi cike da shakku yana tunani ta ina aka samu ruwan wanka haka?,mai dumi da qamshi,cikin kokwanto ya sanya hannunshi cikin ruwan,anya ba jinnu ke neman yi masa wasa da hankali ba,take sha'awar yin wankan ta sake kamashi,saboda ruwan yayi masa dai dai irin yadda yake so,bai bata lokaci ba kuwa ya shige kwamin wankan abunshi,ya kwanta luf a ciki gajiya na warwarewa daga jikinsa yana zaton anya ba ummee bace tayi masa duka wannan hidiman,yasani cewa ita kadai duk duniya tafi kowa sanin abunda yake so,saidai a iya sanshi ummen bata taba takowa sashen nasu ba,a hankali zuciyarsa ta shiga masa tariyar awannin da suka shude dazu,sanda ya cimmata tana tattare kwalaben dakin,anya ba ita tayi wannan aikin ba
"Ba ita bace,me zata iya wannan,bai tunanin tana da fikirar da zata iya duka wannan aikin,ita dinma bata ma yi masa kwata kwata kalar masu kuzari a jikinsu da zasu iya wannan aikin ba daga safe zuwa yanzu(nace lol saboda baka saba gani cikin gidanka ba)" hannunshi ya daga ya kalla inda yankan yake yana kallo,har yanzu wajen jazur yake abinka da farar fata,yayi mamakin yadda wajen ya kame haka da wuri,sannan zugin ya ragu sosai,ya tuna yadda tayi masa treating hannun,bai taba dauka ana irin hakan ba a gaske,yasan dai a fina finai hakan na faruwa,ko kuma ga matan turawa wa mazajensu ko samarinsu,tunanin ya dauka ya ajiye gefe,yana da buqatar barin qasar nan a gobe ko zai samu nutsuwar zuciya,yana jin bai da wani abunyi a cikinta,wannan tunanin ya sanyashi miqewa daga cikin ruwan wankan ba don ya gama awannin da ya sabayi ciki ba,ya saba kunfa ya qarasa wanke jikinsa ya daura towel ya fito.
Bakin madubinsa ya tsaya da niyyar yin shafa,sai a sannan ya lura madubin nashi ya koma babu komai a kai saboda haukar daya fuskanta a daren jiya,wani mugun tsaki ya ja,yana sake jin zafinta da haushinta,tana kuma sake fice masa a ka,wani dan abu ya danna gefan gadonsa ya janyo wata qaramar locker,take dukkan wasu kayan shafe shafensa suka bayyana,ya kwasosu ya watsa saman madubin yana dauka daya da daya yana amfani da kowanne a muhallinshi,bayan ya kammala ya fitar da qananun kaya ya saka sanann ya sanya takalmi wanda ya dace da kayan.
"Na aika a kai muku abun kari,su kuma gyara sashen halan kunyi sabani ne"
"Eh ummi,amma na kammala gyaran sashen ma"
"Masha Allah" ummin ta fada cikin farinciki gane da sauyin da ya fara samuwa shiru ya biyo baya saboda ficewar mahmoud bayan ya gama tsokane tsokanenshi
"Kije ku gaisa da maamaa ko,idan kun gama ki hawo sama ina so muyi magana" a ladabce ta amsa mata kana ta miqe a nutse ta fice.
Bata jima wajen anty maman ba ta dawo,a darare ta haura saman,ta tura qofar dakin ta shiga bayan ta nemi izini wajen ummeen tayi mata,nuni tayi mata da gefanta inda take zaune gefan gado,a kunyace sannan a darare ta zauna,hannayenta baki daya ummee ta kamo cikin nata
"Ki saki jikinki amiran umman khalipha,ki daukeni kamar mamanki kamar yadda na daukeki tamkar tawa amiran" kai ta gyada alamun to
"Ina fata jiyan kin min alfarmar dana roqa wajenki ko?" Ta jefo mata tambayar,nauyi ya saukar mata,ta yayq zata gaya mata baici abincin ba sabida abinda ya faru a sashen nasu?sai data gama karantarta sannan tace
"Kada ki damu,na tabbata jiya akwai abinda ya faru mara dadi a bangarenku,tunda yau naga ya fice ba tare da yazi gurina ba,yakan yi hakanne matuqar akwai matsala,baya son yazo naga damuwa kan fuskarshi bare hakan ya shafi tawa walwalar......sumayya"
"Na'am ummee" ta amsa kanta a qasa
"Ta iya yiwuwa baki son almustapha,ta iya yiwuwa bai miki ba,ni da baabaanshi duka shaidane biyayya ce ta hadaku kuke zaune,ban sani ba ko zan iya neman wata alfarma wajenki"
"Ummee ki fadi ko meye,in sha Allah ni mai biyayya ce a gareki" ajiyar zuciya ta saki
"Sumayya,ina son don Allah don annabi ki dauka min alqwarin bawa almustapha dukkan wata kulawa da macen qwarai ke baiwa mijinta,ki taimaka ki zama sikar dawowar walwala da jim dadinsa,rashin kyakkyawar zamantakewar auren mustapha ta jima tana cimin rai,ba tonon asiri ba sam almustapha baisan dadin aure ba,bashi da abun fada game da aure tsawon shekarun daya kwashe,yana da buqatar samun wata mace a gefansa,macen data kasance ba uwa bace,macen da zata karbi sunan abokiyar rayuwa mai tallafar damuwa farinciki nasara dama asara,macen da zqi jingina da ita ya sauke damuwarsa,macan da zata iya daukar role na mahaifiya a bigiren da mahaifiyar tayi nisa ko babu ita,macen da zata kasance ko yaushe daura da shi,zaki iya zama dukkan wadan nan abubuwa a rayuwar mustapha?,zaki iya min wannan alfarmar wadda ni ban isa na yiwa rayuwar tasa ba?,zaki taimaka wajen gyaran rayuwarshi kamar yadda baabaa ya taba roqa daga gareki?" Nauyi kunya da tausayin ummeen suka dabaibayeta,babu shakka kowacce uwa tana qaunar danta,tana buri da fatan ingantuwar rayuwarsa,don me ba zata yiwa wadan nan mutane masu karamcin wannan karamcin ba?
