Sashe 4
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna shirin shiga rumfarta tana daga labulen dakin
"Au sai yau kaga damar zuwa kenan......shashan yaro ana maka gata kana noqewa" ta fada tana sakin labulen ta juya zuwa ciki.
Bata lura tare suke ba sai da suka shiga ciki suka zauna,sumayya ta gaisheta ta amsa sama sama,ganin idonta sam bai hana yaya yahanasu yin duk maganganunta ba,ita dai kam kanta ta sunkuyar,daga bisani ta miqe ta basu guri jin musu nason barkewa tsakanin mukhtar da yaya yahanasu kan lissafin abinda suke da buqatar ya bada,kama daga kudin aure kudin zance lefe har zuwa sadaki,yace zaya bada kudin aure da na sadaki amma shikam bazaya iya yin wani lefe ba,kasuwa babu ciniki,nan ta barsu batasan yanda suka kaya ba yadai fito yace ta tashi su tafi.
Ko sallamar da take wa yaya yahanasun bata tanka mata ba har suke wuce,suna kan hanya babu wanda yace da dan uwansa komai har suka qarasa gidansu.
Ciki ya shiga suka gaisa da maman nata kasancewar abba malam mahaifinsu kamar yadda suke ce masa baya nan,'yan qannanta duk suna tsakar gida mukhtar ya raba misu biscuite kamar yadda ya saba,ya miqe zai fice yana cewa zai zaga bayansu gun wani abokinsa idan ya dawo zai kirata su wuce tace tom.
Gaisawa sosai sukayi da mamanta ta tambayi lafiyarta da ta gidanta ta amsa mata da komai lafiya.
Shiru ne ya biyo baya,tunanin abinda ya faru dazun gidan yaya yahanasu yayi nasarar wafce tunaninta ba tare da ta shirya ba,haka maman ta tadda ta,ta ajjiye kwanon dambun data je debo mata
"Lafiya dai ko sumayya" murmushin yaqe tayi ta janyo kwanon dambun tana budewa sannan tace
"Mama aure yaya mukhtar zai qara" maganar ta dan taba maman,tsakanin da d'a da mahaifi,tausayinta ta dinga ji yana ratsata,babu shakka abu ne mai wuya zama da kishiya a wannan zamanin,abu ne da har yau yaqi dadi a cikin gidajen aurenmu,ga yarinyar tata gwanar haquri da shegen zurfin ciki ce,amma duk da haka ta sani ba duka aka taru aka zama daya ba,duk abinda zata gaya mata a yanzu shi zai zame mata madubin dubawarta.
Murmushi maman tayi sannan tace
"Babu komai,ai namiji mijin mace hudu ne,Allah ne ya halasta masa,abinda nake son gaya miki kawai shine kada ki soma cewa zaki tada hankalinki ko ki daga hankalin mijinki,ki zauna da ita tsakani da Allah,ki sauke duk wani haqqi nata dake wuyanki,sumayya kada ki sake kice zaki cuceta,idan kika cuceta sumayya ni mahaifiyarki ban yafe miki ba".
Kai ta gyada" in sha Allahu mama zanyi duk abinda kika ce,da ikon Allah bazan zama mai sabawa maganarki ba"a hankali maman ta dinga hilatarta tana kwantar mata da hankali har ta kusa cinye dambun baki daya.
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_bismilla hir rahmanir rahim_
*inna ma'al usri yusrah,fa inna ma'al usri yusrah*
______________________
0⃣3⃣
Suna cikin hirar mukhatr ya turo qaninta mubarak yayi kiranta ta fito zasu tafi,nan mama ta hada mata su kuka kubaiwa daddawa barkono har da tsakin masara saboda dambu ko dan malele,tana hada mata kayan tana dada kwantar mata da hankali tare da jaddada mata kada ta sake ta tashi hankalin mijinta ko ita kanta,ko tace zata yi wani rashin kyautawa ga daya daga cikin 'yan uwan mukhtar,haihuwa kuwa lokaci ne,idan Allah yaso ma sai taga sanadiyyar shigowar wata ita ma ta samu nata rabon,ta dora da cewa
"Bare ma duka duka nawa kike sumayya,mu a da can Allah na tuba ba sai kiyi shekara goma da aure baki haihu ba babu wanda ya damu da ke,haka kema baki damu kanki ba,ci da zuci ne kawai yanzu irin na yaran zamani" maganar sai ta bama sumayya dariya da kunya,har ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta.
