Sashe 49
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana kitchen tana hada girkin duk da wasu kayan buqatun babu,mamaki da tunani fal ranta,a haka taji sallamar hajiyan,ta juya tana amsa mata,qarasowa hajiyan tayi ta kama hannun sumayya kamar zata saki kuka
"Kiyi haquri sumayya da abinda nayi miki dazu,yarinyar nan idan ta umarcemu da abu daga ni har lukman bama iya musa mata,amma nasan alhakin yaran jama'a ne yake bibiyata,haka kawai naji kin kwanta min sumayya zan gaya miki wace ni me na aikata ga rayuwata da rayuwar yarona"
Kafin sumayyan tace wani abu tuni hajiya ta fara bata labarin dukka aure auren da lukman yayi wanda ita ce sila,da fari haushin hajiyan ta dinga ji,amma daga bisani sai tausayinta ita da lukman ya baibayeta baki daya,tabbas abu na farko data fuskanta ya janyo wannan matsalar sakaci da rashin riqe ubangiji hannu bibbiyu,har qwalla sai data yiwa hajiya da lukman din saboda aikin kariman ya shallake hankali.
Cikin sanyin jiki ta riqe hannun hajiyan ganin tana zubda qwalla
"Kiyi haquri hajiya ki fawwalawa Allah lamarinki,ba shakka inna idan ma alhakin ne ba mamaki,Allah na sonki shi yasa zai hukunta ki tun a duniya,din hukuncin lahira da shi gwara na duniya sau babu adadi,in sha Allahu ni zanyi iya bakin qoqarina wajen ganin na daidaita lamarin iya abinda Allah ya huwace min,ina so daga yau kisa a ranki ba zaki qara jin tsoron karima ba,ba zaki sake bin umarninta ba sai abinda ya dace shi zakiyi,a duk sanda kika ganta idan kika ji faduwar gaba ko tsoro ki karanta ALLAHUMMAKH FINIHIM BIMA SHI'ITA matakin farko kenan,sannan daga yau kada ki sake cin duk abinda ya fito daga hannunta,ki umarci lukman ya kawo miki kayan abincinki a zuwan zaki ci gaba da girki,ni kuma in sha Allahi zanci gaba da dafa miki" kai take gyadawa cike da gamsuwa tana jin tamkar damuwarta na gab da yayewa
"Sannan lukman danki ne hajiya,bakin uwa kaifi gareshi,ki dage da yi masa addu'a,Allah ya yaye masa bala'in da ya fada ta sanadin abinda ke kika aikata shi,bashi kadai ba,har ke dinma saikin dage da addu'a wa kanki na neman tsari"
Kai ta sake jinjinawa
"Har na manta rabon da na sashi a addu'a ta,na gode da tunatar da ni da kikayi,na gode sosai"
"Sannan hajiya,kinsan rayuwar da nuwaira take cikin gida kuwa?" Ta tabo inda yafi mata qaiqayi
"Na sani sumayya na sani,saidai bani da ikon magana bani da ikon gyarawa" ta fada cikin jimami,don har ga Allah duk cikin jikokinta tafi qaubarta,din ta fita daban a cikinsu,nutsuwarta da komai da komai,shiru sumayyan tayi sannan tace
"Babu komai,zanyi iya bakin qoqarina itama akanta kafin Allah ya kawo qarshen lamarin"
"Na gode sumayya na gode,haqiqa kin zamo *HASKE* cikin gidan d'ana cikin kwana daya tal,ina miki fatan alheri sannan kuma ina miki fatan samun nasara,Allah ya albarkaci rayuwarki da alkhairi masu tarin yawa,ya tsareki" amin sumayya ta dinga cewa tana jin dadin addu'ar har cikin ranta,ko da can ita din mai son wani na gaba da ita ne ya albarkaceta,kusan tare suka gama aikin ta kammalewa hajiyan cikin kula yadda tasan zai ishesu ita da nuwaira,tace zata turo mata ita taci na rana dana dare,don ta lura bata samu albarakacin cin na safe ba,sai na hajiyan da suka yayyafita.
