Sashe 146
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tsaye yake bayan ya fito daga wanka yana sanya kayan baccinsa,a gajiye yake matuqa,so yake ya kwanta ya huta hakanan ko qwaqwalwarsa zata samu irin hutun da yake fata,sashe daya na zuciyar nashi na masa tunanin me zaya bata taci kafin ta kwanta?,tilas dunsa ne cinta da shanta na a wuyanta,duk da ya tabbata baza a rasa abinci cikin gidan ba amma shi kam bazai tambaya a kawo din ba,mutum ne da tun asali ba mai roqo ba,hakanan baison roqo,dalili da yasa har yau yawan roqo irin na sy'ad ke bashi mamaki,a hankali ta tura qofar zuciyarta na bugawa tamkar zata fito waje,wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki ganinshi tsaye shi kadai sanye da kayan bacci,da gudu ta banko dakin wanda kafin ya kai ga waiwayowa ta ruqunqumeshi ta baya tana sakin kuka,bai ce mata uffan ba bai kuma juyowa ba,saidai yana sauraren sautin kukan da take fitarwa,tuni kukan ya soma hawa masa ka,ta sani ya tsani kuka amma hakan bai hanata rerashi ba aduk sanda tayi niyya,da faru baiyi niyyar lallashinta ba ko kadan saboda maganganun data gaya mishin dazu,amma tunawa da yayi yasha jin mata na fadin irin qunci da bacin ran da suke fuskanta takura da kuma kishi shi ya sanya shi zagaya hannunshi ya dawo da ita gabanshi suna fuskantar juna sannan ya zaunar da ita gefan gado kafin shima ya zauna,hakan yayi mata kyau da dadi qwarai,zuciyarta ta shiga gaya mata cewa ba shakka tana da nasara
"Ya kamata ki nutsu kiyi controlling kanki,aurena bai nufin konai zai sauya tsakanina da ke"cikin sheshsheqar kuka tace
"Almustapha,wallahi bazan iya zama da kowacce diya mace ba amatsayin wai itama matarka ce bazan iya ba wallahi,ya zama tilas ka saketa wannan dole ne" fubanta yake yana qoqarin controlling kansa jin yadda take bashi umarni kai tsaye tamkar uta din ita tayi naqudarsa kafin daga bisani yace
"Look su'ad,bana so ki sake tada wannan magana,kada ki sake ambaton saki cikin maganarki don babu shi duka ciki qwaqwalwata,ki iya bakinki ki san me zaki furta" ba qaramin hasalata kalaman sukayi ba,tuni zuciyarta ta dinga gaya mata tsananin sonta yake,qaunarta yake shi ya sanya har yake gaya miki hakan a kanta,take kalaman mom dinta suka fado mata na kada ta ragawa kowa,tayi hauka sosai don ta qwatarwa kanta 'yanci,miqewa tayi tsaye tana qanqan da idanunta,hannayenta riqe a qugunta,karo na farko data shirya kallon tsabar qwayar idanunshi ta masa rashin kunya
"Ai dama namiji ba dan goyo bane,gaskiya mana naji kidahuman matan africa na fadin haka,mu dama mun jima da sanin haka,to wallahi almustapha bari na gaya maka wani abu,duk eani qulla qulla da munafuncin da aka hada kan auren nan tilas ya rabu,don ni bazan taba zama da kishiya ba wallahi bata isa na hada miji da ita ba,wallahi dole ka saketa idan ba haka ba zan dauki mafi munin mataki wanda bazaiw kowa dadi ba,zan iya kashe...." Wata gigitacciyar tsawa ya daka mata wadda ta sanya ta yin shiru,cikim zafi da fushi wanda suka bayyana muraran a fuskarshi ya soma nuna ta da yatsa
"Kada bakinki yayi ganganci ko kuskuren zagar min iyaye,idan kuwa kika aikata hakan ki lissafashi cikin ganganci na farko da kika taba yi cikin rayuwarki" cikin tsiwa da bushewar zuciya tace