Suna shirin kwanciya bacci lokacin yana zaune gefan gadonsu yana shan ruwan baqin shayi,ita kuma tana taje kanta,ta cikin madubin yake qare mata kallo yadda kullum take sake zama cikakkiyar mace,tamkar ba zata masa magana ba amma abun nata cinta a zuciya,saboda daga shigowarsu gida zuwa shirin kwanciya da sukeyi yanzu yaya yahanasu ta kira shi ya kusa sau biyar,duk da bata kusa amma ta fahimci taqaddamar me suke,maganar lefe ne da yace ba zaya yi ba,ta dan cije lebanta sannan tace
"Ya mukhtar"
"Ya akayi sumy?" Ya fadi yana saurarenta.
Sai data jawo dressing chair gabansa ta zauna sannan ya dubeshi,cikin nutsuwar nan tata hadi da kaifin hankali da zurfin tunani
"Ya mukhtar kayi haquri idan na maka shishshigi,sai nake ganin baka kyauta ba",cikin rashin fahimta ya tambayeta
" da akayi me fa?"ta danyi jim kamar ba zata yi magana ba sannan tace
"A ganina bai kamata ka dinga sa'insa da yaya yahanasu ba,ko banza ta girmeka,bugu da qari ita ta zame maka tamkar mahaifiyarka ka manta?,ita ta raineka har ka kawo girmanka,ka san cewa dai ba zata taba yin abinda zai cutar da kai ba,a ganina auren nan saboda qaruwarka ne take buqatar kayi,ko babu komai idan fa'iza ta haihu sai an fara cewa danka kafin a ce dan yaya yahanasu ko?" Ta dan sarara da maganar tana hadiye wani abu mai daci wanda bata san meue sanadiyyar tasowarsa ba daga qirjinta.
Ko bata qarasa ba ya fahimci kan me take magana,saboda haka ya bata fuska
"Kinga sumayya,babu ruwanki da wannan maganar ki fita a cikinta,lefe ne nace bazanyi ba suyi mata,ai bani nace ina son auren ba ko?,ina zaman zamana haka kawai ina lallaba rayuwata sai su baro min aikin da bani na saka su ba?".
Kai take gyadawa idonta cikin nasa wanda tuni ya tara qwalla shirin zubowa kawai take
" na gode ya mukhatar,ina ka taba gani an auri budurwa ba'a yi mata lefe ba?bayan haka kuma ka riga da ka san cewa matuqar bakayi lefe ba to sumayya ce ta hanaka,duk wanda yaga laifina ko ya zageni ya mukhtar kai ka jawomin"sai ta tashi daga saman kujerar ta haye gado ta lulluba har saman kanta kaana ta fashe da kuka.
Har cikin ransa ya dinga jin shigar kukan nata,ya runtse ido yana jin bata can can ci haka ba,da me zata ji cikin abu ukun,sai ya sanya hannayeshi ya dagota baki daya zuwa jikinsa yana goge mata hawayen tare da fadin
"Ya isa sumayya,ya isa,me kike so ayi?,gaya min" sai da taja hanci kadan sannan tace
"Kayi lefe kamar yadda yaya yahanasu ta buqata"
"Shikenan an gama,sunci darajarki" sai ta saki dan qaramin murmushi sannan tace
"Na gode".