Nan tayi zamanta gun hajiya,ita kanta hajiyan sai ta dinga jin dadi cikin ranta,nuwaira ma ta dinga sato jiki tana leqowa har sanda sumayyan ta koma bangarensu.
***** ****** ******
Cikin kwanaki hudu rak sumayya ta gama dukkan wani shiri nata na tunkarar wakeken qalubalen data fuskanci yana danqare a gidan,ita kanta mamakin kanta take yadda zuciyarta ta taurare baki daya har take ganin zata qalubalanci karima wadda baki daya ta rusa rayuwar gidan ta dora ta kan turbar da take so,sam sam yaranta irin yaran nan marasa tarbiyya ko qanqani,su zagi babba duk girmansa ba komai bane a gunsu,sam sam sumayya bata shiga shirginsu ko sakar muau fuska tunda ta fuskanci inda tarbiyyarsu tasa gaba,hakan ya sanya suka fara shakkarta,sai kuma mai biwa babbar da ta soma son kula sumayya,sau tari takan qwanqwasa qofarta idan ta bude mata tace ta shigo kuma sai taqi,sai ta fuskanci shakkar mamarta take,hakan ya sanya ita sumayyan ta fara qoqarin janyota a jiki,ga shegen gulma munafunci da iya kawo labari,hatta da mahaifinsu suna iya dauko gulmarsa su kawo mata ita kuma ta tuhumeshi kan haka,sumayyan na sha'awar hatta da tarbiyyar yaran ta saisaita musu ita,don ta kula sam daga makarantar boko babu kuma wata makaranta ta biyu da yaran ke zuwa wadda ake kira da makarantar addini ko islamiyya,baki daya idan ka dauke sumayya banu mai rayuwa kan ra'ayinsa sai abinda ta shinfida,tun abun na bawa sumayya haushi har ya koma bata tausayi,ita sam ma baki daya bata ta angon ko kadan,wanda zuwa yanzu hatta lokacin fita da dawowarsa gida karima ta sauya masa duk don kada su hadu da sumayyan,ta saka an qara narka masa aikin mantau akan sumayya wadda ko gefen silifas dinta lukman din ma baije ba,sau tari takan tambayi kanta me yasa ta auri lukman sai ta rasa dalili,amsa daya ke zuwa kanta
"Qila don kizo ki ceci rayuwar 'yar gidan ne" ita kanta tafi gamsuwa da wannan ce sahihiyar amsar
****** ******* *******
Cikin satittika qalilan shaquwa ta fara shiga tsakaninta da hajiya,kusan koda yaushe can take wuni,ta yima haijan aikace aikace sannan suyi girkinsu abinsu,sannu a hankali sauyi ya fara samuwa tattare da hajiyan,sumayya ta zaburar da ita ta kuma koya mata addu'o'i sosai,rana ta farko da suka fara fuskantar zuwan sauyi shine randa kariman ta shigo da abincinta wanda aka saba sanwa hajiyan don bazance bata ba,duk da hajiyan ta jima bata ci amma sumayya tace ta dinga karba kada ta gaya mata idan yaso saita dinga bayarwa,tunda ta shigo ta lura hajiyan sam bata rawar qafa yadda ta saba idan ta shigo gunta,abu na biyu tana jiran taga hajiyan ta gaidata yadda ta saba sai taga tayi fuska,ta maida hankalinta gun sumayya dake shafa mata man zafi a gwiwarta data riqe mata take mata ciwo,wanda abaya bata da wannan gatan saidai taci ciwonta ta warke don dolenta.
