Sashe 198
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A falo ta samu eesha saman kujera qafa daya kan daya anata sana'ar danna waya,daga kai tayi ta dubi sumayya,duk da batayi makeup ba amma ba qaramin kyau tayi ba,ta dan zubawa material din jikinta ido,tana da irinshi,daga dubai mamarta ta kawo mata shi,yana daga daga cikin kayan ta da take ji da su,wani kishi ya cika kata ido,dinkin doguwar riga ne wanda ya fitar da sigarta,ta zuba saitin cikinta ido,baiyi fitowar da kowa zai iya ganewa ba,amma matuqar ka qware wajen gulma sa ido da iya munafunci kallo daya zaka yi masa ka gane tana dauke da yaron ciki,wani abu ya tsaya mata a wuya,cikin da bai isa zama mutum ba ya tsone mata ido,saboda ta fuskanci kowa maraba yake da shi,faranta ran kowa yake banda ita,land line dake falon ta dauka tayi kira sashen ma'aikata,tayi sa'a kuwa baba uwanin ce ta dauka ta buqaci ganinta
"Gani nan uwar daki" ta ambata,bata tsaya falon ba tayi shigewarta kitchen taba jiranta,qwararan mintuna biyar saiga baban
"Baba....yaufa zamuyi baqi me za'a tana darmusu ne?,amarensu mahmoud?"
"Eh gaskiya ya kamata,me kike buqatar ayi musu?,ai saiki fada ki samu waje ki zauna" dariya tayi
"Baba,wai haka zanta kwanciya kamar ruwa?,kema kin sani motsa jikin ai yana da muhimmanci ko?,yanzu bari kiga" nan ta tsara ma baban abinda za'ayi,baba na tsaye ita tana daga zaune suka soma aikinsu,suna yi baba na bata labaruka suna hirarsu abinsu,kafin su kammala kusan shigowar eesha hudu,tazo ta bude freezer ta fice,ko waiwayowa sumayya bata yiba bare ta nuna taga shigowarta,ita dai abun na daure mata kai,ta rasa meke tsakaninsu?,bayan da suka kammala sumayya ta dora tuwan semo wanda duja baifu malmala shida ba,tayi miyar kuka wadda taji nama da tantaqwashi,ita take sha'awa,tana dab da barin kitchen din amira ta fado,daga gidan mutuwar take,saboda suna da alaqa da familyn saifullahi
"Uwar biyu" ta soma fadi sannan ta bude freezer ta dauki ruwan sanyi ta sha sosai saboda ranar da ake yi,sumayyan na tsaye tana dubanta
"Ya na ganki haka afujajan" kai ta kada
"Ke dai bari kawai,wallahi bacci kazo nayi kafin yamma na wuce gida,drivan ma na sallameshi na karbi key din na koma da kaina" dariya ta danyi
"Wannan bacci wannan bacci amira anya qalau kike,jiya fa ina jiyo ummi na miki fada kin dora girki kinje ki kwanta kin barshi ya soma qonewa,vanda Allah ya sanya mai aikinki bata tafi gida ba gobara zaki hada"
"Shaye shaye na fara" ta fada cikin sigar tsokana
"Ko kuma da kin riga kin sha din ba" itama ta maida mata cikin tsokanar suka soma takawa don ficewa daga kitchen din suna dariya
"Allah amiran yaya musty(da yake taa sauya mata suna)bansan meke damuna ba,yanzun fa ko saif bana iya jira ya dawo kan ya dawo na jima duniyar bacci"
"Tabdi....kije kiga likita kam,Allah yasa kema kin biyo sahu?"