"A daki mutum a hanashi kuka,na fuskanci almustapha baka qaunata har yanzu?"cikin fushi da son cusa haushi shima yace
" ke sai yau kika sani?"baki ta saki galala tana dubanshi hawaye na malala bisa kuncinta,q maimakon ya qasqantar da kai ya lallasheta shine yake gaya mata wannan baqar kalmar da ya raba fada mata can wasu shekaru baya da shka wuce,tuni ya miqe yaci gaba da daura zaren kayan baccin dake jikinsa,kai ta shiga girgizawa zuciya na tunzurata,juyawa tayi ta sauka qasa da gudu,yabi bayanta da kallo yana jan wani mugun tsaki,kai tsaye kitchen ta nufa ta zari daya daga cikin setin wuqaqenta wadda sabuwa ce dal,bata taba amfani da ita ba kasancewar babu abinda ta taba shiga kitchen din tayi tunda aka tanadar mata sji,saidai ta karbo musu koma meye wajensu umme in har ma tazo qasar,saman ta koma ta banka qofar dakin sanda yake qoqarin zama gefan gadon ta qaraso gabansa ta tsaya
"Almustapha,wallahi gwara na kashe kaina da naci gaba da sauraron kalaman qi daga gareka,gwara na kashe kaina dana zauna da wata" ta fada tana daga wuqar da niyyar dabawa cikinta,cikin wani irin zafin nama ya sanya hannunshi ya riqe wuqar,wanda hakan yayi sanadiyyar yankewarsa jini ya soma diga,bai kula da wannan ko ya damu ba,don ya lura su'ad mahaukaciya ce wadda aqidar yahudawa ta gama ratsata,wannan shine karo na biyu da tayi yunqurin hallaka kanta saboda shi
"Ke wacce iriyar dabba ce mara hankali,shashashar banza mahaukaciya kawai"zuge wuqar tayi daga hannunshi wanda zafin sai da ya ratsashi har cikin kwanyarsa
"Kome zaka fada saidai ka fada,amma almustapha amma yau ko ban kashe kaina ba zanje na kasheta idan yaso nima a kasheni" ta fada tana juyawa da sauri ba tare data damu da ciwon data ji masa ba,da hanzari ya fincota tana waiwayowa zata sauke masa rashin kunya ya zabgeta da wani irin lafiyayyen mari daya tarwatsa tsarin qwaqwalwarta sannan ya hankadata ta fada saman gado,yasanya qafarshi ya take hannunta wanda hakan ya tilasta mata sakin wuqar ya zareta
"Ban taba dana sanin saninki ba su'ad sai yau,ashe ke din ba mutum bace har kike ikirarin kashe kanki ki kashe wani?,banza wawiya kawai mara hankali" ya fada yana nufar qofa zai fice,wannan ya watstsakar da ita daga marin da yayi mata ta yunqura tana fadin maganganu cikin ihu da zummar binsa,tuni ya fice dauke da wuqar,ya sanya key ya rufe qofar sannan ya qarasa kan kujerun falon ha zaune yana dunqule da tafin hannunsa,yana iya jiyo surutanta wani cikin hausa wani cikin harshen nasara tana bugun qofar,daga bisani ya dinga ji qara ta gilasai wanda da alama barna ta soma masa cikin dakin,hakane kuwa,don duk wani glass na dakin ka daga t.v palsma,mirrow,bedside lamp babu wanda bata hada ta kwankwatse ba,cikinbqanqanin lokaci itama ta jiwa kanta ciwo,zuciya ke tunzurashi ya bude qofar ya shiga yayi mata dukan kawo wuqa yana qoqarin danne fushinsa,ya tabbatar idan yaci gaba da zama komai zai iya faruwa,zai iya gaza ci gaba da yin haquri ya bude dakin wanda ya tabbata gamuwarsu a wannan lokacin bazai haifar da d'aa mai ido ba,hakan ya sanyashi ya miqe ya gwammace ya sauko qasa,don baiga abinda zai kashi nata dakin ba.
