Sashe 25
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sau da dama idan saqonni da kiran ZAINAB ya ishi mukhtar yakan zauna yayita sababi,sai ta sa baki da haqurqurtar da shi,wani lokaci kuma ta zolayeshi shi kuma ya bita da harara,ko ya ranqwashi kanta,a haka lamarin yaci gaba da wanzuwa har tsawon watanni uku cur babu sassauci haka na babu sauyi.
*Wace ce zainab?*
Zainab haifaffiyar garin kano wadda ke zaune cikin unguwar sheshe,suna da rufin asiri dai dai gwargwado,gida ne wanda ya kasance ya samu rarrabuwar kai da sabanin mabanbantan ra'ayi ga jama'ar gidan,maman zainab itace amarya a cikin gidan yayin da zainab ta kasance 'yarta ta uku baya ga maza biyu da ta biyo,mama amarya mahaifiyar zainab ta zamewa mata biyu data tarar cikin gidan qarfen qafa,babu wanda ke da fada a ji cikin gidan sai ita,ita ke juya kowa ciki harda mai gidan,taci karenta babu babbaka har zuwa lokacin da Allah ya yiwa mai gidan rasuwa aka raba musu gado kowa ya kama gabanshi,koda zainab tayi auren fari mama amarya ba irin mijin da take so zainab din ta aura ba kenan,miji take so ta samu koda ba mai kudi ba amma yana da abun hannunsa,wanda zasu maqale suyita tatsarsa suna tara abun duniya,talaka ne bashir futuk,qarfin soyayyar da zainab din ke masa ya rufe mata idanu har ta aureshi,tayi aurenta ne bayan data kammala kataratun ta na NCE a federal college of education kano wato FCE,kusan zamu iya cewa bashir abokin karatunta ne tare suke daukan lactures course dinsu daya,bayan kammala karatu kuma aiki bai samu ba,sai shagon wani maqocinsu dake kasuwa yake zuwa yana masa jira ana biyansa.
Duk iya yadda mama amaryan taso ta fahimtar da zainab din taqi fahimta,duk da kusan cewa babu abinda ta baro na daga halayen uwarta,bata cimma nasara ba sai bayan da akayi auren,sukaci soyayyarsu suka cinye,a lokacin da gishiri ya fara fita daga kan kaza ne zainab din ta fahimci bashir bai dace da ita ba,daya bayan daya ta dinga bin sawun duk wata dabi'a da huduba da uwar ke azata kai.
Cikin watanni biyar kacal suka balle auren,a lokacin tana dauke da ciki na watanni uku,duk yadda suja zo zubar da cikin abin ya gagara,a cewar mama amaryan baya da wani amfani tunda ubansa bai mallaki komai ba bare su saka ran samun wani alfanu tattare da shi.
Saidai kuma ina,maqaginsa ya riga ya QADDARA sai ya taka doron qasa,bayan wata bakwai ta haife yaronta namiji,ko yayeshi bata yi ba ta soma balle zawarci mai lasisi,a lokacin ta sake haduwa da qawaye kala kala idanunta suka bude,tasan duniya sosai har fiye da yadda uwarta ta sani ta koma dorata akai,hakan ya so tsorata maman har ta soma shirin hanata wasu abubuwan,amma ina.......maqeri ya riga mabada hali,tuni zainab din tasa aka rufe bakin maman da yayyenta maza biyu,duk wani abu da zata aiwatar bata laifi a idanunsu,musamman idan ta samo ta yaga musu.
Tun randa taga mukhtar zuciyarta ta yaba da shi,bata bata lokaci ba wajen bada sunanshi aka mata bincike a kansa,yadda takeso haka sakamakon yazo mata,mukhtar din yayi dai dai da ra'ayinta,saidai bata qaunar kishiya ko misqala zarratin,amma da ta samu labarin wace sumayya sai hankalinta ya kwanta,ta tabbatar ba matsala bace a gunta,aiki guda daya tak zata mata rana guda ta koreta daga gidan,duk da tana diyar malamai ai bata da maganin kirsa ko?.