Washegari yana cikin karyawa kafin ya fita wayarsa ta soma ringing,sumayya ta dauko ta miqa masa da yake tana kan t.v stand tana chargy,daga yanayin maganarsa kawai ya tabbatar mata yaya yahanasu ce,kuma zancan jiya ne bai wuce ba,a gimtse ya amsa cewa zaiyi laifen,amma fa sam shi ba kudi zai bada ba,zaiyi iyakacin abinda zai iya ya kawo musu,daga haka ya kashe wayan ma baki daya,tana gefe tana saurarensu kanta sunkuye tana wasa da yatsun hannunta,ya kammala ta masa rakiya kamar yadda ta saba,dawowa yayi da baya ya rungumeta sannan ya sumbaci goshinta
" Allah yayi miki albarka"ya fada yana sakinta
"Amin ya mukhtar" ta fada cikin farinciki,saboda tuni maman ta ta gaya mata albarkar miji na bin mace,hakanan fushinsa ko yardarsa na tare da ta ubangiji.
Cike da farinciki ta koma cikin gidan saboda albarkar da ya sa mata ta faranta mata,taci gaba da kintsa ragowar ayyukan da suka rage mata,bata jima da kammalawa ba ta zauna tana hutawa wayarta ta dauki qara,da sauri ta daga ganin sunan abbanta na yawo bisa screen din wayar.
Cikin girmamawa ta gaidashi ya amsa mata yana tambayarta gida da kuma mukhtar tace ai yama fita.
"Mamanki ta gaya min mukhtar zai qara aure"
"Eh abba malam"
"To ina fata ba zaki watsa mana qasa a ido ba,ba za kiyi watsi da tarbiyyar da muka baki ba"
"In sha Allahu malam"
"To Allah ubangiji ya albarkaceki ya albarkaci aurenki" daga haka ya dora mata da nasiha cikin hikima da ilimi,cike da fadar Allah da ma'aikinsa,hakan ba qaramin sake kwantar mata da hankali yayi ba,ya qare nasihar tasa da fadin
"Babu wani abu da kike buqata?"
"Eh babu malam" ta fadi hakan saboda babu abinda mukhtar ya gaza da shi,don hatta kudin kashewa yakan qimanta ya bata,ya danganta da yanayin samun da yayi a kasuwa.
"To shikenan,haka ake so,inaga zan duba wajen sati na gaba ko wajejen satin sama,zan aiko abubakar(yayanta ne shine na fari a gidansu,amma baiyi aure ba karatu yake)zaizo. A fidda kayan gadonki da kujerunki a sauya miki wasu" farinciki ya cikata,duk da cewa wadan nan natan ma babu abinda sukayi,don sanda sukayi shekara hudu da aure mukhtar ya fitar da na aurenta na ainihi ya sauya mata su.
"Na gode,na gode qwarai malam Allah ya saka da alkhairi,ya qara lafiya da nisan kwana mai amfani,Allah ya qara budi da rufin asiri"
"Amin ya Allah,amma abinda zaki biyani da shi kawai kici gaba da zaman aure cikin gidanki"
"Da yardar Allah malam" ta amsa masa daga haka sukayi sallama.
Sosai malam yake aon sumayya,don tun tana mitsitsiyarta halayyarta daban take,tana da tarin haquri kawaici da zurfin ciki,shi yasa duk cikin yaransa yafi sonta,duk da cewar dukan yaran nasa maman sumayyan ce ta haifesu,ko a lokacin da suka aura mata mukhtar ma ce mata kawai yayi ga miji yayi mata kuma aure zaiyi mata,bata ce komai ba don ba wayo gareta ba,duk da haka dama kunya gareta,gudu tayi ma ta bar gurin sanda malam din ke gaya mata,ita ce yarinya mace ta farko a gurinsa sai qannenta su hudu.
Mukhtar zamu iya cewa rako wani abokinsa yayi gurin malam din kasancewar malam din yana bada karatu tsakanin sallar magariba da isha'i wa matasa da dattijan unguwa,gani daya ya yiwa sumayya yaji tayi masa kasancewarsa mutum wanda sam baya da sha'awar auren macen da tayi zurfi a karatu,tunda yayi universty shima yaga irin qazamar rayuwar da mafi yawancin 'yammatan keyi duk da ba duka aka taru aka zama daya ba.
To sara ne yazo kan gaba shima malam ba mai son yaransa suyi bokon bane,saboda haka yana bincike kan mukhtar ya tabbatar da nagartar halayyarsa ya basu auren sumayyan.
