← Book details Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 226

Sashe 77

Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

        Sallar da bata iya yiba kenan har aka kammala sallar laila ta shigo kiranta tazo suci abinci,can qasa ta amsa mata data qoshi sai anjima zata ci,haka taci gaba da kwanciya,tana ganin tarin misscalled din abdur rahman amma ta kasa dagawa har ya gaji ya bar kiran ya turo mata texs,baccin dole ne ya dauketa,bata wani jima ba ta farka,har a lokacin tana jin wata iriyar damuwa na ratsata,sallar isha'in da bata yiba tayi,sannan tayi tarawih din raka'a bakwai har da wutiri.

  *******   ******   *******

       Daga ranar karatun shi ya zame mata abun sauraronta daga sallar isha'i har a kammala,sosai karatun da muryar ke debe mata kewa ya sanyata nutsuwa,wani lokaci tana ji tana hawaye don ba qaramin tuna mata mukhtar yake yi ba,babu wanda yasan halin da take ciki sai ita kadaj,kawai dai anty dije taga ta rage walwala,bata kawo komai ba ta dauka ibadar da ake ciki ne.

       A haka aka kammala azumi ashirin cif,ranar ashirin da daya sai taji ba waccan muryar bace,duk sai taji ta damu,ji take kamar ta fita ta gano me ya kawo wannan sauyin,daga bisani ta tuna anty dije ta gaya mata goman farko da na tsakiya kawai yake jan sallah,to wannan wane ne?,babu shakka ba don anty dije ta sanshi ba babu abinda zai hana tace mukhtar dinta ne,baki daya sai ta jita sukuku,ba qaramin dadin jin muryar take ba,a ranar uncle farouq ya shigo musu da kayan sallarsu,kowannensu kala shuda shida a dinke,sumayya laila da anty dije kam harda mayafai takalma da jakankuna,daga mayafin kawai sumayyan tayi ta ajjiye gefe,tun mutuwar mukhtar ta sake qanqame hijabi duk da cewa dama al'adarta ne sanyashi,sai dai a baya tana sanya mayafan lokaci lokaci,anty dije ta lura sai ta bada sautun yadin hijabai masu kyau aka yi mata irin wadanda take so,anty dijen ita ta sanya kudinsu ta saya musu dan kunnaye da awarwaro da sarqa fashion designers masu kyau kala uku uku.

         Washe gari akayo aike daga gidan baabaa prof,duk da cewa a jiya ya daga saudiyya shima zasu dawo tare da iyalansa a ranar sallah,a qasarsa yake nashi bikin sallah saboda ziyara da ake kawo masa tako ina,abokai 'ya'ya jikoki 'yan uwa da abokan arziqi,daya daga cikin ma'aikatan gidan ne,sanye da unifoarm dinsu,a mutunce ta gaida anty dijen sannan ta miqa mata wata qatuwar baqar leda dake dauke da tambarin wani company dake dubai,company ne da yaje mallakin daya daga cikin iyalin baabaa prof din,shahara da daukakar company din ya sanya wasu suma saka jarinsu a ciki
"Kiyi haquri umman khalipha,tun jiya baabaa ya bada saqon,sai yau na samu sauqin aiki,munata ayyuka ne"
"Babu komai shema'u,baabaa dai kam bai gajiya,Allah yasa a gama lafiya" murmushi tayi
"Baabaa badai alkhairi ba,ko mu bai mana mu kadai har 'yan uwa na kusa alherinsa bai barsu ba,ina zaton wannan karon har baquwarki da nata kayan,naji kamar ita taiwa baabaan abincin kwana ashirin ko?" Dariya anty dije tayi
"Sumayya,eh itace"
"Ai baabaa na jin dadin abincin nan kam qwarai,rannan har yasa a kira ta su gaisa sai yayi baqi kuma ya sha'afa"
"Allah sarki,ai idan suka dawo da kaina zan tura ta ta gaidashi,Allah ya saka masa da alheri,yaci gaba da shirya masa zuria"
"Amin ya Allah"
Shema'u ta fada tana ficewa.

       Juya ledar anty dije tayi tana murushi,tambarin kamfanin kadai data gani tasan ba kaya bane masu qananun kudi,bude ledar tayi ta fara zarosu,diguwar riga ce irinta mata mai bala'in kyau da tsari wadda aka zauna aka yiwa aikin duwatsu daga sama har qasa,iya dutsen kadai idan ka kalla kasan ba qaramin kudi zaka sanya ba kafin ka mallakesu,yadin kansa abin kallo ne bare dutsen,guda daya baqa ce,sai dayar fara ce qal da aka yiwa aikin baqaqen duwatsu,dayar kuma ruwan jinin kare ja ba dau ba ya dan rusuna amma baikai duhun maroon ba,tana duba size din rigar ta gane sune na sumayya,kowacce akwai vail da ya dace da ita,murmushi tayi don tasan aikin amira ne wannan,wani shegen fashion mai zubin gwal guda daya da banguls dinsa,haka na lailaa suke saidai banbancin tsaho da kala,tasan laila kam za'a sha murna,duk shekara ya saba haka yake musu,duk cikin kayan sallarta tafi ji da kayan gidan baabaa prof,mazan ma baki dayansu jallabiua ce irinta maza mai tsada,sai gezna wadda kana mata kallon farko itama kasan ansha kudi kala bibbiyu duka kalolin iri daya,sanda aka kawo su sumayya basanan sun tafi wankin kai,da suka dawo baki sumayya ta saki,zata iya cewa banda lace din da aka bata taba kaya masu tsada haka ba,ko lace din ta tabbata baikai kudin wadan nan ba,yana ajjiye ma bata dinkashi ba,godiya tayi sosai kamar suna wajen tare da yaba dimbin karamcin ahalin gidan.