Kwance take lamo bisa gadon nata tana iya jiyo hargowa saman gidan,tuni ta dauke muryar su'ad ta kuma tabbatar itace,fargaba da tsoron irin hayaniyar data dinga ji ita ta kamata,sannu a hankali ta dinga kiran sunayen Allah,sannu sannu fargabarta da tsoronta suka gushe,kalaman anty dije suka dawo mata sanda zata taho abuja
"Idan har su'ad ta tsorataki kinyi asara,wacce kalar kishiya ce baki gani ba,kada ki yadda ki kasa kyautatawa mijinki saboda wata,zaku taru ne dukanku ku zama daya,don qwace goruba hannun kuturu ba abu bane mai wuya,samun almstapha a tafin hannunki saidai idan baki so ba" tabbas haka maganar anty take,ya kamata zuwa yanzu ace ta tsike,ya kamaceta ace ta fara qwatar 'yancinta hannun kishiya,su dinma fa mata ne kamarta,don me zata zauna suna garata daga wannan waje zuwa wannan?,akanme zata zuba musu ido su dinga yin yadda suka ga dama da rayuwarta,'yanci shi take buqata wannan karon,ta kuma bawa kanta tabbaci da qwarin gwiwar tabar bari ana cutarta yadda itama ba zata cuci kowa ba to a zauna lafiya,tana buri da fatan wannan ya zame mata gidanta na qarshe koda banu soyayya da shaquwa tsakaninta da mai gidan,amma akwai da dama masu zamansun a haka girmamawa da kyautatawa ita ke musu jagora.
Sallamar data ji cikin falon nasu anata yi ita ta sanyata miqewa ba tare da shayi ko fargaba ba ta zira hijabinta ta bude qofan ta fito,biyu daga cikin ma'aikatan gidan ne dauke da kwanduna guda biyu,cikin girmamawa suka dan rusuna wanda hakan ya bata kunya suna gabatar da kansu sannan suka ce
"Abincin dare ne maamaa tace a kawo muku,wannan kwandon abincin yallabai ne,saidai ummee tace don Allah a sashi yaci kada yasha coffee yace zaya zauna haka" murmushi ya subuce mata wanda hakan ya bayyana fararen haqoranta,kunyar ummeen ta kamata duk da bata wajen,masar kwandunan tayi tana cewa ayi musu godiya da sannu,shka juya suka fice zucuyarsu fal mamaki da murna,ganin sauyi muraran yau a sashen yallabai,abinda ba'a taba yi musu ba,sau tari idan suka kawo abincin ma tana yatsina zata sanyasu su shiryashi saman tebur,idan kuma bai mata ba tana masifa zata basu umarnin abinda zasu dafa din komai dare.