Kanta yayi masifar daurewa,abu na farko da yazo kanta aikin hajiyan ya fara sako sako don dama kwana biyu tafi maida kai a kan lukman din
"Ga abinci nan" kariman ta fada a wulaqance,juyowa hajiyan tayi tana duban flask din ranta cike da takaicin yadda ma ta dinga karbar wannan abincin
"Wai ni?,ai da kinyi gaba da abinki don na jima banci abincinku ba,'yata na girkamin kullum" ta fada tana duban sumayya,take tsoro ya shigi karima,ashe tayi sake har haka?,ashe fa diyar malamai wannan karon lukman ya kwaso mata,lallai ba shakka shi yasa taga bata taba tambayar abincinta ba a gidan duk yadda ta sha alwashi akan yi mata kaca kaca duk sanda ta tambayi a bata abinci.
Hankalinta tashe ta fito daga bangaren ciken da tsoron lallai idan ta gama da hajiya babu shakka lukman zata dawowa,kacibus sukayi da nuwaira wadda ke dawowa daga gidan kitso da sumayya ta turata tayi saboda ba zata iya mata ba jiya ta yanke da wuqa a hannunta,baki ta saka tana duban nuwairan yadda ta canza cikin sati biyu kacal da kariman tayi bata nan,ta tilasta lukman ya biya musu umra ita da shi don har sai da yaci bashin wajen dubu dari biyar sannan ya cika musu,su kuma yaranta da zata tafi ta tattarasu ta maida su gidan iyayenta ta bar nuwaira ko oho,don dama ta saba yi mata irin hakan,tsoro ya kama nuwairan sai ta rabe gefe sannan ta tattakura ta sheqa da gudu sai bangaren hajiya,don kayan dake jikinta na waccar sallar ne shekara uku da dinka su,bata barinta ta sanya su sai wani abun ya tashi duk da cewa suna da lodin kaya harda wanda bata taba sawa ba ma sababbi,ta riga ta saba kayanta koda yaushe haka suke tamkar tsummokara,a haka ma sai an bata umarnin wadansa zata saka,bayan 'yan uwanta kullum cikin saka mai kyau suke.
Bata bi ta kan nuwaira ba don ba ita ce yanzu a gabanta,bangarenta ta wuce hankalinta a matuqar tashe,tabbas lallai babu shakka idan batayi wani abu ba ta lura duniyar rayuwarta gab take da girgiza koma rugujewa baki daya,dole ne gidan ya koma yadda yake,dole kowa ya koma yadda take so ciki kuwa harda sumayyan
****** ******* ******
Tunda ya karbeshi kusan shi ua zame masa uwa da uba baki daya,yana matuqar debe masa kewa,yana sanyashi nishadi,wata qauna ta yaron nasa yake ji cikin jikinsa da jininsa,sau tari ya kanyi mamakin kansa yadda yake zama yayita kallon abdallan kamar babu gobe,babu yadda yaya yahansu batayi ba akan ya bata shi amma ya qiya,ya bata haquri don bazai iya bata shi din ba.
Da safe tare suke shiryawa ya bashi abinci su fita kasuwa tare da shi,zuwa azahar zai bar kasuwa ya dan fita da shi su zaga gari su dawo da la'asar,qarfe shida subar kasuwa su dawo gida,har gado ya siya na yara ya sanya masa can cikin shagon,nan ma idan sun dawo sunyi wanka sannan suci takeaway din da ya tsaya hanya yayo musu,daga nan ya zube masa kayan wasansa yana tayashi yana kallon t.v har yaron yayi bacci,wani lokaci yakan bata lokaci saman abun sallah yana wa yaron nasa addu'a tare da yiwa kansa,wanda hakan ya sake samarwa da ruhinsa nutsuwa,shikewa Abdallahn komai,dai dai da rana guda mukhtar bai taba jin ya qosa koya gajiya ba,kai kanka idan ka kalli yaron ba zakayi zaton bai tare da mahaifiyarsa ba,kusan kullum sabon kayan mukhtar zai sanya masa,ado yake masa sosai,hakanan idan shadda zaya sanya ko yadi anko suke abinsu,duk wanda ya gansu a hanya zasu burgeshi,wata qauna ta musamman ce tsakanin d'a da ubansa,wani lokaci idan ya soma rigiman mamansa sai ya kaishi gunsu halima ya wuni don bai iya barinsa ya kwana,da dare yazo ya dauki abinsa su wuce.