      Cikin ranakun goman qarashen so kadan bata yi sanya wajen zabga addu'a gareta da d'anta da sauran yaran musulmi ba da al'umma ba,musamman ranakun da suke mara,wato ranakun da ake tsammacin dare lailatul qadr,tayi addu'ar samun kyakkyawar rayuwa da kuma kyakkyawar QADDARA,sai ta dinga jin nutsuwa da kwanciyar hankali,tsoro da damuwarta suka dinga raguwa a hankali.

        Ran ashirin da tara ga wata aka tabbatar da ganin watan sallah waahegari idin qaramar sallah kenan,a gajiye ranar suke don wuni sukayi gidan qunshi,da cewa sumayyan tayi ma bata yi,anty dije ce ta matsanta mata tilas ta bisu,ga wainar shinkafa da ta tsara zata yi musu a ranar sallah,Allah ya taimaka kafin ta kwanta tayi miyarta,zumudin zuwan sallar take sosai wannan karon,saboda uncle farouq yace sallah da kwana biyar zasu tafi kano,a qalla zasuyi sati guda sannan su dawo su fara shirin tafiya london.

*******   ******    *********

        Qarfe goma na safe tuni an sakko daga sallah,zuwa lokacim sumayya ta kammala aikinta,wankanta tayi ta shirya cikin daya daga cikin dinkin da abban laila ya musu,ba wani makeup tayi ba amma kayan sun mata kyau,rabon abincin sallah anty dijen tayi kamar yadda ta saba.

       Da yammaci su laila da khalipha nata hada barka da sallah sabbin kudi baki yaqi rufuwa,sai shigowa suke suna bawa sumayya labari su wance sunzo gidan baabaa su wane sunzo,itakam kusan bata sansu ba saidai tace musu to,dariya anty dije tayi
"Abokansu ne jikokin baabaa prof, 'ya'yan babban dansa da me bi masa,kinsan duk wani da nashi da jika dake nesa a gida yake sallah". Abban lailan nata baqi,wasu na zuwa wasu na tafiya kusan haka suka wuni.

        Wajen biyar tana sama dakin anty dije tana gyara mata,saboda yau baki daya ta kasa zama saboda baqi,hayaniya ta dinga jiyowa da qarar motoci,sau ta miqe a hankali,ta yaye labule tare da bude qofar da zata sadaka da balcony din anty dije dake saman,bata fiya budeshi ba sai lokacin zafi ko kuma idan ta kama saboda idan ka fita kana iya hango jama'an waje suma suna iya ganinka musamman da yake yana center din tafkeken get din shiga gidan su amira,duk da cewa waccar babbar qofar da akafi shiga  wadda jami'an tsaro ke gadinta tana daya daya layin nasu,wannan a nan suka fi harkokinsu.

      Motocine na alfarma qirar zamani,wanda ke dauke da lamba mai tambarin sunan baabaa prof,wanda hakan ke alamta mallaki ne na ahalinsa,kimanin mota shida kowacce na qoqarin shiga gidan ba tare da wata ta gogi wata ba,sai da suka kammala shiga baki daya sannan wadanda suka wangame get din suka rufe shi,ajiyar zuciya ta saki sannan ta juya ta koma cikin dakin wanda hakan yayi dai dai da shigowar anty dije
"Kai,har kin gama?" Tana duba yadda ta gyara kayan
"Na gama anty" inji sumayya tana dan kashingidewa
"Kinga yanzun abban laila ke gayan su baabaa sun dawo,amma dai wannan karon zaki ki masa sannu da zuwa ko ku gaisa"dan murmushi ta saki yana yamutsa fuska
"Eh anty,amma dai ba yanzu ba ko?"
"Nima ai bance yanzu ba,kinji an ambaci maqiyinki shiga gidan baabaa ko?" Dariya ta tuntsire da ita har tana kwanciya ganin irin yadda antyn tayi maganar.

  *****  ********    ******

    Washe gari da yammaci hudu da ashirin bayan ta gama yima anty dijen komai,sai ta shirya cikin wasu kayan nata,swiss ne mai asalin tsadar wanda aka tsara mata dinki na riga da skert,babu kwalliya a fuskarta kamar ko yaushe tun bayan rashin mukhtar cikin rayuwarta illa hoda jagira da liptsic,sabon hijabinta mai hannu wannan karon iya gwiwarta ta zura wanda yayi marching da lace din jikinta,tayi kyau sosai kayan sun haska ta,tun dazun take laqai laqai na zuwa gaida baaban,hakan ne yasa ma ta tsiri yi masa dambun zallar tsokar kaza.

       Anty dijen ita ta sake turo qofar dakin karo na biyu tun bayan shigarta wanka
"Baki gama bane har yanzu?"
"Na gama anty" ta fada tana fesa turare
"To,saidai fa ki shiga ke daya kya tadda lailan acan,don duka suna can gidan,ta kasa jiranki,don naji tana kamar zasu park ne"
"To" ta fada badon ranta ya so ba,takalmi ta zura mara tsahon dunduniya sannan ta fito.

        Daga qofar gidan baka gane gidan na qunshe da baqi ba sai ka kai ga shiga harabar gidan,yara ne da 'yammata kala kala,wadanda kana duban yanayin shigarsu zaka tabbatar da cewa lallai boko ya ratsasu,wayewa da kuma sanin kam duniya,kamar yadda group group ya rabu haka kowacce da irin tata shigar,ta wannan tana wace wance,nan da can zaka ga mutum biyu uku har hudu ma a tsaitsaye,kowa na sabgar gabansa saboda wadatar guri da kujerun zama a ko ina,wanda suke nuna lokaci irin wannan ake fiddo su ayi amfani da su.
Chapter 77 · 0% Book details