*** *** ****
Hankalinta bai kwanta ba sai data gana da yaya yahanasu,wadda bata tunkareta ba sai data yi shiri sosai akanta,qwarai yaya yahansun taji wata qauna da aminta wa zainab,musamman data ji cewa ta taba haihuwar d'a namiji ma,nan zainab din ta zube mata alkhairai masu tarin yawa tare da tsara yadda zasu cimma nukhtar din duk da taimakon yaua yahansu wadda ke kiran kanta YAAYA kuma UWA a gunsa.
*** *** ***
Suna shirin cin abincin dare kiran yaya yahanasun ya baqunci wayarsa,dama ya tsammaci hakan saboda tun yammacin jiya da ya ziyarci gidan yaga gilmawar wata cikin layin nasu tamkar zainab din,zuciyarsa bata gasgata masa hakan ba tunda ya riga da ya sani bata san muhallinsu ba,amma duk da haka zuciyarsa bata samu nutsuwa ba har zuwa wannan lokaci.
"Kiyi haquri yaya,amma yanzu bazan samu damar fitowa ba" ya sanar da ita kai tsaye.
"La'ilaha illallahu,mukhtar yaushe kayi wannan riqar,akwai ranar dama da zata zo zan buqaci ganinka kaqi mukhtar" sai ta sa kuka
"Lallai ba shakka sumayya ta gama da mu,taci galaba akanmu ta sake cutar min da d'an uwa" sam baya son yaji kukan nata kamar yadda zuciyarsa ke quna idan yaji tana zagi aibata ko zargin sunayyarsa,hakan ya sanya ya amsa mata kan cewa yaba zuwa.
Wayar ya sauke yana duban sumayya
"Sumayya bana son fitar nan,ina zargin wani abu"ya fada idanunsa na sauya launi da alamun ransa ya fara motsuwa,kai ta kada
"Ka zargi alkhairi ya mukhtar,tunda kasan koma mene yaya jininka ba zata taba cutarka tana sane ba ko?" Shiru ya danyi sannan yace
"Na sani,amma matuqar abinda nake zaegi taje shirin aiwatarwa wannan karon wallahil azim sunayya ba zata kwashe mana da dadi ba,bazan yarda a ringa walagigi da rayuwarmu" duk da cewa a dunqule yayi maganar amma sai data haifar mata da matsanancin faduwar gaba wanda ta sanya har ta kasa tankawa, ya miqe ya shiga dakinsa ya dauki hularsa ya zura da muqullin babur dinsa don ya riga da ya ajjiye motarsa a inda take kwana ya fice daga gidan.
Kan kujera ta koma ta kwanta rigingine gabanta na ci gaba da lugude,a hankali ta dinga ambaton
"Ya rabbi yassir wala ta'asir" sabida neman gudun mawa da daukin wajen ubangiji.
Cikin falonta ya taddata wanda tun kafin ya kai ga shiga ya dinga jiyo dariya da hirarsu ita da yaran da alama cikin nishadi suke da walwala,sallamarsa ya katse hirar tasu,da daya da daya suka fice a dakin ya zama daga shi sai yaya yahanasun.
Suna kan gaisawa jamila ta shigo da jug guda biyu ruwa da lemo da kofuna ta dire masa,ya dauke kai ya dubi yaya yahansun yace
"Gani" sai ta dan murmusa
"Haba muntari,sai kace wanda ake gutsura,ko ruwa ai ka sha ko?" Sai yaga rashin dacewar yadda yazo matan,ko babu komai tsakaninsu ta bashi shekaru,saboda haka ya rusuna ya tsiyayi ruwan yayi kurba daya ya ajjiye kofin.
*** *** ***
Tana jin qarar babur dinsa ta miqe da hanzarinta,har ya shigo da shi ya kulle gidan ya qaraso falon tana tsaye,sam hankalinta ya gaza kwanciya a haka ya sameta a tsayen.