"Kiyi haquri sumayya da abinda nayi miki dazu,yarinyar nan idan ta umarcemu da abu daga ni har lukman bama iya musa mata,amma nasan alhakin yaran jama'a ne yake bibiyata,haka kawai naji kin kwanta min sumayya zan gaya miki wace ni me na aikata ga rayuwata da rayuwar yarona"
Kafin sumayyan tace wani abu tuni hajiya ta fara bata labarin dukka aure auren da lukman yayi wanda ita ce sila,da fari haushin hajiyan ta dinga ji,amma daga bisani sai tausayinta ita da lukman ya baibayeta baki daya,tabbas abu na farko data fuskanta ya janyo wannan matsalar sakaci da rashin riqe ubangiji hannu bibbiyu,har qwalla sai data yiwa hajiya da lukman din saboda aikin kariman ya shallake hankali.
Cikin sanyin jiki ta riqe hannun hajiyan ganin tana zubda qwalla
"Kiyi haquri hajiya ki fawwalawa Allah lamarinki,ba shakka inna idan ma alhakin ne ba mamaki,Allah na sonki shi yasa zai hukunta ki tun a duniya,din hukuncin lahira da shi gwara na duniya sau babu adadi,in sha Allahu ni zanyi iya bakin qoqarina wajen ganin na daidaita lamarin iya abinda Allah ya huwace min,ina so daga yau kisa a ranki ba zaki qara jin tsoron karima ba,ba zaki sake bin umarninta ba sai abinda ya dace shi zakiyi,a duk sanda kika ganta idan kika ji faduwar gaba ko tsoro ki karanta ALLAHUMMAKH FINIHIM BIMA SHI'ITA matakin farko kenan,sannan daga yau kada ki sake cin duk abinda ya fito daga hannunta,ki umarci lukman ya kawo miki kayan abincinki a zuwan zaki ci gaba da girki,ni kuma in sha Allahi zanci gaba da dafa miki" kai take gyadawa cike da gamsuwa tana jin tamkar damuwarta na gab da yayewa
"Sannan lukman danki ne hajiya,bakin uwa kaifi gareshi,ki dage da yi masa addu'a,Allah ya yaye masa bala'in da ya fada ta sanadin abinda ke kika aikata shi,bashi kadai ba,har ke dinma saikin dage da addu'a wa kanki na neman tsari"
Kai ta sake jinjinawa
"Har na manta rabon da na sashi a addu'a ta,na gode da tunatar da ni da kikayi,na gode sosai"
"Sannan hajiya,kinsan rayuwar da nuwaira take cikin gida kuwa?" Ta tabo inda yafi mata qaiqayi
"Na sani sumayya na sani,saidai bani da ikon magana bani da ikon gyarawa" ta fada cikin jimami,don har ga Allah duk cikin jikokinta tafi qaubarta,din ta fita daban a cikinsu,nutsuwarta da komai da komai,shiru sumayyan tayi sannan tace
"Babu komai,zanyi iya bakin qoqarina itama akanta kafin Allah ya kawo qarshen lamarin"
"Na gode sumayya na gode,haqiqa kin zamo *HASKE* cikin gidan d'ana cikin kwana daya tal,ina miki fatan alheri sannan kuma ina miki fatan samun nasara,Allah ya albarkaci rayuwarki da alkhairi masu tarin yawa,ya tsareki" amin sumayya ta dinga cewa tana jin dadin addu'ar har cikin ranta,ko da can ita din mai son wani na gaba da ita ne ya albarkaceta,kusan tare suka gama aikin ta kammalewa hajiyan cikin kula yadda tasan zai ishesu ita da nuwaira,tace zata turo mata ita taci na rana dana dare,don ta lura bata samu albarakacin cin na safe ba,sai na hajiyan da suka yayyafita.
