Sashe 139
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yana gab da shiga elavator ya jiyi muryar hamza na qarasowa,hakan bai sanya shi ya tsaya ba ya shige ciki abinsa,da dan gudu hamzan ya qaraso ya shige ta rufe da su bayan ya amshi files dinsa dake hannun wannan mutumin,harara ya juya ya gallawa almustapha
"Maan,nifa banson wulaqanci da iskanci,nidin macace da zaka wani jaamin aji,idan ban narka maka dundu ba kace ba nine hamza ba" hararar shima ya watsa masa
"Haka kawai don ka zubda mana mutunci sai ka dinga ma mutane wannan kiran mafarautan kaman zan bar garin,sai kace bakasan inda office dina yake ba,baka ganin yadda ka taramin jama'a suna kallona wadancan yaran sun wami qwalolowa mutane idanu kamar zasu cinyeshi danye" dariya hamza ya bushe da ita ya dunqule hannu ya daki kafadarsa yana fadin
"Shege man,ashe kana kula,banda abinka kai da keson yaran wata qasar mai zai hana cikin indiyawan nan ka qara da daya" ya fada cikin salom tsokana sanda akwakun qarawa tafiya hanzari (elavator) ta iso da su block din da ofishinsa yake,bai kula shi ba shi kuwa hamza yabi bayanshi yana sheqa dariya abinsa,kusan duk duniya su kadai ke iya taba musty su dinma ba kowanne lokaci ba,bai tanka masa ba har ya sanya kati qofar lafiyayyen office dinshi ta bude wanda ya wadatu da tsafta qamshi da sanyi ya shige hamzan ya biyoshi,freezer ya bude ya fidda lemonsa da yake matuqar so ya daga ya soma sha yana takowa inda hamza ke zaune yana masa shaqiyanci,ya kammala sha ya jefa kwalin dustbin yayi kamar zai wuce sai ya shammaci hamzan ya damqo shi sosai ya riqe wuyan rigarsa yana dubanshi
"Ni kake ma shaqiyanci yau zaka gane kuranka" dariyarsa yaci gaba da yi don time to time sun saba haka da mustaphan wanda a wannan fage shi daga suke hakan koda su lamin bai sake musu haka,hannunshi hamza ya ware yana ci gaba da diyarsa yace
"Ah to,laifi nayi,wallahi aure ya kamaceka ka qara musty kowa yasan hakan" tsaki ya ja ya saki kwalarsa yana komawa da baya
"Allah ya sawwaqe,ni na gaya maka ina da buqatar aure don ubanka"cikin sin ya tunzurashi yace
"Basai ka gaya min ba,last night naje wajenka a hotel na taddaka kana mafarki,har wawurata kayi da qyar na sha" ya qarasa cikin matsananciyar dariya,naushi ya kawo masa ya kauce,sumarshi mustaphan ya shafa,ya fuskanci caakar da shi hamza ke son yi,qarancin suruti da yake da shine ya sanya bai iya maida raddi ko wasu amsoshi masu zafi ba matuqar ba cikin bacin rai yake ba,yanzun ma lalubar mai zai maida masa yake
"Kai zaka qara aure bani ba mayen mata"
"For what?,Nikam alhamdulillah,abida ta tsaren gaba ta tsaren baya,tun jiya wayarta ke damuna ma tayi missing dina tana buqatar na dawo gida,cikin satin nan kuwa zan gudu tunda mun gama daidaita komai samfuran kawai zamu fara saqawa,kai ke buqatar aure har yau aurenka babu riba,nan da few months za'a soma kirana da daddy" maganar ta daki mustapha,sai yayi shiru bai iya nada amsa ba,komawa yayi saman doguwar kujera ya kwanta gami da miqe qafafunshi bayan ya cire sau cikinshi da safar sa,duk da hamza baiyi da niyyar cin fuska ba tsokana ce kawai irin tasa sai ya dinga ji kamar bai kyauta ba,kamar ta bata ran abokin nashi,shima sai ya koma ya zauna yana fadin
"Am sorry musty,i dont mean to hurt you"
"Is ok" ya fada can qasa idanunshi a lumshe yana shafa fuskarshi da tafin hannunshi.