"Allah ko?,kaddau bakin saif ya kamani?" Ta fada tana fiddo ido
"Ke dalla,meye ne kika wani waremin idanunkin nan irin na yayanki kamar ni nayi abun" ta fada sanda sukaqaraso cikin falon eesha na zaune,dariya amira ta saki har da d'an ihunta
"Kice kawai yayana rikitaki yake da idanunshin nan,kinsan Allah sunfi nawa kyau,ni kaina lokacin ina qarama cewa nake muyi musanye,Allah yasa ki haifo mana mai kama da shi"murmushi kawai tayi tana tuna yanayin kallonshi,yadda ya iya hukunci da ido,yana rikita ta ba qarya ba a duk sanda ya ritsata da kallonshi,murmushi ya subuce mata a sarari ba tare data sani ba
"yar is,kinzo ko ki nemi hanyar gidan ko?,wallahi kada kiyi aure ki tsammaci zan dinga jelan zuwa gidanki" sumayya ta tsinci amira na gayawa eesha,dariya eeshan tayi
"Ke kuwa zuwa ya kama,idan akayi 'yar gida ai kinga ko bako qaunar Allah dole kizo,ko banza na zama yayarki"ta fada da biyu,tabbas maganan ta samu shiga zuciyar sumayya,ta kuma fahimci sarai inda zancan eesha ya dosa,saidai batasan ka wa take maganan ba,mahmoud da mus'ab har yau basu cika wata biyu da aure ba,ya adam bai garin ma baki daya matanshi biyu ga yara kusan hudu,ya girme mata ma sosai,almustapha fa?,wani sashe na zuciyarta ya gaya mata,sai ta soma juya zancan a hankali cikin ranta
"Ah lallai fa,ga mai yawan rai kenan.....kinga bacci zanje nayi na wasu awannai,bari naje na dawo sai mu qarasa zancan....wai nikam me ya samu number salama bata shiga?" Ta tambayi eeshan tana yin gaba
"Salama?,bakisan muhsin ya sauya mata layi ba,bikinta bai wuce one month ba yace bai sonta da tsohon layinta,but dazun ma tace na tura mata num dinki ba mamaki kiji ta kiraki"
"Kice akwai shagali....saura ku sai ku bada himma" ta fada tana dariya
"Me kike ci na baka na zuba" eeshan ta fada tana yatsina fuska
"Eesha shegiyar gari....wai ina bash ne?"
"Standby zaki ce,jeki dawo kizo na gaya miki"
"Alright"Amiran ta kuma fada tana bin bayan sumayya da tunitayi gaba.
Suna shiga amira ta kama kafadar sumayya dake qoqarin daure gashinta don shiga wanka
"ke wai baki karanci komai tattare da eesha ba?,ba kya ganin irin kallo da take binki da shi" murmushi sumayya tayi duk da itama abun ya tsaye mata a rai,har yau kuma bai daina bata mamaki ba
"Kinsan wai yaya man take so?"amira ta fada tana kecewa da dariya ta fada saman gado,maganar ta daki sumayya,sai yanzu ta gano abinda ya sanya eesha bata qaunarta,amma sai ta dake
"to Allah ya tabbatar da alkhairi" harara amira ta watsa mata sannan tace
"Haka zaki fada?,ke yanzu fatar kishiya kikewa kanki banda waccar da take gabanki?" Cikin dakiya tace
"To meye?,bakiji abinda kema kika fada ba,nima wata nazo na taras"
"Amma wallahi baki son ya almustapha amira,da eesha da su'af meye banbancinsu?,qasar haihuwa ce kawai ta raba su,ai ko mata sun qare bazan masa fatan auren eesha ba wkh duk da tana 'yar uwata,amma duk dan uwa na gari zaya so yaga nashi na auren magartacciyar mace kaman ke"
"Lallai kam,idan rabonshi ce ai ba wanda ya isa ya hana ko?" Ta fada a fili tamkar ba komai,cikin zuciyarta kuwa kaman zata fashe
"Allah ya tsari gatari da saran shuka,kinsan ma duk cikin yaran family ba wanda sam basa hada inuwa da yaya almustapha irin eesha?,itafa ta sanya ya saka dokar hana samarinsu zuwa gidan nan matuqar suka zo hutu da sallah,tun randa ya ganta da wani cikin mota suna har harkoki"
"To Allah ya kyauta,kedai kwanta kawai kiyi baccinki"ta fadi tana daukar towel saboda ta sake watsa ruwa
"naqi din,kuma kamar a kunnen ya almustapha kin masa mugun fatan auren eesha"dariya ta baiwa sumayyan saboda yadda tayi kicin kicin kaman ance mata saif zai qara aure,toilet ta shige don ta tabbata ta biyewa amira sai su bata lokaci a wajen.