Saidai yanayin da taga fuskarsa ya zabge kaso mafi yawa na tashin hankalin da ta shiga,har ta saki bayyananniyar ajiyar zuciya ba tare da ta sani ba,'yar qaramar dariya ya saki yana fadin
"Me ya tsorataki haka?" Qwayar idanunta ta juya
"Kaine mana,hankalina ya qi kwanciya tunda ka fita"
"To ya kwanta,don babu komai sai alkhairi" duk da bata ji farinciki ko kadan ba yadda ta tsammata sai tace
"To Allah ya lamunce ya shige mana gaba" tayi maganar tana zama.
Ko kadan baiyi mata maganar komai ba,babu abinda yace mata kan hakan har bayan kwana biyu,a tsarinta mutum ce da bata shishshigi cikin lamuran da suka shafi rayuwar wani,hakanan ko da ga mukhtar din ne bata tambayarsa wasu lamura nashi na daban saidai idan shi yaga dama don rad'in kansa ya sanar mata,hakan ya sanya itama bata tambayeshi ba sai tayi zaton wani lamari ne da ya shafesu shi da 'yar uwar tasa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣3⃣
________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa'asa an takrahu shai'an wa huwa khairul lakum,wa'asa an tuhibbu shai'an wa huwa sharrul lakum,wallahu ya'alamu wa'antum la ta'alamu*
*Allahumma farrij hammal mahmumin,Allahumm farrij karbal makrubin*
_______________________________
*Bayan kwanaki biyu*
*** *** *** ***
a hankali ta shigo dakin ganin tunda ya kammala wanka ya shiga bai fito ba bayan ta kammala shirya abincin dare sa zasu ci,turus ta tsaya tana dubansa.
Tsaye yake gaban mudubi sanye da sabuwar shaddarsa ruwan qwaiduwar qwai dinkin boda,taje sumar kansa yake,sosai kayan suka masa kyau,sai ta jingina da bango ta harde hannayenta tana dubansa,da alama ma baisan ta shigo ba.
"Da kyau,irin wannan kwalliya haka da akemin?" Juyowa yayi ya dubeta yana murmushi
"Girmanki ne ai,amma zan danje unguwa tukunna" sai ta danyi jim gabanta na faduwa,take ranta ya darsa mata wani abu,batasan sanda bakinta ya subuce ba
"Zance zaka kenan" juyowa ya sakeyi yana ajjuye cumb din tare da takowa gabanta
"Ya akayi kika canka?,naso ace da kaina na gaya miki my sumy" wani irin abu taji yana ratsata tun daga kanta har qafafunta,yanayin fuskarta ya sauya
"Wai don Allah da gaske kake ko wasa?"
"Da gaske nake mana sumayya,na taba miki irin wannan wasan" ya fada yana qoqarin janyota jikinsa,sai ta zame jikin ta kana ta ja da baya,jikinta ya soma rawa hawaye na shirin zubo mata,hakan ya sanya ta tallafi kanta ta hanyar zama gefan gado,baiyi qasa a gwiwa ba ya bita ya zauna gefanta
"Yi a hankali mana sumayya,me na daga hankali kuma,koma wace zata zo ai kema kinsan a bayanki take ko?" Idanunta ta dago wadanda suka cika da qwalla har sun fara gangarowa ta dubeshi
"Meye na tada hankali kuma,shin ban cancanci nayi kishinka bane ya mukhtar?"
"Kin cancanci fiye da haka ma sumayya,amma kiyi haquri,in sha Allahu ina saka ran wannan karon alkhairi ne auren da zanyi".
Cike da mamaki ta watsa masa wani kallon
" wanne alkhairi ya mukhtar?,har ka manta wuyar da mukaci cikin shekara guda kacal?....."
"No....ki kyautata zato sumayya ba haka na sanki ba....", qarar wayar sa ce ta katse abinda yake shirin gaya mata,ya sanya hannu ya daga wayar bayan ya hade fuska kamar yana gaban mai kiran
" nace miki gani nan ko?"daga haka ya datse kiran ya maida hankalinsa kanta.