"Ya kamata ki nutsu kiyi controlling kanki,aurena bai nufin konai zai sauya tsakanina da ke"cikin sheshsheqar kuka tace
"Almustapha,wallahi bazan iya zama da kowacce diya mace ba amatsayin wai itama matarka ce bazan iya ba wallahi,ya zama tilas ka saketa wannan dole ne" fubanta yake yana qoqarin controlling kansa jin yadda take bashi umarni kai tsaye tamkar uta din ita tayi naqudarsa kafin daga bisani yace
"Look su'ad,bana so ki sake tada wannan magana,kada ki sake ambaton saki cikin maganarki don babu shi duka ciki qwaqwalwata,ki iya bakinki ki san me zaki furta" ba qaramin hasalata kalaman sukayi ba,tuni zuciyarta ta dinga gaya mata tsananin sonta yake,qaunarta yake shi ya sanya har yake gaya miki hakan a kanta,take kalaman mom dinta suka fado mata na kada ta ragawa kowa,tayi hauka sosai don ta qwatarwa kanta 'yanci,miqewa tayi tsaye tana qanqan da idanunta,hannayenta riqe a qugunta,karo na farko data shirya kallon tsabar qwayar idanunshi ta masa rashin kunya
"Ai dama namiji ba dan goyo bane,gaskiya mana naji kidahuman matan africa na fadin haka,mu dama mun jima da sanin haka,to wallahi almustapha bari na gaya maka wani abu,duk eani qulla qulla da munafuncin da aka hada kan auren nan tilas ya rabu,don ni bazan taba zama da kishiya ba wallahi bata isa na hada miji da ita ba,wallahi dole ka saketa idan ba haka ba zan dauki mafi munin mataki wanda bazaiw kowa dadi ba,zan iya kashe...." Wata gigitacciyar tsawa ya daka mata wadda ta sanya ta yin shiru,cikim zafi da fushi wanda suka bayyana muraran a fuskarshi ya soma nuna ta da yatsa
"Kada bakinki yayi ganganci ko kuskuren zagar min iyaye,idan kuwa kika aikata hakan ki lissafashi cikin ganganci na farko da kika taba yi cikin rayuwarki" cikin tsiwa da bushewar zuciya tace
"A daki mutum a hanashi kuka,na fuskanci almustapha baka qaunata har yanzu?"cikin fushi da son cusa haushi shima yace
" ke sai yau kika sani?"baki ta saki galala tana dubanshi hawaye na malala bisa kuncinta,q maimakon ya qasqantar da kai ya lallasheta shine yake gaya mata wannan baqar kalmar da ya raba fada mata can wasu shekaru baya da shka wuce,tuni ya miqe yaci gaba da daura zaren kayan baccin dake jikinsa,kai ta shiga girgizawa zuciya na tunzurata,juyawa tayi ta sauka qasa da gudu,yabi bayanta da kallo yana jan wani mugun tsaki,kai tsaye kitchen ta nufa ta zari daya daga cikin setin wuqaqenta wadda sabuwa ce dal,bata taba amfani da ita ba kasancewar babu abinda ta taba shiga kitchen din tayi tunda aka tanadar mata sji,saidai ta karbo musu koma meye wajensu umme in har ma tazo qasar,saman ta koma ta banka qofar dakin sanda yake qoqarin zama gefan gadon ta qaraso gabansa ta tsaya
"Almustapha,wallahi gwara na kashe kaina da naci gaba da sauraron kalaman qi daga gareka,gwara na kashe kaina dana zauna da wata" ta fada tana daga wuqar da niyyar dabawa cikinta,cikin wani irin zafin nama ya sanya hannunshi ya riqe wuqar,wanda hakan yayi sanadiyyar yankewarsa jini ya soma diga,bai kula da wannan ko ya damu ba,don ya lura su'ad mahaukaciya ce wadda aqidar yahudawa ta gama ratsata,wannan shine karo na biyu da tayi yunqurin hallaka kanta saboda shi
"Ke wacce iriyar dabba ce mara hankali,shashashar banza mahaukaciya kawai"zuge wuqar tayi daga hannunshi wanda zafin sai da ya ratsashi har cikin kwanyarsa