Tana fitowa wayarta ta soma ringing,tana dubawa sunan almustapha ne a sama,murmushi ya subuce mata,halan yau 'yan rigimar ne a kusa,dududu awa uku fa da gama wayarsu,sai ta zauna bakin madubu ta daga kiran ta kara kunnenta tare da yin sallama
"kewarki nake" ya soma fada,murmushi ta sake masa mai dan fidda sauti har cikin kunnenshi
"Awa uku da rabuwarmu fa?"
"Jinta nake makan shekara uku,ummu abdallah kaman ma baki tausayi na,ashe haka so yake wahal da zuciyar mutum?,kinsan yanzhn haka wani asibiti ke buqatar taimakona za'a yiwa matan wani aiki amma na gagara zuwa,ko naje din ma nasan ba abinda zan iya aiwatarwa....please my summy kiji tausayina mana" ya qarasge zanacan a shagwabe,dariya ta saki salon magananshin ya tsumata
"Wallahi abu abdalla ka zama wami shagwababbe,anty su'ad ta lalata ka"
"Zaki gane hakan idan na kamaki a hannu,kinsan Allah....ranan ko babynmu bazan tausayawa ba bare ke,zaki zo hannu" ya fada yana katse kiran,murmushi ta dinga fiddawa,bata ajjiye wayar ba sai data tura masa sms da tasan zata haukatoshi sannan tayi switchoff din wayar yadda koya kira bazai sameta ba,ido ta lumshe tana sakin murmushi,ba qarta ita kanta tasan ba qaramin rashin mijinta tayi ba
"Laila majnoon,idan kun gama baqin sunzo" amira dake kwamce ta fada,ita kanta abun ma burgeta,wato haka yaya almustapha yake baje soyayyarshi,amma idan ka ganshi a waje sai kace wani zaki,musamman idan ya soma muzuran nan nashi ko bada umarni,baka ce ya taba dariya ba,amma yanzu ya wani narke kaman dan yaye,sam ita sumayya ma ta manta da ita sai da tayi magana
"To 'yar sa ido" dariya suka sanya baki daya,amira ta miqe daga saman gadon ta zauna sosai
"Seriouse amiran yaya musty....wai meye sirrin don Allah,salon soyayyarkun nan a bani nasha don Allah"
"Min indillah" ta bata amsa tana ciro kayan da zata saka
"Da gaske?"
"Biya sai na gaya miki"
"Ko nawa ne ko zan nada indai za'a gayan" dariya ta baiwa sumayya sosai,ita kanta wani lokaci ta zauna ta kanyi mamakin kansu,ita da kanta batasan akwai duniyar data qunshi zallar farinciki har haka ba sai yanzu,duba da irin bigire na nau'in rayuwa daban daban data afka,taso mukhtar a sanda bata mallaki hankalinta ba,a sanda bata banbance so qauna da shaquwa,wasu mata sun shiga rayuwarsu sun kawo naqasu wa farinciki da shaquwar dake tsakaninsu,sannan bayan duka wannan tazo ta rashi a sanda bata da kowa sai shi kadai ta mallaka,bata saba da kowanne namiji ba sai shi,tazo ta auri lukman bisa tsautsayi da qaddarar data hauta na dole sai ta shiga rayuwar wasu,daga qarshe ta samu almustapha,wanda ta sameshi ne a lokacin da hankali ya gama gameta,ta gama sanin zaqi da madaci,so qauna da shaquwa da kuma,tasan dama da hagunta.
Aina da asma'u sune matan mus'ab da mahamoud,dukkaninsu basu fi sa'annin sumayya ba,koda zata girme musu bazata basu shekara ba,bare kana ganinsu zaka musu kudin goron sa'anni ne,dukkaninsu wayayyu ne masu matuqar kirki,karatunsi da wayewarsu bai hanasu kasancewa 'yammata nutsatstsu masu cikakkiyar tarbiyya ba,kowacce ta samu tarbiyya daga gidansu,kamar asm'u wadda makaranta daya sukayi karatu da mahmoud wata private university dake nan garin abuja,saidai tana matakin farko ne mahmoud yana matakin qarshe,kamun kanta da nutsuwarra shi ya fara jan hankalinsa,abinda bai fiya gani ba wajen 'yammatan dake manyan makarantu na jami'o'i,bare irin nasu makarantun na yaran masu da shi,kowacce ta dauki tabara da rashin tarbiyya rashin cikakken kamun kai a amtsayin wayewa,wannan ya zama ruwan dare cikin makarantunmu na walau na gwamanti ko kuma na kudi.