Tsawon minti talatin suja zaune a haka hamza na shan lemo bayan ya gama amsa wayar abida mustaphan na sauraran duk abinda suke cewa,duk da shi ba mutum bane mai sanya idanu kan lamuran wasu ba ba ruwanshi amma wannan karon kunnenshi sun kasa haqura,soyayyar ta burgeshi qwarai,shi mutum ne mai son yaga ana nuna damuwa da kulawa a kansa,zumbur ya miqe daga kwanciyar kamar wanda aka tsikara ya janyo wata sabuwar safar yana sanyawa cikin wani dan abu dake gefanshi don ya gama da waccar da ya cire yana fadin
"Muje ka saukeni airphort,sauran awa daya da rabi jirginmu ya tashi"
"Zuwa ina?" Hamza ya tambaya
"Nijeria" ya bashi amsa a taqaice kamar yadda ya saba,baki hamzan ya sake yana kallonshi,wani irin mutum ne mustaphan,yanzun suna tare zai tafi nijerian amma ya kasa bude baki ya gaya musu?,yasan halinshi sarai yafi gaban haka ma indai mustapha ne.
"Me zaka yo bayan ba time din zuwanka bane"
"Baabaa ke nema na" cikin son ya tsokaneshi yace
"Allah ya sanya wata 'yar naijan ya nema maka aure kai Allah yasa ma har an daura muga ya zakayi da 'yar africa tunda wadan da ba african ba ma kaqi" wata muguwaf harara ya watsa masa,haka kawai ya dinga ki kamar hamza ya masa baki ne
"Da kuwa sai na nada maka duka mummunan fatan da ka yimin,kafin na sanyata da qafafunta ta koma inda ta fito,na maka kama da wanda zai tara mata?,mace daya ta isheni rayuwa,dayan ma da ana bada rabi karba zanyi" sosai maganar mustaphan ta bashi dariya,yasan yaddq zai tsinkuleshi sosai.
miqewa yayi ya dire cup din yayin da mustapha ya gama gyara wuyan suit dinshi ya kwashi wayarsa da sauran abinda yake da buqata ya kashe duk wani electric dake office din suka fito,
"Kwana nawa zaka yi?"
"Ban sani ba nima" ya fada yana maida wayar aljihun suit dinshi
"Wacce iriyar masa ce haka kai har abada bayani wa mutane wuya yake maka?"
"Oh god,ka fiya tambaya,ka sanyani magana da yawa,bayan kana gani yanzu muka gama meeting nayi maganar da ba adadi,zaka sanya qirjina ciwo fa?"
"Bari na rufa maka asiri nayi shiru,don idan ya soma cuwon baka da mai jinyarka ko kwantar ma da hankali,amma ka sani this week nima zanyo gida"
"Sai ka iso" ya fada a taqaice,don yasan idan ba haka yayi masa ba bazai barshi ba,murmushi hamza yayi yana yiwa abokin nashi addu'ar Allah ya hadashi da mace ta gari wadda zatasan zafinsa da darajarsa,yasan dama bazai hana shi tafiya ba mutum ne mai kula da haqqin iyali ko na nashi ba.
******* ******** *******
Kano ta yiwa baabaa dadi,tunda ya baro abuja lokacin daurin aure bai koma ba,har yau rana irin ta yau da mustapha ke isowa nijeria wajenshi wanda a yau yammacin yau ne yake saka ran zai koma abuja shida matan nashi guda biyu,kullum yana kusa da abokinshi har yau labarin bayan saduwar bai qare ba.
Bayan gama shirin nashi cikin qaton dakin nashi falle daya dake dauke da faffadan gado da malalen carfet,wanda shine dakinshi na farko daya tabayi kuma shi dinma har yau ba rabu da shi ba,anty maamaa ta aiko mishi da abinci yaci sannan ya fito don ya gaisa da su.