"Kome zaka fada saidai ka fada,amma almustapha amma yau ko ban kashe kaina ba zanje na kasheta idan yaso nima a kasheni" ta fada tana juyawa da sauri ba tare data damu da ciwon data ji masa ba,da hanzari ya fincota tana waiwayowa zata sauke masa rashin kunya ya zabgeta da wani irin lafiyayyen mari daya tarwatsa tsarin qwaqwalwarta sannan ya hankadata ta fada saman gado,yasanya qafarshi ya take hannunta wanda hakan ya tilasta mata sakin wuqar ya zareta
"Ban taba dana sanin saninki ba su'ad sai yau,ashe ke din ba mutum bace har kike ikirarin kashe kanki ki kashe wani?,banza wawiya kawai mara hankali" ya fada yana nufar qofa zai fice,wannan ya watstsakar da ita daga marin da yayi mata ta yunqura tana fadin maganganu cikin ihu da zummar binsa,tuni ya fice dauke da wuqar,ya sanya key ya rufe qofar sannan ya qarasa kan kujerun falon ha zaune yana dunqule da tafin hannunsa,yana iya jiyo surutanta wani cikin hausa wani cikin harshen nasara tana bugun qofar,daga bisani ya dinga ji qara ta gilasai wanda da alama barna ta soma masa cikin dakin,hakane kuwa,don duk wani glass na dakin ka daga t.v palsma,mirrow,bedside lamp babu wanda bata hada ta kwankwatse ba,cikinbqanqanin lokaci itama ta jiwa kanta ciwo,zuciya ke tunzurashi ya bude qofar ya shiga yayi mata dukan kawo wuqa yana qoqarin danne fushinsa,ya tabbatar idan yaci gaba da zama komai zai iya faruwa,zai iya gaza ci gaba da yin haquri ya bude dakin wanda ya tabbata gamuwarsu a wannan lokacin bazai haifar da d'aa mai ido ba,hakan ya sanyashi ya miqe ya gwammace ya sauko qasa,don baiga abinda zai kashi nata dakin ba.
Kwance take lamo bisa gadon nata tana iya jiyo hargowa saman gidan,tuni ta dauke muryar su'ad ta kuma tabbatar itace,fargaba da tsoron irin hayaniyar data dinga ji ita ta kamata,sannu a hankali ta dinga kiran sunayen Allah,sannu sannu fargabarta da tsoronta suka gushe,kalaman anty dije suka dawo mata sanda zata taho abuja
"Idan har su'ad ta tsorataki kinyi asara,wacce kalar kishiya ce baki gani ba,kada ki yadda ki kasa kyautatawa mijinki saboda wata,zaku taru ne dukanku ku zama daya,don qwace goruba hannun kuturu ba abu bane mai wuya,samun almstapha a tafin hannunki saidai idan baki so ba" tabbas haka maganar anty take,ya kamata zuwa yanzu ace ta tsike,ya kamaceta ace ta fara qwatar 'yancinta hannun kishiya,su dinma fa mata ne kamarta,don me zata zauna suna garata daga wannan waje zuwa wannan?,akanme zata zuba musu ido su dinga yin yadda suka ga dama da rayuwarta,'yanci shi take buqata wannan karon,ta kuma bawa kanta tabbaci da qwarin gwiwar tabar bari ana cutarta yadda itama ba zata cuci kowa ba to a zauna lafiya,tana buri da fatan wannan ya zame mata gidanta na qarshe koda banu soyayya da shaquwa tsakaninta da mai gidan,amma akwai da dama masu zamansun a haka girmamawa da kyautatawa ita ke musu jagora.
Sallamar data ji cikin falon nasu anata yi ita ta sanyata miqewa ba tare da shayi ko fargaba ba ta zira hijabinta ta bude qofan ta fito,biyu daga cikin ma'aikatan gidan ne dauke da kwanduna guda biyu,cikin girmamawa suka dan rusuna wanda hakan ya bata kunya suna gabatar da kansu sannan suka ce
"Abincin dare ne maamaa tace a kawo muku,wannan kwandon abincin yallabai ne,saidai ummee tace don Allah a sashi yaci kada yasha coffee yace zaya zauna haka" murmushi ya subuce mata wanda hakan ya bayyana fararen haqoranta,kunyar ummeen ta kamata duk da bata wajen,masar kwandunan tayi tana cewa ayi musu godiya da sannu,shka juya suka fice zucuyarsu fal mamaki da murna,ganin sauyi muraran yau a sashen yallabai,abinda ba'a taba yi musu ba,sau tari idan suka kawo abincin ma tana yatsina zata sanyasu su shiryashi saman tebur,idan kuma bai mata ba tana masifa zata basu umarnin abinda zasu dafa din komai dare.