"Gani nan uwar daki" ta ambata,bata tsaya falon ba tayi shigewarta kitchen taba jiranta,qwararan mintuna biyar saiga baban
"Baba....yaufa zamuyi baqi me za'a tana darmusu ne?,amarensu mahmoud?"
"Eh gaskiya ya kamata,me kike buqatar ayi musu?,ai saiki fada ki samu waje ki zauna" dariya tayi
"Baba,wai haka zanta kwanciya kamar ruwa?,kema kin sani motsa jikin ai yana da muhimmanci ko?,yanzu bari kiga" nan ta tsara ma baban abinda za'ayi,baba na tsaye ita tana daga zaune suka soma aikinsu,suna yi baba na bata labaruka suna hirarsu abinsu,kafin su kammala kusan shigowar eesha hudu,tazo ta bude freezer ta fice,ko waiwayowa sumayya bata yiba bare ta nuna taga shigowarta,ita dai abun na daure mata kai,ta rasa meke tsakaninsu?,bayan da suka kammala sumayya ta dora tuwan semo wanda duja baifu malmala shida ba,tayi miyar kuka wadda taji nama da tantaqwashi,ita take sha'awa,tana dab da barin kitchen din amira ta fado,daga gidan mutuwar take,saboda suna da alaqa da familyn saifullahi
"Uwar biyu" ta soma fadi sannan ta bude freezer ta dauki ruwan sanyi ta sha sosai saboda ranar da ake yi,sumayyan na tsaye tana dubanta
"Ya na ganki haka afujajan" kai ta kada
"Ke dai bari kawai,wallahi bacci kazo nayi kafin yamma na wuce gida,drivan ma na sallameshi na karbi key din na koma da kaina" dariya ta danyi
"Wannan bacci wannan bacci amira anya qalau kike,jiya fa ina jiyo ummi na miki fada kin dora girki kinje ki kwanta kin barshi ya soma qonewa,vanda Allah ya sanya mai aikinki bata tafi gida ba gobara zaki hada"
"Shaye shaye na fara" ta fada cikin sigar tsokana
"Ko kuma da kin riga kin sha din ba" itama ta maida mata cikin tsokanar suka soma takawa don ficewa daga kitchen din suna dariya
"Allah amiran yaya musty(da yake taa sauya mata suna)bansan meke damuna ba,yanzun fa ko saif bana iya jira ya dawo kan ya dawo na jima duniyar bacci"
"Tabdi....kije kiga likita kam,Allah yasa kema kin biyo sahu?"