Bangaren ummensa ya fara shiga,ya taddata zaune a falo tana gyaran farcenta,gefe da ita kadan ya samu ya zauna sosai ya tanqwashe qafafu,fuskarta fadade da fara'a take dubanshi,gashi mutum zam sak amma rashin iyalin qwarai na wasa da nutsuwarshi
"Barka da rana ummee,na sameku lafiya?"
"Lafiya qalau almustapha,ya hudimomi da sabgogi?"
"Alhamdulillahi ummee" ya fadi yana shafa suman kanshi
"Ya kowa da kowa?"
"Duk suna lafiya" ta bashi amsa,tasan da su amira huda da farida wanda ke dakin aure yake,yakan yawaita tambayarta yanayin zamansu,shiru ya dan ratsa tsakaninsj,shi bai da abin cewa kasancewarsa ba mai yawan magana ba,yayin da ummee ke kai kawon yadda almustaphan zai amshi maganar aurenshi,don ta tabbatar da cewa a yau baabaa zai gaya masa maganar
"Kunyi waya ne da yayanku?" Kai ya girgiza alamar a'ah idanunshi cikin na ummeen,ya gama karantar akwai wani lamari tattare da ita,bai wasa da dukkan lamuranta hakan ya sanya bashi wuya wajensa karantar yanayinta
"Okey,zaka wajen mahaifinka zakuyi magana da shi,abinda nake son gaya maka mahaifinka mahaifinka ne kafi kowa sani,bani da buqatar kayi jayayya ko mujadala da shi,tashi kaje nasan yana can yana jiranka" miqewa yayi yana amsa mata da to,yayin da zuciyarsa ke wassafa masa meye wannan wai da ya faru haka da shi wamda shi bai sani ba?,bai wuce ba sai da ya shiga ya gaida anty maamaan,cikin kulawa itama ta amsa masa,saidai ya lura itama tana masa irin kallon da yaga ummee na masa,yayim da tace masa sanda zai fita
"Almustapha,ka daure ka dore kan halinka na biyayya kaji?" Itama to dince amsar,sai ya samu kansa da hanzarin isa wajen baabaan don yaji koma mene,don shi mutum ne da baison boye boye,sak yake,fadin gaskiya komai dacinta.
"Maan,nifa banson wulaqanci da iskanci,nidin macace da zaka wani jaamin aji,idan ban narka maka dundu ba kace ba nine hamza ba" hararar shima ya watsa masa
"Haka kawai don ka zubda mana mutunci sai ka dinga ma mutane wannan kiran mafarautan kaman zan bar garin,sai kace bakasan inda office dina yake ba,baka ganin yadda ka taramin jama'a suna kallona wadancan yaran sun wami qwalolowa mutane idanu kamar zasu cinyeshi danye" dariya hamza ya bushe da ita ya dunqule hannu ya daki kafadarsa yana fadin
"Shege man,ashe kana kula,banda abinka kai da keson yaran wata qasar mai zai hana cikin indiyawan nan ka qara da daya" ya fada cikin salom tsokana sanda akwakun qarawa tafiya hanzari (elavator) ta iso da su block din da ofishinsa yake,bai kula shi ba shi kuwa hamza yabi bayanshi yana sheqa dariya abinsa,kusan duk duniya su kadai ke iya taba musty su dinma ba kowanne lokaci ba,bai tanka masa ba har ya sanya kati qofar lafiyayyen office dinshi ta bude wanda ya wadatu da tsafta qamshi da sanyi ya shige hamzan ya biyoshi,freezer ya bude ya fidda lemonsa da yake matuqar so ya daga ya soma sha yana takowa inda hamza ke zaune yana masa shaqiyanci,ya kammala sha ya jefa kwalin dustbin yayi kamar zai wuce sai ya shammaci hamzan ya damqo shi sosai ya riqe wuyan rigarsa yana dubanshi
"Ni kake ma shaqiyanci yau zaka gane kuranka" dariyarsa yaci gaba da yi don time to time sun saba haka da mustaphan wanda a wannan fage shi daga suke hakan koda su lamin bai sake musu haka,hannunshi hamza ya ware yana ci gaba da diyarsa yace