Nan tayi zamanta gun hajiya,ita kanta hajiyan sai ta dinga jin dadi cikin ranta,nuwaira ma ta dinga sato jiki tana leqowa har sanda sumayyan ta koma bangarensu.
***** ****** ******
Cikin kwanaki hudu rak sumayya ta gama dukkan wani shiri nata na tunkarar wakeken qalubalen data fuskanci yana danqare a gidan,ita kanta mamakin kanta take yadda zuciyarta ta taurare baki daya har take ganin zata qalubalanci karima wadda baki daya ta rusa rayuwar gidan ta dora ta kan turbar da take so,sam sam yaranta irin yaran nan marasa tarbiyya ko qanqani,su zagi babba duk girmansa ba komai bane a gunsu,sam sam sumayya bata shiga shirginsu ko sakar muau fuska tunda ta fuskanci inda tarbiyyarsu tasa gaba,hakan ya sanya suka fara shakkarta,sai kuma mai biwa babbar da ta soma son kula sumayya,sau tari takan qwanqwasa qofarta idan ta bude mata tace ta shigo kuma sai taqi,sai ta fuskanci shakkar mamarta take,hakan ya sanya ita sumayyan ta fara qoqarin janyota a jiki,ga shegen gulma munafunci da iya kawo labari,hatta da mahaifinsu suna iya dauko gulmarsa su kawo mata ita kuma ta tuhumeshi kan haka,sumayyan na sha'awar hatta da tarbiyyar yaran ta saisaita musu ita,don ta kula sam daga makarantar boko babu kuma wata makaranta ta biyu da yaran ke zuwa wadda ake kira da makarantar addini ko islamiyya,baki daya idan ka dauke sumayya banu mai rayuwa kan ra'ayinsa sai abinda ta shinfida,tun abun na bawa sumayya haushi har ya koma bata tausayi,ita sam ma baki daya bata ta angon ko kadan,wanda zuwa yanzu hatta lokacin fita da dawowarsa gida karima ta sauya masa duk don kada su hadu da sumayyan,ta saka an qara narka masa aikin mantau akan sumayya wadda ko gefen silifas dinta lukman din ma baije ba,sau tari takan tambayi kanta me yasa ta auri lukman sai ta rasa dalili,amsa daya ke zuwa kanta
"Qila don kizo ki ceci rayuwar 'yar gidan ne" ita kanta tafi gamsuwa da wannan ce sahihiyar amsar
****** ******* *******
Cikin satittika qalilan shaquwa ta fara shiga tsakaninta da hajiya,kusan koda yaushe can take wuni,ta yima haijan aikace aikace sannan suyi girkinsu abinsu,sannu a hankali sauyi ya fara samuwa tattare da hajiyan,sumayya ta zaburar da ita ta kuma koya mata addu'o'i sosai,rana ta farko da suka fara fuskantar zuwan sauyi shine randa kariman ta shigo da abincinta wanda aka saba sanwa hajiyan don bazance bata ba,duk da hajiyan ta jima bata ci amma sumayya tace ta dinga karba kada ta gaya mata idan yaso saita dinga bayarwa,tunda ta shigo ta lura hajiyan sam bata rawar qafa yadda ta saba idan ta shigo gunta,abu na biyu tana jiran taga hajiyan ta gaidata yadda ta saba sai taga tayi fuska,ta maida hankalinta gun sumayya dake shafa mata man zafi a gwiwarta data riqe mata take mata ciwo,wanda abaya bata da wannan gatan saidai taci ciwonta ta warke don dolenta.
Kanta yayi masifar daurewa,abu na farko da yazo kanta aikin hajiyan ya fara sako sako don dama kwana biyu tafi maida kai a kan lukman din
"Ga abinci nan" kariman ta fada a wulaqance,juyowa hajiyan tayi tana duban flask din ranta cike da takaicin yadda ma ta dinga karbar wannan abincin
"Wai ni?,ai da kinyi gaba da abinki don na jima banci abincinku ba,'yata na girkamin kullum" ta fada tana duban sumayya,take tsoro ya shigi karima,ashe tayi sake har haka?,ashe fa diyar malamai wannan karon lukman ya kwaso mata,lallai ba shakka shi yasa taga bata taba tambayar abincinta ba a gidan duk yadda ta sha alwashi akan yi mata kaca kaca duk sanda ta tambayi a bata abinci.