"Au sai yau kaga damar zuwa kenan......shashan yaro ana maka gata kana noqewa" ta fada tana sakin labulen ta juya zuwa ciki.
Bata lura tare suke ba sai da suka shiga ciki suka zauna,sumayya ta gaisheta ta amsa sama sama,ganin idonta sam bai hana yaya yahanasu yin duk maganganunta ba,ita dai kam kanta ta sunkuyar,daga bisani ta miqe ta basu guri jin musu nason barkewa tsakanin mukhtar da yaya yahanasu kan lissafin abinda suke da buqatar ya bada,kama daga kudin aure kudin zance lefe har zuwa sadaki,yace zaya bada kudin aure da na sadaki amma shikam bazaya iya yin wani lefe ba,kasuwa babu ciniki,nan ta barsu batasan yanda suka kaya ba yadai fito yace ta tashi su tafi.
Ko sallamar da take wa yaya yahanasun bata tanka mata ba har suke wuce,suna kan hanya babu wanda yace da dan uwansa komai har suka qarasa gidansu.
Ciki ya shiga suka gaisa da maman nata kasancewar abba malam mahaifinsu kamar yadda suke ce masa baya nan,'yan qannanta duk suna tsakar gida mukhtar ya raba misu biscuite kamar yadda ya saba,ya miqe zai fice yana cewa zai zaga bayansu gun wani abokinsa idan ya dawo zai kirata su wuce tace tom.
Gaisawa sosai sukayi da mamanta ta tambayi lafiyarta da ta gidanta ta amsa mata da komai lafiya.
Shiru ne ya biyo baya,tunanin abinda ya faru dazun gidan yaya yahanasu yayi nasarar wafce tunaninta ba tare da ta shirya ba,haka maman ta tadda ta,ta ajjiye kwanon dambun data je debo mata
"Lafiya dai ko sumayya" murmushin yaqe tayi ta janyo kwanon dambun tana budewa sannan tace
"Mama aure yaya mukhtar zai qara" maganar ta dan taba maman,tsakanin da d'a da mahaifi,tausayinta ta dinga ji yana ratsata,babu shakka abu ne mai wuya zama da kishiya a wannan zamanin,abu ne da har yau yaqi dadi a cikin gidajen aurenmu,ga yarinyar tata gwanar haquri da shegen zurfin ciki ce,amma duk da haka ta sani ba duka aka taru aka zama daya ba,duk abinda zata gaya mata a yanzu shi zai zame mata madubin dubawarta.
Murmushi maman tayi sannan tace
"Babu komai,ai namiji mijin mace hudu ne,Allah ne ya halasta masa,abinda nake son gaya miki kawai shine kada ki soma cewa zaki tada hankalinki ko ki daga hankalin mijinki,ki zauna da ita tsakani da Allah,ki sauke duk wani haqqi nata dake wuyanki,sumayya kada ki sake kice zaki cuceta,idan kika cuceta sumayya ni mahaifiyarki ban yafe miki ba".
Kai ta gyada" in sha Allahu mama zanyi duk abinda kika ce,da ikon Allah bazan zama mai sabawa maganarki ba"a hankali maman ta dinga hilatarta tana kwantar mata da hankali har ta kusa cinye dambun baki daya.
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_bismilla hir rahmanir rahim_
*inna ma'al usri yusrah,fa inna ma'al usri yusrah*
______________________
0⃣3⃣
Suna cikin hirar mukhatr ya turo qaninta mubarak yayi kiranta ta fito zasu tafi,nan mama ta hada mata su kuka kubaiwa daddawa barkono har da tsakin masara saboda dambu ko dan malele,tana hada mata kayan tana dada kwantar mata da hankali tare da jaddada mata kada ta sake ta tashi hankalin mijinta ko ita kanta,ko tace zata yi wani rashin kyautawa ga daya daga cikin 'yan uwan mukhtar,haihuwa kuwa lokaci ne,idan Allah yaso ma sai taga sanadiyyar shigowar wata ita ma ta samu nata rabon,ta dora da cewa
"Bare ma duka duka nawa kike sumayya,mu a da can Allah na tuba ba sai kiyi shekara goma da aure baki haihu ba babu wanda ya damu da ke,haka kema baki damu kanki ba,ci da zuci ne kawai yanzu irin na yaran zamani" maganar sai ta bama sumayya dariya da kunya,har ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta.