"Ah to,laifi nayi,wallahi aure ya kamaceka ka qara musty kowa yasan hakan" tsaki ya ja ya saki kwalarsa yana komawa da baya
"Allah ya sawwaqe,ni na gaya maka ina da buqatar aure don ubanka"cikin sin ya tunzurashi yace
"Basai ka gaya min ba,last night naje wajenka a hotel na taddaka kana mafarki,har wawurata kayi da qyar na sha" ya qarasa cikin matsananciyar dariya,naushi ya kawo masa ya kauce,sumarshi mustaphan ya shafa,ya fuskanci caakar da shi hamza ke son yi,qarancin suruti da yake da shine ya sanya bai iya maida raddi ko wasu amsoshi masu zafi ba matuqar ba cikin bacin rai yake ba,yanzun ma lalubar mai zai maida masa yake
"Kai zaka qara aure bani ba mayen mata"
"For what?,Nikam alhamdulillah,abida ta tsaren gaba ta tsaren baya,tun jiya wayarta ke damuna ma tayi missing dina tana buqatar na dawo gida,cikin satin nan kuwa zan gudu tunda mun gama daidaita komai samfuran kawai zamu fara saqawa,kai ke buqatar aure har yau aurenka babu riba,nan da few months za'a soma kirana da daddy" maganar ta daki mustapha,sai yayi shiru bai iya nada amsa ba,komawa yayi saman doguwar kujera ya kwanta gami da miqe qafafunshi bayan ya cire sau cikinshi da safar sa,duk da hamza baiyi da niyyar cin fuska ba tsokana ce kawai irin tasa sai ya dinga ji kamar bai kyauta ba,kamar ta bata ran abokin nashi,shima sai ya koma ya zauna yana fadin
"Am sorry musty,i dont mean to hurt you"
"Is ok" ya fada can qasa idanunshi a lumshe yana shafa fuskarshi da tafin hannunshi.
Tsawon minti talatin suja zaune a haka hamza na shan lemo bayan ya gama amsa wayar abida mustaphan na sauraran duk abinda suke cewa,duk da shi ba mutum bane mai sanya idanu kan lamuran wasu ba ba ruwanshi amma wannan karon kunnenshi sun kasa haqura,soyayyar ta burgeshi qwarai,shi mutum ne mai son yaga ana nuna damuwa da kulawa a kansa,zumbur ya miqe daga kwanciyar kamar wanda aka tsikara ya janyo wata sabuwar safar yana sanyawa cikin wani dan abu dake gefanshi don ya gama da waccar da ya cire yana fadin
"Muje ka saukeni airphort,sauran awa daya da rabi jirginmu ya tashi"
"Zuwa ina?" Hamza ya tambaya
"Nijeria" ya bashi amsa a taqaice kamar yadda ya saba,baki hamzan ya sake yana kallonshi,wani irin mutum ne mustaphan,yanzun suna tare zai tafi nijerian amma ya kasa bude baki ya gaya musu?,yasan halinshi sarai yafi gaban haka ma indai mustapha ne.
"Me zaka yo bayan ba time din zuwanka bane"
"Baabaa ke nema na" cikin son ya tsokaneshi yace
"Allah ya sanya wata 'yar naijan ya nema maka aure kai Allah yasa ma har an daura muga ya zakayi da 'yar africa tunda wadan da ba african ba ma kaqi" wata muguwaf harara ya watsa masa,haka kawai ya dinga ki kamar hamza ya masa baki ne
"Da kuwa sai na nada maka duka mummunan fatan da ka yimin,kafin na sanyata da qafafunta ta koma inda ta fito,na maka kama da wanda zai tara mata?,mace daya ta isheni rayuwa,dayan ma da ana bada rabi karba zanyi" sosai maganar mustaphan ta bashi dariya,yasan yaddq zai tsinkuleshi sosai.
miqewa yayi ya dire cup din yayin da mustapha ya gama gyara wuyan suit dinshi ya kwashi wayarsa da sauran abinda yake da buqata ya kashe duk wani electric dake office din suka fito,
"Kwana nawa zaka yi?"