Hannu ya sanya ya share mata hawayen sannan ya miqe
"Ki bari na dawo zamuyi magana,ki kwantar da hankalinki sumayya kinji" bata iya amsa masa ba har ya sanya hularsa ya fice.
*Wace ce zainab?*
Zainab haifaffiyar garin kano wadda ke zaune cikin unguwar sheshe,suna da rufin asiri dai dai gwargwado,gida ne wanda ya kasance ya samu rarrabuwar kai da sabanin mabanbantan ra'ayi ga jama'ar gidan,maman zainab itace amarya a cikin gidan yayin da zainab ta kasance 'yarta ta uku baya ga maza biyu da ta biyo,mama amarya mahaifiyar zainab ta zamewa mata biyu data tarar cikin gidan qarfen qafa,babu wanda ke da fada a ji cikin gidan sai ita,ita ke juya kowa ciki harda mai gidan,taci karenta babu babbaka har zuwa lokacin da Allah ya yiwa mai gidan rasuwa aka raba musu gado kowa ya kama gabanshi,koda zainab tayi auren fari mama amarya ba irin mijin da take so zainab din ta aura ba kenan,miji take so ta samu koda ba mai kudi ba amma yana da abun hannunsa,wanda zasu maqale suyita tatsarsa suna tara abun duniya,talaka ne bashir futuk,qarfin soyayyar da zainab din ke masa ya rufe mata idanu har ta aureshi,tayi aurenta ne bayan data kammala kataratun ta na NCE a federal college of education kano wato FCE,kusan zamu iya cewa bashir abokin karatunta ne tare suke daukan lactures course dinsu daya,bayan kammala karatu kuma aiki bai samu ba,sai shagon wani maqocinsu dake kasuwa yake zuwa yana masa jira ana biyansa.
Duk iya yadda mama amaryan taso ta fahimtar da zainab din taqi fahimta,duk da kusan cewa babu abinda ta baro na daga halayen uwarta,bata cimma nasara ba sai bayan da akayi auren,sukaci soyayyarsu suka cinye,a lokacin da gishiri ya fara fita daga kan kaza ne zainab din ta fahimci bashir bai dace da ita ba,daya bayan daya ta dinga bin sawun duk wata dabi'a da huduba da uwar ke azata kai.
Cikin watanni biyar kacal suka balle auren,a lokacin tana dauke da ciki na watanni uku,duk yadda suja zo zubar da cikin abin ya gagara,a cewar mama amaryan baya da wani amfani tunda ubansa bai mallaki komai ba bare su saka ran samun wani alfanu tattare da shi.
Saidai kuma ina,maqaginsa ya riga ya QADDARA sai ya taka doron qasa,bayan wata bakwai ta haife yaronta namiji,ko yayeshi bata yi ba ta soma balle zawarci mai lasisi,a lokacin ta sake haduwa da qawaye kala kala idanunta suka bude,tasan duniya sosai har fiye da yadda uwarta ta sani ta koma dorata akai,hakan ya so tsorata maman har ta soma shirin hanata wasu abubuwan,amma ina.......maqeri ya riga mabada hali,tuni zainab din tasa aka rufe bakin maman da yayyenta maza biyu,duk wani abu da zata aiwatar bata laifi a idanunsu,musamman idan ta samo ta yaga musu.
Tun randa taga mukhtar zuciyarta ta yaba da shi,bata bata lokaci ba wajen bada sunanshi aka mata bincike a kansa,yadda takeso haka sakamakon yazo mata,mukhtar din yayi dai dai da ra'ayinta,saidai bata qaunar kishiya ko misqala zarratin,amma da ta samu labarin wace sumayya sai hankalinta ya kwanta,ta tabbatar ba matsala bace a gunta,aiki guda daya tak zata mata rana guda ta koreta daga gidan,duk da tana diyar malamai ai bata da maganin kirsa ko?.