Suna shirin kwanciya bacci lokacin yana zaune gefan gadonsu yana shan ruwan baqin shayi,ita kuma tana taje kanta,ta cikin madubin yake qare mata kallo yadda kullum take sake zama cikakkiyar mace,tamkar ba zata masa magana ba amma abun nata cinta a zuciya,saboda daga shigowarsu gida zuwa shirin kwanciya da sukeyi yanzu yaya yahanasu ta kira shi ya kusa sau biyar,duk da bata kusa amma ta fahimci taqaddamar me suke,maganar lefe ne da yace ba zaya yi ba,ta dan cije lebanta sannan tace
"Ya mukhtar"
"Ya akayi sumy?" Ya fadi yana saurarenta.
Sai data jawo dressing chair gabansa ta zauna sannan ya dubeshi,cikin nutsuwar nan tata hadi da kaifin hankali da zurfin tunani
"Ya mukhtar kayi haquri idan na maka shishshigi,sai nake ganin baka kyauta ba",cikin rashin fahimta ya tambayeta
" da akayi me fa?"ta danyi jim kamar ba zata yi magana ba sannan tace
"A ganina bai kamata ka dinga sa'insa da yaya yahanasu ba,ko banza ta girmeka,bugu da qari ita ta zame maka tamkar mahaifiyarka ka manta?,ita ta raineka har ka kawo girmanka,ka san cewa dai ba zata taba yin abinda zai cutar da kai ba,a ganina auren nan saboda qaruwarka ne take buqatar kayi,ko babu komai idan fa'iza ta haihu sai an fara cewa danka kafin a ce dan yaya yahanasu ko?" Ta dan sarara da maganar tana hadiye wani abu mai daci wanda bata san meue sanadiyyar tasowarsa ba daga qirjinta.
Ko bata qarasa ba ya fahimci kan me take magana,saboda haka ya bata fuska
"Kinga sumayya,babu ruwanki da wannan maganar ki fita a cikinta,lefe ne nace bazanyi ba suyi mata,ai bani nace ina son auren ba ko?,ina zaman zamana haka kawai ina lallaba rayuwata sai su baro min aikin da bani na saka su ba?".
Kai take gyadawa idonta cikin nasa wanda tuni ya tara qwalla shirin zubowa kawai take
" na gode ya mukhatar,ina ka taba gani an auri budurwa ba'a yi mata lefe ba?bayan haka kuma ka riga da ka san cewa matuqar bakayi lefe ba to sumayya ce ta hanaka,duk wanda yaga laifina ko ya zageni ya mukhtar kai ka jawomin"sai ta tashi daga saman kujerar ta haye gado ta lulluba har saman kanta kaana ta fashe da kuka.
Har cikin ransa ya dinga jin shigar kukan nata,ya runtse ido yana jin bata can can ci haka ba,da me zata ji cikin abu ukun,sai ya sanya hannayeshi ya dagota baki daya zuwa jikinsa yana goge mata hawayen tare da fadin
"Ya isa sumayya,ya isa,me kike so ayi?,gaya min" sai da taja hanci kadan sannan tace
"Kayi lefe kamar yadda yaya yahanasu ta buqata"
"Shikenan an gama,sunci darajarki" sai ta saki dan qaramin murmushi sannan tace
"Na gode".