"Nayi miki ummee nayi in sha Allah,saidai ki yimin afuwa aduk sanda aka samu gazawa kan hakan" madaukakin farinciki ya kama zuciyar ummeen,lallausan murmushi shinfide kan fuskarta tace
"Ina roqon ubangiji ya albarakaci gabaki da bayanki,damaki da hagunki,samanki da qasanki,ya faranta miki yadda kika saka farinciki a zuciyata,kike kuma da burin sakawa a nan gaba cikin ruhin daana,ba shakka bana zaton za'a samu kasawa,zan tsaya miki sumayya da dukkan tsayawa wadda ta dace suruka tayi cikin rayuwar surukuwarta,na gaya miki waye mijinki almistapha?,me ye tsarin rayuwarsa?,me yafi so me kuma yafi qi?" Kunya ta dabaibaye sumayya,tayi qas da kanta tana murmushi,haqiqa bata taba cin karo da uwar miji ba a tarihin rayuwar aurenta irin ummen
"Daina kunyata,ni uwace amira,ni da nake tsammatar zuwanki gareni neman shawara idan abu ya shige miki duhu"murmushi ta sake saki kawai ba tare da tace komai ba,a hankalu ta dinga gaya mata ra'a yoyin almustaphan,wasu su bata mamaki,wasu taji sunyi mata tsauri,sannan ta rufe da cewa
"ina fata zaki rufe tarihin kaiwa mijinku abinci a duk sanda yake qasar nan,kamar yadda duk lokacin da adam ke gari babu wanda ke aikawa da abinci sashinsa"
"In sha Allah ummee"
"Da kyau,saiki fara daga yau,duk da nasan cewa mawuyacine yadda ranshi ke bacan nan idan bai tsiri komawa dubai ba a gobe,a duk sanda hakan ta hadashi da ita yakan dauki wannan mataki me don ragewa kansa bacin rai,saboda bashi da wani abu da zai iya kawar masa da wannan bacin rai a ganinsa sai nisantar inda ran mashi ya baci,tun yana qarami haka yake,rashin tsayyar mace kusa da shi ya zame masa al'ada,ina kuma fatan nan da lokaci kadan zaki maida wannan al'adar tasa ta zama tarihi,kada ki damu,sannan kada ki hanashi,hakan ma wata dama ce da zaki sake bitar halayensa da shirya yadda zaki bullo"
"To ummee"
"Allah yayi miki albarka" ranta qal take amsawa,tana jin cikim zuciya da gangar jikinta wani muhimmin taimako da sadaukarwa zata yi,karo na biyu a rayuwarta tun bayan barinta gidan lukman
(Gareku iyayenmu mata,wallahi na qaramin lamari banr roqawa yaronki mace ta gari cikin addu'arki tun yana qaraminsa,MACEN JARABA ba qaramin hatsari bace cikin rayuwar d'aa namiji,babu babban dacewa da jin dadin rayuwa ga namiji irin samun MACE TA GARI,manzan Allah S A W yana cewa mafi jin dadin duniya shine mace ta gari,rayuwarshi zata iya tarwatsewa ya rasa walwala har ya koma ga Allah a dalilin rashin mace ta gari,Allah kasa mu dace,ka hada 'ya'yanmu,'yan uwanmu,iyayenmu qannenmu yayyenmu mazajenmu da mata na gari).
Kusan yadda ta dawo qasar bada sanin kowa ba a gidan haka ta hada kayanta ta nufi airphort da zummar komawa america,tana jin wannan karo duk son da takewa muhammad almustapha zata yakiceshi gefe ta hukuntashi,ta azabtar da zuciyarsa ta hanyar yin nesa da shi da hana shi ganinta,sai ta rama ninkin wulaqancin da yayi mata.