*** *** ****
Hankalinta bai kwanta ba sai data gana da yaya yahanasu,wadda bata tunkareta ba sai data yi shiri sosai akanta,qwarai yaya yahansun taji wata qauna da aminta wa zainab,musamman data ji cewa ta taba haihuwar d'a namiji ma,nan zainab din ta zube mata alkhairai masu tarin yawa tare da tsara yadda zasu cimma nukhtar din duk da taimakon yaua yahansu wadda ke kiran kanta YAAYA kuma UWA a gunsa.
*** *** ***
Suna shirin cin abincin dare kiran yaya yahanasun ya baqunci wayarsa,dama ya tsammaci hakan saboda tun yammacin jiya da ya ziyarci gidan yaga gilmawar wata cikin layin nasu tamkar zainab din,zuciyarsa bata gasgata masa hakan ba tunda ya riga da ya sani bata san muhallinsu ba,amma duk da haka zuciyarsa bata samu nutsuwa ba har zuwa wannan lokaci.
"Kiyi haquri yaya,amma yanzu bazan samu damar fitowa ba" ya sanar da ita kai tsaye.
"La'ilaha illallahu,mukhtar yaushe kayi wannan riqar,akwai ranar dama da zata zo zan buqaci ganinka kaqi mukhtar" sai ta sa kuka
"Lallai ba shakka sumayya ta gama da mu,taci galaba akanmu ta sake cutar min da d'an uwa" sam baya son yaji kukan nata kamar yadda zuciyarsa ke quna idan yaji tana zagi aibata ko zargin sunayyarsa,hakan ya sanya ya amsa mata kan cewa yaba zuwa.
Wayar ya sauke yana duban sumayya
"Sumayya bana son fitar nan,ina zargin wani abu"ya fada idanunsa na sauya launi da alamun ransa ya fara motsuwa,kai ta kada
"Ka zargi alkhairi ya mukhtar,tunda kasan koma mene yaya jininka ba zata taba cutarka tana sane ba ko?" Shiru ya danyi sannan yace
"Na sani,amma matuqar abinda nake zaegi taje shirin aiwatarwa wannan karon wallahil azim sunayya ba zata kwashe mana da dadi ba,bazan yarda a ringa walagigi da rayuwarmu" duk da cewa a dunqule yayi maganar amma sai data haifar mata da matsanancin faduwar gaba wanda ta sanya har ta kasa tankawa, ya miqe ya shiga dakinsa ya dauki hularsa ya zura da muqullin babur dinsa don ya riga da ya ajjiye motarsa a inda take kwana ya fice daga gidan.
Kan kujera ta koma ta kwanta rigingine gabanta na ci gaba da lugude,a hankali ta dinga ambaton
"Ya rabbi yassir wala ta'asir" sabida neman gudun mawa da daukin wajen ubangiji.
Cikin falonta ya taddata wanda tun kafin ya kai ga shiga ya dinga jiyo dariya da hirarsu ita da yaran da alama cikin nishadi suke da walwala,sallamarsa ya katse hirar tasu,da daya da daya suka fice a dakin ya zama daga shi sai yaya yahanasun.
Suna kan gaisawa jamila ta shigo da jug guda biyu ruwa da lemo da kofuna ta dire masa,ya dauke kai ya dubi yaya yahansun yace
"Gani" sai ta dan murmusa
"Haba muntari,sai kace wanda ake gutsura,ko ruwa ai ka sha ko?" Sai yaga rashin dacewar yadda yazo matan,ko babu komai tsakaninsu ta bashi shekaru,saboda haka ya rusuna ya tsiyayi ruwan yayi kurba daya ya ajjiye kofin.
*** *** ***
Tana jin qarar babur dinsa ta miqe da hanzarinta,har ya shigo da shi ya kulle gidan ya qaraso falon tana tsaye,sam hankalinta ya gaza kwanciya a haka ya sameta a tsayen.