"Ban sani ba nima" ya fada yana maida wayar aljihun suit dinshi
"Wacce iriyar masa ce haka kai har abada bayani wa mutane wuya yake maka?"
"Oh god,ka fiya tambaya,ka sanyani magana da yawa,bayan kana gani yanzu muka gama meeting nayi maganar da ba adadi,zaka sanya qirjina ciwo fa?"
"Bari na rufa maka asiri nayi shiru,don idan ya soma cuwon baka da mai jinyarka ko kwantar ma da hankali,amma ka sani this week nima zanyo gida"
"Sai ka iso" ya fada a taqaice,don yasan idan ba haka yayi masa ba bazai barshi ba,murmushi hamza yayi yana yiwa abokin nashi addu'ar Allah ya hadashi da mace ta gari wadda zatasan zafinsa da darajarsa,yasan dama bazai hana shi tafiya ba mutum ne mai kula da haqqin iyali ko na nashi ba.
******* ******** *******
Kano ta yiwa baabaa dadi,tunda ya baro abuja lokacin daurin aure bai koma ba,har yau rana irin ta yau da mustapha ke isowa nijeria wajenshi wanda a yau yammacin yau ne yake saka ran zai koma abuja shida matan nashi guda biyu,kullum yana kusa da abokinshi har yau labarin bayan saduwar bai qare ba.
Bayan gama shirin nashi cikin qaton dakin nashi falle daya dake dauke da faffadan gado da malalen carfet,wanda shine dakinshi na farko daya tabayi kuma shi dinma har yau ba rabu da shi ba,anty maamaa ta aiko mishi da abinci yaci sannan ya fito don ya gaisa da su.
Bangaren ummensa ya fara shiga,ya taddata zaune a falo tana gyaran farcenta,gefe da ita kadan ya samu ya zauna sosai ya tanqwashe qafafu,fuskarta fadade da fara'a take dubanshi,gashi mutum zam sak amma rashin iyalin qwarai na wasa da nutsuwarshi
"Barka da rana ummee,na sameku lafiya?"
"Lafiya qalau almustapha,ya hudimomi da sabgogi?"
"Alhamdulillahi ummee" ya fadi yana shafa suman kanshi
"Ya kowa da kowa?"
"Duk suna lafiya" ta bashi amsa,tasan da su amira huda da farida wanda ke dakin aure yake,yakan yawaita tambayarta yanayin zamansu,shiru ya dan ratsa tsakaninsj,shi bai da abin cewa kasancewarsa ba mai yawan magana ba,yayin da ummee ke kai kawon yadda almustaphan zai amshi maganar aurenshi,don ta tabbatar da cewa a yau baabaa zai gaya masa maganar
"Kunyi waya ne da yayanku?" Kai ya girgiza alamar a'ah idanunshi cikin na ummeen,ya gama karantar akwai wani lamari tattare da ita,bai wasa da dukkan lamuranta hakan ya sanya bashi wuya wajensa karantar yanayinta
"Okey,zaka wajen mahaifinka zakuyi magana da shi,abinda nake son gaya maka mahaifinka mahaifinka ne kafi kowa sani,bani da buqatar kayi jayayya ko mujadala da shi,tashi kaje nasan yana can yana jiranka" miqewa yayi yana amsa mata da to,yayin da zuciyarsa ke wassafa masa meye wannan wai da ya faru haka da shi wamda shi bai sani ba?,bai wuce ba sai da ya shiga ya gaida anty maamaan,cikin kulawa itama ta amsa masa,saidai ya lura itama tana masa irin kallon da yaga ummee na masa,yayim da tace masa sanda zai fita
"Almustapha,ka daure ka dore kan halinka na biyayya kaji?" Itama to dince amsar,sai ya samu kansa da hanzarin isa wajen baabaan don yaji koma mene,don shi mutum ne da baison boye boye,sak yake,fadin gaskiya komai dacinta.