Wannan kenan.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
7⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*RANAR DA WASU FUSKOKI ZASUYI HASKE,WASU FUSKOKI KUMA SUYI BAQI(RANAR QIYAMA)*
___________________________________
sai la'asar sannan sumayyan ta koma bangarenta,sosai taji dadin zama wajen,sunyi hira mai muhimmanci da ummee,wanda tun tana jin kunya da d'ari d'ari har ta soma sakin jiki,ta sake qwarai cikin ma'aikatan gidan,wucewa tayi bangarenta tana tunanin me zata tanadar masa,kasancewar baison cin abun mai nauyi da daddare,yayin da itama ummee ta shiga tata sabgar tana tunanin yadda zata bullowa mustaphan matuqar ya tada maganar tafiya dubai,wanda tasan mawuyacine bai ambaceta ba.
Qarfe takwas na dare da mintuna ashirin ya tako cikin falon wanda babu motsin kowa sai na na'urori da kuma hasken qwayaye,samanshi ya nufa kai tsaye yana furzar da hucin iska daga bakinsa,shi daya yake tuno gamonsa da su'ad lamarin na sake bata ranshi,ya tabbatar da cewa ta tafin kamar yadda ta fadi,hakanan shima yana kan nashi qudurin na baiga abinda zai sanya shi nemanta ba koda zasu shekara dubu a haka,turus ya danyi yana mamakin yadda dakin ya dawo hayyacinshi bayan yasan me gayaran dakinshi baya nan,don bai gaya mishi zuwanshi abuja ba,da yake idan ba kowa a sashin sallamarsu yake har sai randa suka zo,a hankali tamkar mai ciwon qafa yake takawa yana duban yadda komai ya zama neat kamar ba'a yi waccar barnar ba ciki,a haka har yaqarasa bakin gado ya soma fidda kayan jikinsa yana mamakin wanda ya aikata hakan,bandaki ya shige yana niyyar hada ruwan wanka,tsayawa yayi cike da shakku yana tunani ta ina aka samu ruwan wanka haka?,mai dumi da qamshi,cikin kokwanto ya sanya hannunshi cikin ruwan,anya ba jinnu ke neman yi masa wasa da hankali ba,take sha'awar yin wankan ta sake kamashi,saboda ruwan yayi masa dai dai irin yadda yake so,bai bata lokaci ba kuwa ya shige kwamin wankan abunshi,ya kwanta luf a ciki gajiya na warwarewa daga jikinsa yana zaton anya ba ummee bace tayi masa duka wannan hidiman,yasani cewa ita kadai duk duniya tafi kowa sanin abunda yake so,saidai a iya sanshi ummen bata taba takowa sashen nasu ba,a hankali zuciyarsa ta shiga masa tariyar awannin da suka shude dazu,sanda ya cimmata tana tattare kwalaben dakin,anya ba ita tayi wannan aikin ba
"Ba ita bace,me zata iya wannan,bai tunanin tana da fikirar da zata iya duka wannan aikin,ita dinma bata ma yi masa kwata kwata kalar masu kuzari a jikinsu da zasu iya wannan aikin ba daga safe zuwa yanzu(nace lol saboda baka saba gani cikin gidanka ba)" hannunshi ya daga ya kalla inda yankan yake yana kallo,har yanzu wajen jazur yake abinka da farar fata,yayi mamakin yadda wajen ya kame haka da wuri,sannan zugin ya ragu sosai,ya tuna yadda tayi masa treating hannun,bai taba dauka ana irin hakan ba a gaske,yasan dai a fina finai hakan na faruwa,ko kuma ga matan turawa wa mazajensu ko samarinsu,tunanin ya dauka ya ajiye gefe,yana da buqatar barin qasar nan a gobe ko zai samu nutsuwar zuciya,yana jin bai da wani abunyi a cikinta,wannan tunanin ya sanyashi miqewa daga cikin ruwan wankan ba don ya gama awannin da ya sabayi ciki ba,ya saba kunfa ya qarasa wanke jikinsa ya daura towel ya fito.
Bakin madubinsa ya tsaya da niyyar yin shafa,sai a sannan ya lura madubin nashi ya koma babu komai a kai saboda haukar daya fuskanta a daren jiya,wani mugun tsaki ya ja,yana sake jin zafinta da haushinta,tana kuma sake fice masa a ka,wani dan abu ya danna gefan gadonsa ya janyo wata qaramar locker,take dukkan wasu kayan shafe shafensa suka bayyana,ya kwasosu ya watsa saman madubin yana dauka daya da daya yana amfani da kowanne a muhallinshi,bayan ya kammala ya fitar da qananun kaya ya saka sanann ya sanya takalmi wanda ya dace da kayan.