"Allah ko?,kaddau bakin saif ya kamani?" Ta fada tana fiddo ido
"Ke dalla,meye ne kika wani waremin idanunkin nan irin na yayanki kamar ni nayi abun" ta fada sanda sukaqaraso cikin falon eesha na zaune,dariya amira ta saki har da d'an ihunta
"Kice kawai yayana rikitaki yake da idanunshin nan,kinsan Allah sunfi nawa kyau,ni kaina lokacin ina qarama cewa nake muyi musanye,Allah yasa ki haifo mana mai kama da shi"murmushi kawai tayi tana tuna yanayin kallonshi,yadda ya iya hukunci da ido,yana rikita ta ba qarya ba a duk sanda ya ritsata da kallonshi,murmushi ya subuce mata a sarari ba tare data sani ba
"yar is,kinzo ko ki nemi hanyar gidan ko?,wallahi kada kiyi aure ki tsammaci zan dinga jelan zuwa gidanki" sumayya ta tsinci amira na gayawa eesha,dariya eeshan tayi
"Ke kuwa zuwa ya kama,idan akayi 'yar gida ai kinga ko bako qaunar Allah dole kizo,ko banza na zama yayarki"ta fada da biyu,tabbas maganan ta samu shiga zuciyar sumayya,ta kuma fahimci sarai inda zancan eesha ya dosa,saidai batasan ka wa take maganan ba,mahmoud da mus'ab har yau basu cika wata biyu da aure ba,ya adam bai garin ma baki daya matanshi biyu ga yara kusan hudu,ya girme mata ma sosai,almustapha fa?,wani sashe na zuciyarta ya gaya mata,sai ta soma juya zancan a hankali cikin ranta
"Ah lallai fa,ga mai yawan rai kenan.....kinga bacci zanje nayi na wasu awannai,bari naje na dawo sai mu qarasa zancan....wai nikam me ya samu number salama bata shiga?" Ta tambayi eeshan tana yin gaba
"Salama?,bakisan muhsin ya sauya mata layi ba,bikinta bai wuce one month ba yace bai sonta da tsohon layinta,but dazun ma tace na tura mata num dinki ba mamaki kiji ta kiraki"
"Kice akwai shagali....saura ku sai ku bada himma" ta fada tana dariya
"Me kike ci na baka na zuba" eeshan ta fada tana yatsina fuska
"Eesha shegiyar gari....wai ina bash ne?"
"Standby zaki ce,jeki dawo kizo na gaya miki"
"Alright"Amiran ta kuma fada tana bin bayan sumayya da tunitayi gaba.
Suna shiga amira ta kama kafadar sumayya dake qoqarin daure gashinta don shiga wanka
"ke wai baki karanci komai tattare da eesha ba?,ba kya ganin irin kallo da take binki da shi" murmushi sumayya tayi duk da itama abun ya tsaye mata a rai,har yau kuma bai daina bata mamaki ba
"Kinsan wai yaya man take so?"amira ta fada tana kecewa da dariya ta fada saman gado,maganar ta daki sumayya,sai yanzu ta gano abinda ya sanya eesha bata qaunarta,amma sai ta dake
"to Allah ya tabbatar da alkhairi" harara amira ta watsa mata sannan tace
"Haka zaki fada?,ke yanzu fatar kishiya kikewa kanki banda waccar da take gabanki?" Cikin dakiya tace
"To meye?,bakiji abinda kema kika fada ba,nima wata nazo na taras"
"Amma wallahi baki son ya almustapha amira,da eesha da su'af meye banbancinsu?,qasar haihuwa ce kawai ta raba su,ai ko mata sun qare bazan masa fatan auren eesha ba wkh duk da tana 'yar uwata,amma duk dan uwa na gari zaya so yaga nashi na auren magartacciyar mace kaman ke"
"Lallai kam,idan rabonshi ce ai ba wanda ya isa ya hana ko?" Ta fada a fili tamkar ba komai,cikin zuciyarta kuwa kaman zata fashe
"Allah ya tsari gatari da saran shuka,kinsan ma duk cikin yaran family ba wanda sam basa hada inuwa da yaya almustapha irin eesha?,itafa ta sanya ya saka dokar hana samarinsu zuwa gidan nan matuqar suka zo hutu da sallah,tun randa ya ganta da wani cikin mota suna har harkoki"
"To Allah ya kyauta,kedai kwanta kawai kiyi baccinki"ta fadi tana daukar towel saboda ta sake watsa ruwa
"naqi din,kuma kamar a kunnen ya almustapha kin masa mugun fatan auren eesha"dariya ta baiwa sumayyan saboda yadda tayi kicin kicin kaman ance mata saif zai qara aure,toilet ta shige don ta tabbata ta biyewa amira sai su bata lokaci a wajen.
Tana fitowa wayarta ta soma ringing,tana dubawa sunan almustapha ne a sama,murmushi ya subuce mata,halan yau 'yan rigimar ne a kusa,dududu awa uku fa da gama wayarsu,sai ta zauna bakin madubu ta daga kiran ta kara kunnenta tare da yin sallama
"kewarki nake" ya soma fada,murmushi ta sake masa mai dan fidda sauti har cikin kunnenshi
"Awa uku da rabuwarmu fa?"