Saidai yanayin da taga fuskarsa ya zabge kaso mafi yawa na tashin hankalin da ta shiga,har ta saki bayyananniyar ajiyar zuciya ba tare da ta sani ba,'yar qaramar dariya ya saki yana fadin
"Me ya tsorataki haka?" Qwayar idanunta ta juya
"Kaine mana,hankalina ya qi kwanciya tunda ka fita"
"To ya kwanta,don babu komai sai alkhairi" duk da bata ji farinciki ko kadan ba yadda ta tsammata sai tace
"To Allah ya lamunce ya shige mana gaba" tayi maganar tana zama.
Ko kadan baiyi mata maganar komai ba,babu abinda yace mata kan hakan har bayan kwana biyu,a tsarinta mutum ce da bata shishshigi cikin lamuran da suka shafi rayuwar wani,hakanan ko da ga mukhtar din ne bata tambayarsa wasu lamura nashi na daban saidai idan shi yaga dama don rad'in kansa ya sanar mata,hakan ya sanya itama bata tambayeshi ba sai tayi zaton wani lamari ne da ya shafesu shi da 'yar uwar tasa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣3⃣
________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa'asa an takrahu shai'an wa huwa khairul lakum,wa'asa an tuhibbu shai'an wa huwa sharrul lakum,wallahu ya'alamu wa'antum la ta'alamu*
*Allahumma farrij hammal mahmumin,Allahumm farrij karbal makrubin*
_______________________________
*Bayan kwanaki biyu*
*** *** *** ***
a hankali ta shigo dakin ganin tunda ya kammala wanka ya shiga bai fito ba bayan ta kammala shirya abincin dare sa zasu ci,turus ta tsaya tana dubansa.
Tsaye yake gaban mudubi sanye da sabuwar shaddarsa ruwan qwaiduwar qwai dinkin boda,taje sumar kansa yake,sosai kayan suka masa kyau,sai ta jingina da bango ta harde hannayenta tana dubansa,da alama ma baisan ta shigo ba.
"Da kyau,irin wannan kwalliya haka da akemin?" Juyowa yayi ya dubeta yana murmushi
"Girmanki ne ai,amma zan danje unguwa tukunna" sai ta danyi jim gabanta na faduwa,take ranta ya darsa mata wani abu,batasan sanda bakinta ya subuce ba
"Zance zaka kenan" juyowa ya sakeyi yana ajjuye cumb din tare da takowa gabanta
"Ya akayi kika canka?,naso ace da kaina na gaya miki my sumy" wani irin abu taji yana ratsata tun daga kanta har qafafunta,yanayin fuskarta ya sauya
"Wai don Allah da gaske kake ko wasa?"
"Da gaske nake mana sumayya,na taba miki irin wannan wasan" ya fada yana qoqarin janyota jikinsa,sai ta zame jikin ta kana ta ja da baya,jikinta ya soma rawa hawaye na shirin zubo mata,hakan ya sanya ta tallafi kanta ta hanyar zama gefan gado,baiyi qasa a gwiwa ba ya bita ya zauna gefanta
"Yi a hankali mana sumayya,me na daga hankali kuma,koma wace zata zo ai kema kinsan a bayanki take ko?" Idanunta ta dago wadanda suka cika da qwalla har sun fara gangarowa ta dubeshi
"Meye na tada hankali kuma,shin ban cancanci nayi kishinka bane ya mukhtar?"
"Kin cancanci fiye da haka ma sumayya,amma kiyi haquri,in sha Allahu ina saka ran wannan karon alkhairi ne auren da zanyi".
Cike da mamaki ta watsa masa wani kallon
" wanne alkhairi ya mukhtar?,har ka manta wuyar da mukaci cikin shekara guda kacal?....."
"No....ki kyautata zato sumayya ba haka na sanki ba....", qarar wayar sa ce ta katse abinda yake shirin gaya mata,ya sanya hannu ya daga wayar bayan ya hade fuska kamar yana gaban mai kiran
" nace miki gani nan ko?"daga haka ya datse kiran ya maida hankalinsa kanta.
Hannu ya sanya ya share mata hawayen sannan ya miqe
"Ki bari na dawo zamuyi magana,ki kwantar da hankalinki sumayya kinji" bata iya amsa masa ba har ya sanya hularsa ya fice.