Washegari yana cikin karyawa kafin ya fita wayarsa ta soma ringing,sumayya ta dauko ta miqa masa da yake tana kan t.v stand tana chargy,daga yanayin maganarsa kawai ya tabbatar mata yaya yahanasu ce,kuma zancan jiya ne bai wuce ba,a gimtse ya amsa cewa zaiyi laifen,amma fa sam shi ba kudi zai bada ba,zaiyi iyakacin abinda zai iya ya kawo musu,daga haka ya kashe wayan ma baki daya,tana gefe tana saurarensu kanta sunkuye tana wasa da yatsun hannunta,ya kammala ta masa rakiya kamar yadda ta saba,dawowa yayi da baya ya rungumeta sannan ya sumbaci goshinta
" Allah yayi miki albarka"ya fada yana sakinta
"Amin ya mukhtar" ta fada cikin farinciki,saboda tuni maman ta ta gaya mata albarkar miji na bin mace,hakanan fushinsa ko yardarsa na tare da ta ubangiji.
Cike da farinciki ta koma cikin gidan saboda albarkar da ya sa mata ta faranta mata,taci gaba da kintsa ragowar ayyukan da suka rage mata,bata jima da kammalawa ba ta zauna tana hutawa wayarta ta dauki qara,da sauri ta daga ganin sunan abbanta na yawo bisa screen din wayar.
Cikin girmamawa ta gaidashi ya amsa mata yana tambayarta gida da kuma mukhtar tace ai yama fita.
"Mamanki ta gaya min mukhtar zai qara aure"
"Eh abba malam"
"To ina fata ba zaki watsa mana qasa a ido ba,ba za kiyi watsi da tarbiyyar da muka baki ba"
"In sha Allahu malam"
"To Allah ubangiji ya albarkaceki ya albarkaci aurenki" daga haka ya dora mata da nasiha cikin hikima da ilimi,cike da fadar Allah da ma'aikinsa,hakan ba qaramin sake kwantar mata da hankali yayi ba,ya qare nasihar tasa da fadin
"Babu wani abu da kike buqata?"
"Eh babu malam" ta fadi hakan saboda babu abinda mukhtar ya gaza da shi,don hatta kudin kashewa yakan qimanta ya bata,ya danganta da yanayin samun da yayi a kasuwa.
"To shikenan,haka ake so,inaga zan duba wajen sati na gaba ko wajejen satin sama,zan aiko abubakar(yayanta ne shine na fari a gidansu,amma baiyi aure ba karatu yake)zaizo. A fidda kayan gadonki da kujerunki a sauya miki wasu" farinciki ya cikata,duk da cewa wadan nan natan ma babu abinda sukayi,don sanda sukayi shekara hudu da aure mukhtar ya fitar da na aurenta na ainihi ya sauya mata su.
"Na gode,na gode qwarai malam Allah ya saka da alkhairi,ya qara lafiya da nisan kwana mai amfani,Allah ya qara budi da rufin asiri"
"Amin ya Allah,amma abinda zaki biyani da shi kawai kici gaba da zaman aure cikin gidanki"
"Da yardar Allah malam" ta amsa masa daga haka sukayi sallama.
Sosai malam yake aon sumayya,don tun tana mitsitsiyarta halayyarta daban take,tana da tarin haquri kawaici da zurfin ciki,shi yasa duk cikin yaransa yafi sonta,duk da cewar dukan yaran nasa maman sumayyan ce ta haifesu,ko a lokacin da suka aura mata mukhtar ma ce mata kawai yayi ga miji yayi mata kuma aure zaiyi mata,bata ce komai ba don ba wayo gareta ba,duk da haka dama kunya gareta,gudu tayi ma ta bar gurin sanda malam din ke gaya mata,ita ce yarinya mace ta farko a gurinsa sai qannenta su hudu.
Mukhtar zamu iya cewa rako wani abokinsa yayi gurin malam din kasancewar malam din yana bada karatu tsakanin sallar magariba da isha'i wa matasa da dattijan unguwa,gani daya ya yiwa sumayya yaji tayi masa kasancewarsa mutum wanda sam baya da sha'awar auren macen da tayi zurfi a karatu,tunda yayi universty shima yaga irin qazamar rayuwar da mafi yawancin 'yammatan keyi duk da ba duka aka taru aka zama daya ba.
To sara ne yazo kan gaba shima malam ba mai son yaransa suyi bokon bane,saboda haka yana bincike kan mukhtar ya tabbatar da nagartar halayyarsa ya basu auren sumayyan.