"Jinta nake makan shekara uku,ummu abdallah kaman ma baki tausayi na,ashe haka so yake wahal da zuciyar mutum?,kinsan yanzhn haka wani asibiti ke buqatar taimakona za'a yiwa matan wani aiki amma na gagara zuwa,ko naje din ma nasan ba abinda zan iya aiwatarwa....please my summy kiji tausayina mana" ya qarasge zanacan a shagwabe,dariya ta saki salon magananshin ya tsumata
"Wallahi abu abdalla ka zama wami shagwababbe,anty su'ad ta lalata ka"
"Zaki gane hakan idan na kamaki a hannu,kinsan Allah....ranan ko babynmu bazan tausayawa ba bare ke,zaki zo hannu" ya fada yana katse kiran,murmushi ta dinga fiddawa,bata ajjiye wayar ba sai data tura masa sms da tasan zata haukatoshi sannan tayi switchoff din wayar yadda koya kira bazai sameta ba,ido ta lumshe tana sakin murmushi,ba qarta ita kanta tasan ba qaramin rashin mijinta tayi ba
"Laila majnoon,idan kun gama baqin sunzo" amira dake kwamce ta fada,ita kanta abun ma burgeta,wato haka yaya almustapha yake baje soyayyarshi,amma idan ka ganshi a waje sai kace wani zaki,musamman idan ya soma muzuran nan nashi ko bada umarni,baka ce ya taba dariya ba,amma yanzu ya wani narke kaman dan yaye,sam ita sumayya ma ta manta da ita sai da tayi magana
"To 'yar sa ido" dariya suka sanya baki daya,amira ta miqe daga saman gadon ta zauna sosai
"Seriouse amiran yaya musty....wai meye sirrin don Allah,salon soyayyarkun nan a bani nasha don Allah"
"Min indillah" ta bata amsa tana ciro kayan da zata saka
"Da gaske?"
"Biya sai na gaya miki"
"Ko nawa ne ko zan nada indai za'a gayan" dariya ta baiwa sumayya sosai,ita kanta wani lokaci ta zauna ta kanyi mamakin kansu,ita da kanta batasan akwai duniyar data qunshi zallar farinciki har haka ba sai yanzu,duba da irin bigire na nau'in rayuwa daban daban data afka,taso mukhtar a sanda bata mallaki hankalinta ba,a sanda bata banbance so qauna da shaquwa,wasu mata sun shiga rayuwarsu sun kawo naqasu wa farinciki da shaquwar dake tsakaninsu,sannan bayan duka wannan tazo ta rashi a sanda bata da kowa sai shi kadai ta mallaka,bata saba da kowanne namiji ba sai shi,tazo ta auri lukman bisa tsautsayi da qaddarar data hauta na dole sai ta shiga rayuwar wasu,daga qarshe ta samu almustapha,wanda ta sameshi ne a lokacin da hankali ya gama gameta,ta gama sanin zaqi da madaci,so qauna da shaquwa da kuma,tasan dama da hagunta.
Aina da asma'u sune matan mus'ab da mahamoud,dukkaninsu basu fi sa'annin sumayya ba,koda zata girme musu bazata basu shekara ba,bare kana ganinsu zaka musu kudin goron sa'anni ne,dukkaninsu wayayyu ne masu matuqar kirki,karatunsi da wayewarsu bai hanasu kasancewa 'yammata nutsatstsu masu cikakkiyar tarbiyya ba,kowacce ta samu tarbiyya daga gidansu,kamar asm'u wadda makaranta daya sukayi karatu da mahmoud wata private university dake nan garin abuja,saidai tana matakin farko ne mahmoud yana matakin qarshe,kamun kanta da nutsuwarra shi ya fara jan hankalinsa,abinda bai fiya gani ba wajen 'yammatan dake manyan makarantu na jami'o'i,bare irin nasu makarantun na yaran masu da shi,kowacce ta dauki tabara da rashin tarbiyya rashin cikakken kamun kai a amtsayin wayewa,wannan ya zama ruwan dare cikin makarantunmu na walau na gwamanti ko kuma na kudi.