Hankalinta tashe ta fito daga bangaren ciken da tsoron lallai idan ta gama da hajiya babu shakka lukman zata dawowa,kacibus sukayi da nuwaira wadda ke dawowa daga gidan kitso da sumayya ta turata tayi saboda ba zata iya mata ba jiya ta yanke da wuqa a hannunta,baki ta saka tana duban nuwairan yadda ta canza cikin sati biyu kacal da kariman tayi bata nan,ta tilasta lukman ya biya musu umra ita da shi don har sai da yaci bashin wajen dubu dari biyar sannan ya cika musu,su kuma yaranta da zata tafi ta tattarasu ta maida su gidan iyayenta ta bar nuwaira ko oho,don dama ta saba yi mata irin hakan,tsoro ya kama nuwairan sai ta rabe gefe sannan ta tattakura ta sheqa da gudu sai bangaren hajiya,don kayan dake jikinta na waccar sallar ne shekara uku da dinka su,bata barinta ta sanya su sai wani abun ya tashi duk da cewa suna da lodin kaya harda wanda bata taba sawa ba ma sababbi,ta riga ta saba kayanta koda yaushe haka suke tamkar tsummokara,a haka ma sai an bata umarnin wadansa zata saka,bayan 'yan uwanta kullum cikin saka mai kyau suke.
Bata bi ta kan nuwaira ba don ba ita ce yanzu a gabanta,bangarenta ta wuce hankalinta a matuqar tashe,tabbas lallai babu shakka idan batayi wani abu ba ta lura duniyar rayuwarta gab take da girgiza koma rugujewa baki daya,dole ne gidan ya koma yadda yake,dole kowa ya koma yadda take so ciki kuwa harda sumayyan
****** ******* ******
Tunda ya karbeshi kusan shi ua zame masa uwa da uba baki daya,yana matuqar debe masa kewa,yana sanyashi nishadi,wata qauna ta yaron nasa yake ji cikin jikinsa da jininsa,sau tari ya kanyi mamakin kansa yadda yake zama yayita kallon abdallan kamar babu gobe,babu yadda yaya yahansu batayi ba akan ya bata shi amma ya qiya,ya bata haquri don bazai iya bata shi din ba.
Da safe tare suke shiryawa ya bashi abinci su fita kasuwa tare da shi,zuwa azahar zai bar kasuwa ya dan fita da shi su zaga gari su dawo da la'asar,qarfe shida subar kasuwa su dawo gida,har gado ya siya na yara ya sanya masa can cikin shagon,nan ma idan sun dawo sunyi wanka sannan suci takeaway din da ya tsaya hanya yayo musu,daga nan ya zube masa kayan wasansa yana tayashi yana kallon t.v har yaron yayi bacci,wani lokaci yakan bata lokaci saman abun sallah yana wa yaron nasa addu'a tare da yiwa kansa,wanda hakan ya sake samarwa da ruhinsa nutsuwa,shikewa Abdallahn komai,dai dai da rana guda mukhtar bai taba jin ya qosa koya gajiya ba,kai kanka idan ka kalli yaron ba zakayi zaton bai tare da mahaifiyarsa ba,kusan kullum sabon kayan mukhtar zai sanya masa,ado yake masa sosai,hakanan idan shadda zaya sanya ko yadi anko suke abinsu,duk wanda ya gansu a hanya zasu burgeshi,wata qauna ta musamman ce tsakanin d'a da ubansa,wani lokaci idan ya soma rigiman mamansa sai ya kaishi gunsu halima ya wuni don bai iya barinsa ya kwana,da dare yazo ya dauki abinsa su wuce.